< Isaiah 50 >

1 Thus hath said the Lord, Where is your mother's bill of divorcement, wherewith I have sent her away? or who of my creditors is it to whom I have sold you? behold, for your iniquities were ye sold, and for your transgressions was your mother sent away.
Ga abin da Ubangiji yana cewa, “Ina takardar shaida na saki mahaifiyarka daga aure wadda na kora? Ko kuwa ga wanda mutumin da nake bin bashi ne na sayar da kai? Saboda zunubanka aka sayar da kai; saboda laifofinka ne ya sa aka kori mahaifiyarka.
2 Why did I come and no man was there, did I call, with none to answer? hath my hand become too short for redeeming? or is there no power in me to deliver? behold, through my threatening I can dry up the sea, I can change the rivers into a wilderness: their fish stink for want of water, and die for thirst.
Sa’ad da na zo, me ya sa babu kowa? Sa’ad da na yi kira, me ya sa babu wani da ya amsa? Hannuna ya kāsa ne sosai don fansarka? Na rasa ƙarfin kuɓutar da kai ne? Ta wurin tsawatawa kawai na busar da teku, na mai da koguna hamada; kifayensu duk sun ruɓe saboda rashin ruwa suka kuma mutu saboda ƙishi.
3 I can clothe the heavens with blackness, and I can make sackcloth their garment.
Na suturar da sararin sama da duhu na kuma mai da tsummoki abin rufuwarsa.”
4 The Lord Eternal hath given me a tongue for teaching, that I should know how to strengthen the weary with the word: he wakeneth morning by morning, he wakeneth my ear to listen like those who are well taught.
Ubangiji Mai Iko Duka ya ba ni harshen umarni, don in san maganar da za tă ƙarfafa gajiyayye. Ya farkar da ni da safe, ya farkar da kunnena don in saurara kamar wanda ake koya masa.
5 The Lord Eternal hath opened me my ear, and I resisted not: I turned not backward.
Ubangiji Mai Iko Duka ya buɗe kunnuwana, kuma ban yi tayarwa ba; ban ja da baya ba.
6 My back I gave up to the smiters, and my cheeks to those that plucked off the hair: my face I hid not from abuse and spitting.
Na ba da bayana ga masu dūkana, kumatuna ga masu jan gemuna; ban ɓoye fuskata daga masu ba’a da masu tofa mini miyau ba.
7 But the Lord Eternal ever helpeth me; therefore was I not confounded; therefore have I rendered my face like a flint, and I knew that I should not be made ashamed.
Gama Ubangiji Mai Iko Duka zai taimake ni, ba zan sha kunya ba. Saboda haka na kafa fuskata kamar dutsen ƙanƙara, na kuma sani ba zan sha kunya ba.
8 He that justifieth me is near; who will contend with me? let us stand forward together: who hath a dispute with me? let him come near to me.
Gama shi da zai tabbatar da ni, marar laifi ne yana kusa. Wane ne zai kawo ƙararraki game da ni? Bari mu je ɗakin shari’a tare! Wane ne mai zargina? Bari yă kalubalance ni!
9 Behold, the Lord Eternal will help me; who is the man that will condemn me? lo, they all shall wear out as a garment: the moth shall eat them up.
Ubangiji Mai Iko Duka ne zai taimake ni. Wane ne zai iya tabbatar da ni mai laifi? Duk za su koɗe kamar riga; asu za su cinye su.
10 Who is among you that feareth the Lord, that hearkeneth to the voice of his servant? though he have walked in darkness, and had no light: let him trust in the name of the Lord, and lean for support upon his God.
Wane ne a cikinku yake tsoron Ubangiji yana kuma yin biyayya ga maganar bawansa? Bari wanda yake tafiya cikin duhu, wanda ba shi da haske, ya dogara a sunan Ubangiji ya kuma dogara ga Allahnsa.
11 Behold, all ye that kindle fire, that urge on the brands: walk by the blaze of your fire, and by the brands ye have kindled; from my hand hath this been bestowed on you; in pain shall ye lie down.
Amma yanzu fa, dukanku waɗanda kuke ƙuna wuta kuna kuma tanada wa kanku fitilu masu ci, ku je ku yi tafiya a cikin hasken wutarku da na fitilun da kuka ƙuna. Abin da za ku karɓa ke nan daga hannuna. Za ku kwanta a cikin azaba.

< Isaiah 50 >