< Isaiah 48 >

1 Hear ye this, O house of Jacob, who are called by the name of Israel, and are come forth out of the spring of Judah, who swear by the name of the Lord, and make mention of the God of Israel, —not in truth, nor in righteousness.
“Ku kasa kunne ga wannan, ya gidan Yaƙub, waɗanda ake kira da sunan Isra’ila suka kuma fito daga zuriyar Yahuda, ku da kuke yin rantsuwa da sunan Ubangiji kuna kuma kira sunan Allah na Isra’ila, amma ba da gaskiya ko adalci ba,
2 For of the holy city they call themselves, and upon the God of Israel they stay themselves, —The Lord of hosts is his name.
ku da kuke kiran kanku’yan ƙasar birni mai tsarki kuna kuma dogara ga Allah na Isra’ila, Ubangiji Maɗaukaki ne sunansa,
3 The former things have I declared from the beginning; and out of my mouth went they forth, and I announced them: suddenly did I accomplish them, and they came to pass;
na nanata abubuwan da suka riga suka faru tuntuni, bakina ya yi shelar su na kuma sanar da su; sai nan da nan na aikata, suka kuma faru.
4 Because I knew that thou art obstinate, that like an iron sinew is thy neck, and thy brow of copper;
Gama na san yadda kuke da taurinkai; jijiyoyin wuyanku ƙarafa ne, goshinku tagulla ne.
5 And I declared it to thee from the beginning; before yet it came to pass did I let thee hear it: lest thou should say, My idol hath done these things, and my graven image, and my molten image, have ordained them.
Saboda haka na faɗa waɗannan abubuwa tuntuni; kafin su faru na yi shelarsu gare ku saboda kada ku ce, ‘Gumakana ne suka yi su; siffar itacena da allahn zinariyana ne ya ƙaddara su.’
6 Thou hast heard it; see it all now; and you—will you not declare it? I caused thee to hear new things, from this time, even hidden things which thou hadst not known.
Kun riga kun ji waɗannan abubuwa; kuka gan su duka. Ba za ku yarda da su ba? “Daga yanzu zuwa gaba zan faɗa muku sababbin abubuwa, na ɓoyayyun abubuwan da ba ku sani ba.
7 Now are they created, and not from the beginning; and before the day [that I announced them] thou heardest them not; lest thou shouldest say, Behold, I knew them.
Yanzu an halicce su, ba da daɗewa ba; ba ku riga kun ji game da su kafin yau ba. Saboda haka ba za ku ce, ‘I, na san da su ba.’
8 But neither hadst thou heard it; nor didst thou know; nor had in ancient times thy ear been opened; for I knew that thou wouldst deal very treacherously, and a transgressor wast thou called from thy birth.
Ba ku ji ko balle ku gane ba; tun da kunnenku bai buɗu ba. Tabbatacce na san yadda kun zama masu tayarwa; an kira ku’yan tawaye daga haihuwa.
9 For the sake of my name will I defer my anger, and because of my praise will I restrain it toward thee, so that I may not cut thee off.
Saboda girman sunana na jinkirta fushina; saboda girman yabona na janye shi daga gare ku, don dai kada a yanke ku.
10 Behold, I have refined thee, though not into silver: I have approved thee in the crucible of affliction.
Duba, na tace ku, ko da yake ba kamar azurfa ba; na gwada ku cikin wutar wahala.
11 For my own sake will I do it: for how would [my name] be dishonored? and my glory will I not give unto another.
Saboda girmana, saboda girmana, na yi haka. Yaya zan ƙyale a ƙazantar da kaina? Ba zan raba ɗaukakata da wani ba.
12 Hearken unto me, O Jacob, and Israel, my called one; I am he; I am the first, I also am the last.
“Ka kasa kunne gare ni, ya Yaƙub, Isra’ila, wanda na kira cewa, Ni ne shi; ni ne na farko ni ne kuma na ƙarshe.
13 My hand also hath laid the foundation of the earth, and my right hand hath spanned out the heavens: I call unto them, they stand forward together.
Hannuna ne ya kafa harsashen duniya, hannuna na dama kuma ya shimfiɗa sammai; sa’ad da na kira su, duka suka miƙe tsaye gaba ɗaya.
14 Assemble yourselves, all of you, and hear: Who among them hath told these things? He whom the Lord loveth, will do his pleasure on Babylon, and [display] his arm [on] the Chaldeans.
“Ku tattaru, dukanku ku kuma saurara, Wanne a cikin gumakan ya iya faɗa waɗannan abubuwa? Zaɓaɓɓen da Ubangiji yake ƙauna zai aikata nufinsa a kan Babilon; hannunsa zai yi gāba da Babiloniyawa.
15 I, even I, have spoken it, I have also called him: I have brought him, and he shall be prosperous on his way.
Ni kaina, na faɗa; I, na kira shi. Zan kawo shi, zai kuma yi nasara a cikin aikinsa.
16 Come ye near unto me, hear ye this; never from the beginning have I spoken in secret; from the time that it occurred, was I there. And now the Lord Eternal hath sent me, and his Spirit.
“Ku zo kusa da ni ku kuma saurari wannan. “Daga farkon shela ban yi magana a ɓoye ba; a lokacin da ya faru, ina nan a wurin.” Yanzu kuwa Ubangiji Mai Iko Duka ya aiko ni, da Ruhunsa.
17 Thus hath said the Lord, thy Redeemer, the Holy One of Israel, I am the Lord thy God who teach thee for thy profit, who lead thee by the way thou shouldst go.
Ga abin da Ubangiji yana cewa, Mai Fansarku, Mai Tsarkin nan na Isra’ila ya ce, “Ni ne Ubangiji Allahnku, wanda ya koya muku abin da ya fi muku kyau, wanda ya muku hanyar da za ku bi.
18 Oh that thou hadst but listened to my commandments! then would have been as a river thy peace, and thy prosperity as the waves of the sea:
Da a ce kawai za ku mai da hankali ga umarnaina, da salamarku ta zama kamar kogi, adalcinku kamar raƙuman teku.
19 And then would have been as the sand thy seed, and the offspring of thy body like the pebbles of the sea-shore; yet shall his name not be cut off nor destroyed from before me.
Da zuriyarku ta zama kamar yashi,’ya’yanku kamar tsabar hatsin da ba a iya ƙidayawa; da ba za a taɓa yanke sunansu balle a hallaka su daga gabana ba.”
20 Go forth out of Babylon, flee away from the Chaldeans, with the voice of singing declare, announce this, carry it forth as far as the end of the earth; say, The Lord hath redeemed his servant Jacob.
Ku bar Babilon, ku gudu daga Babiloniyawa! Ku yi shelar wannan da sowa ta farin ciki ku kuma furta shi. Ku aika shi zuwa iyakokin duniya; ku ce, “Ubangiji ya fanshi bawansa Yaƙub.”
21 And they thirsted not when he led them through the deserts; waters out of the rock he let drop down for them: and he cleaved the rock, and the waters gushed out.
Ba su ji ƙishi ba sa’ad da ya bishe su a cikin hamada; ya sa ruwa ya malalo dominsu daga dutse; ya tsage dutse ruwa kuwa ya kwararo.
22 There is no peace, saith the Lord, unto the wicked.
“Babu salama ga mugaye” in ji Ubangiji.

< Isaiah 48 >