< Isaiah 47 >

1 Come down, and sit in the dust, O virgin daughter of Babylon; sit on the ground, there is no throne, O daughter of the Chaldeans; for men shall nevermore call thee, Tender and delicate.
“Ki gangara, ki zauna a ƙura, Budurwa Diyar Babilon; ki zauna a ƙasa ba tare da rawani ba, Diyar Babiloniyawa. Ba za a ƙara kira ke marar ƙarfi’yar gata ba.
2 Take the mill, and grind meal: uncover thy locks, lift up the train, uncover the thigh, pass over the rivers.
Ɗauki dutsen niƙa ki niƙa gari; ki kware lulluɓinki. Ki ɗaga fatarinki ki bar ƙafafunki tsirara, ki kuma yi ta ratsa cikin rafuffuka.
3 Thy nakedness shall be uncovered, yea, thy shame shall be seen: I will take vengeance, and I will not regard any man.
Tsirararki zai bayyana za a kuma buɗe kunyarki. Zan ɗauki fansa; ba zan bar wani ba.”
4 Our redeemer—the Lord of hosts is his name, the Holy One of Israel.
Mai Fansarmu, Ubangiji Maɗaukaki shi ne sunansa, shi ne Mai Tsarkin nan na Isra’ila.
5 Sit thou silent, and enter into darkness, O daughter of the Chaldeans; for men shall never more call thee, The mistress of kingdoms.
“Zauna shiru, tafi cikin duhu, Diyar Babiloniya; ba za a ƙara kira ke sarauniyar masarautai.
6 I was wroth over my people, I defiled my inheritance, and gave them into thy hand: [yet] thou didst grant them no mercy; upon the aged hast thou laid very heavily thy yoke.
Na yi fushi da mutanena na ƙazantar da gādona; na ba su ga hannunki, ba ki kuwa nuna musu jinƙai ba. Har ma da tsofaffi kin jibga musu kaya masu nauyi sosai.
7 And thou saidst, For ever shall I be mistress; until that thou didst not lay these things to thy heart, thou didst not call to mind the result thereof.
Kika ce, ‘Zan ci gaba har abada, madawwamiyar sarauniya!’ Amma ba ki lura da waɗannan abubuwa ko ki yi la’akari a kan abin da zai faru ba.
8 And now hear this, luxurious one, that dwellest in security, that sayest in thy heart, I am, and there is nothing else beside me; I shall not sit as a widow, neither shall I know the loss of children:
“To, yanzu fa, ki kasa kunne, ke mai ƙaunar nishaɗi, mai zama da rai kwance kina kuma ce wa kanki, ‘Ni ce, kuma babu wani in ban da ni. Ba zan taɓa zama gwauruwa ko in sha wahalar rashin’ya’ya ba.’
9 Yet both these things shall come to thee in a moment in one day, the loss of children, and widowhood; in their full measure shall they come upon thee, despite of the multitude of thy sorceries, despite of the very great abundance of thy enchantments.
Duk waɗannan za su sha kanki cikin farat ɗaya, a rana guda, rashin’ya’ya da gwauranci. Za su zo a kanki da cikakken minzani, duk da yawan masu dubanki da kuma dukan sihirinki.
10 And thou didst trust in thy wickedness: thou saidst, No one seeth me. Thy wisdom and thy knowledge, —these were they that seduced thee; and thou saidst in thy heart, I am, and there is nothing else beside me.
Kin dogara a muguntarki kika kuma ce, ‘Babu wanda ya gan ni.’ Hikimarki da saninki sun ɓad da ke sa’ad da kika ce wa kanki, ‘Ni ce, kuma babu wani in ban da ni.’
11 And there shall come upon thee an evil, which thou shalt not know how to remove it by prayer; and there shall fall upon thee mischief, which thou shalt not be able to atone for; and there shall come upon thee suddenly desolation, which thou shalt not know.
Bala’i zai fāɗo a kanki, kuma ba za ki san yadda za ki rinjaye shi yă janye ba. Masifa za tă fāɗo a kanki da ba za ki iya tsai da ita da kuɗin fansa ba; lalacewar da ba ki taɓa mafarkinta ba za tă auko miki nan da nan.
12 Stand now with thy enchantments, and with the multitude of thy sorceries, wherein thou hast labored from thy youth; peradventure thou mayest be able to profit, peradventure thou mayest withstand.
“Ki dai ci gaba, da sihirinki da kuma makarunki masu yawa, waɗanda kika yi ta wahala tun kina jaririya. Mai yiwuwa ki yi nasara, mai yiwuwa ki jawo fargaba.
13 Thou art wearied with the multitude of thy counsels. Do let now those that divide off the heavens, that look at the stars, that announce [coming] events at new moons, stand up, and save thee from the things that are to come over thee.
Dukan shawarwarin da kika samu sun dai gajiyar da ke ne kawai! Bari masananki na taurari su zo gaba, waɗannan masu zāna taswirar sammai suna kuma faɗa miki dukan abin da zai faru da ke wata-wata, bari su cece ki daga abin da zai faru da ke.
14 Behold, they are become as stubble; the fire burneth them; they shall not deliver themselves from the power of the flame: not a coal shall be left to warm at, no blaze to sit before it.
Tabbas suna kama da bunnu; wuta za tă cinye su ƙaf. Ba za su ma iya ceton kansu daga ikon wutar ba. Ba wutar da wani zai ji ɗumi; ba wutar da za a zauna kusa da ita.
15 Thus are they become unto thee with whom thou hast labored; those that had commerce with thee from thy youth, wander away every one on his road: there is no one to save thee.
Abin da za su iya yi miki ke nan kawai, waɗannan da kika yi ta fama da su kika kuma yi ciniki da su tun kina jaririya. Kowannensu zai tafi cikin kuskurensa; babu ko ɗayan da zai cece ki.

< Isaiah 47 >