< Isaiah 37 >
1 And it came to pass, when king Hezekiah heard it, that he rent his clothes, and covered himself with sackcloth, and went into the house of the Lord.
Sa’ad da Sarki Hezekiya ya ji haka, sai ya kyakkece rigunansa ya kuma sanya tsummoki ya tafi ya shiga haikalin Ubangiji.
2 And he sent Elyakim, who was superintendent over the house, and Shebna the scribe, and the elders of the priests, covered with sackcloth, to Isaiah the son of Amoz, the prophet.
Ya aiki Eliyakim sarkin fada, Shebna magatakarda da kuma manyan firistoci, duka sanye da tsummoki, wurin Ishaya ɗan Amoz.
3 And they said unto him, Thus hath said Hezekiah, A day of trouble, and of rebuke, and of derision is this day; for the children are come to the birth, and there is not strength to bring forth.
Suka faɗa masa cewa, “Ga abin da Hezekiya ya ce wannan rana ce ta baƙin ciki da tsawatawa da shan kunya, sai ka ce sa’ad da’ya’ya kan zo matakin haihuwa sa’an nan a rasa ƙarfin haihuwarsu.
4 Perhaps the Lord thy God will hear the words of Rabshakeh, whom the king of Assyria his master hath sent to blaspheme the living God, and who hath reproached with the words which the Lord thy God hath heard: wherefore lift up a prayer for the remnant that is still found here.
Mai yiwuwa Ubangiji Allahnka zai ji maganganun sarkin yaƙin da maigidansa, sarkin Assuriya, ya aika don yă zagi Allah mai rai, ya kuma tsawata masa saboda maganganun da Ubangiji Allahnka ya ji. Saboda haka ka yi addu’a saboda raguwar da suke da rai.”
5 And the servants of king Hezekiah came to Isaiah.
Sa’ad da shugabannin Sarki Hezekiya suka zo wurin Ishaya,
6 And Isaiah said unto them, Thus shall ye say unto your master, Thus hath said the Lord, Be not afraid because of the words which thou hast heard, with which the boys of the king of Assyria have blasphemed me.
sai Ishaya ya ce musu, “Ku faɗa wa maigidanku cewa, ‘Ga abin da Ubangiji ya faɗa. Kada ka ji tsoron abin da ka ji, maganganun nan da bayin sarkin Assuriya suka yi mini saɓo.
7 Behold, I will put an [other] spirit in him, and when he will hear a rumor, he shall return to his own land; and I will cause him to fall by the sword in his own land.
Ka saurara! Zan sa ruhuna a cikinsa saboda sa’ad da ya ji wani labari, zai koma zuwa ƙasarsa, a can kuwa zan sa a kashe shi da takobi.’”
8 And Rabshakeh returned, and found the king of Assyria warring against Libnah; for he had heard that he was departed from Lachish.
Sa’ad da sarkin yaƙin ya ji cewa sarkin Assuriya ya bar Lakish, sai ya janye ya kuma sami sarki yana yaƙi da Libna.
9 And he heard it said of Thirhakah the king of Ethiopia, He is come out to fight with thee. And when he had heard it, he sent messengers to Hezekiah, saying,
To, fa, Sennakerib ya sami labari cewa Tirhaka, mutumin Kush sarkin Masar, yana fitowa don yă yi yaƙi da shi. Sa’ad da ya ji haka, sai ya aiki jakadu zuwa wurin Hezekiya da wannan magana.
10 Thus shall ye say to Hezekiah the king of Judah, as followeth, Let not thy God, in whom thou trustest, deceive thee, saying, Jerusalem shall not be given up into the hand of the king of Assyria.
“Ku faɗa wa Hezekiya sarkin Yahuda cewa kada ka bar allahn da ka dogara a kai ya ruɗe ka sa’ad da ya ce, ‘Ba za a ba da Urushalima ga sarkin Assuriya ba.’
11 Behold, thou thyself hast heard what the kings of Assyria have done to all the lands by destroying them utterly: and thou alone shouldst be delivered?
Tabbatacce ka ji abin da sarakunan Assuriya suka aikata ga dukan ƙasashe, suna hallaka su tas. Kai kuwa za ka tsira ne?
12 Have the gods of the nations which my fathers destroyed delivered them, as Gozan, and Charan, and Rezeph, and the children of 'Eden, who were in Thelassar?
Allolin al’umman da kakannina suka hallaka sun cece su ne, allolin Gozan, Haran, Rezef da kuma na mutanen Eden waɗanda suke zama a Tel Assar?
13 Where is the king of Chamath, and the king of Arpad, and the king of the city of Sepharvayim, of Hena', and 'Ivvah?
Ina sarkin Hamat yake, sarkin Arfad fa, sarkin Sefarfayim, ko na Hena ko na Iffa?”
14 And Hezekiah took the letter out of the hand of the messengers, and read it: and Hezekiah went up unto the house of the Lord, and spread it out before the Lord.
Hezekiya ya karɓi wasiƙar daga jakadun ya karanta ta. Sa’an nan ya haura zuwa haikalin Ubangiji ya shimfiɗa ta a gaban Ubangiji.
15 And Hezekiah prayed unto the Lord, saying,
Sai Hezekiya ya yi addu’a ga Ubangiji ya ce,
16 O Lord of hosts, the God of Israel, who dwellest between the cherubim, thou art the [true] God, thou alone, for all the kingdoms of the earth; [for] it is thou who hast made the heavens and earth.
“Ya Ubangiji Allah Maɗaukaki, Allah na Isra’ila, zaune a tsakanin kerubobi, kai kaɗai ne Allah a kan dukan masarautan duniya.
17 Bend down, O Lord, thy ear, and hear; open, O Lord, thy eye, and see: and hear all the words of Sennacherib, which he hath sent to blaspheme the living God.
Ka kasa kunne, ya Ubangiji, ka kuma ji; ka buɗe idanunka, ya Ubangiji, ka kuma gani; ka saurara ga dukan maganganun da Sennakerib ya aika don yă zagi Allah mai rai.
18 Truly, Lord, the kings of Assyria have devastated all the nations, and their land;
“Gaskiya ce, ya Ubangiji, cewa sarakunan Assuriyawa sun mai da dukan waɗannan mutane da ƙasashensu kango.
19 And they have placed their gods into the fire; for they are no gods, but the work of man's hands, wood and stone; and these have they destroyed.
Sun jefar da gumakansu cikin wuta suka kuma hallaka su, gama su ba alloli ba ne itace ne kawai da dutse, da hannuwan mutane suka sarrafa.
20 And now, O Lord our God, save us out of his hand, that all the kingdoms of the earth may know that thou art the Lord, thou alone.
Yanzu, ya Ubangiji Allahnmu, ka cece mu daga hannunsa, saboda masarautai a duniya su san cewa kai kaɗai ne, ya Ubangiji, Allah.”
21 Then sent Isaiah the son of Amoz unto Hezekiah, saying, Thus hath said the Lord the God of Israel, Whereas thou hast prayed to me concerning Sennacherib the king of Assyria:
Sa’an nan Ishaya ɗan Amoz ya aika da saƙo wa Hezekiya cewa, “Ga abin da Ubangiji, Allah na Isra’ila, ya faɗa. Saboda ka yi addu’a gare ni game da Sennakerib sarkin Assuriya,
22 This is the word that the Lord hath spoken over him: She despiseth thee, she laugheth thee to scorn, the virgin daughter of Zion; behind she shaketh her head, the daughter of Jerusalem.
ga abin da maganar Ubangiji ya faɗa a kansa, “Budurwa Diyar Sihiyona ta rena tana kuma maka ba’a. Diyar Urushalima tana kada kai yayinda kake gudu.
23 Whom hast thou blasphemed, and [whom] hast thou scorned? and against whom hast thou raised thy voice, and lifted up thy eyes on high? against the Holy One of Israel.
Wane ne ka zargi ka kuma yi wa saɓo? A kan wa ka tā da muryarka ka kuma daga idanu cikin fariya? A kan Mai Tsarkin nan na Isra’ila!
24 Through thy servants hast thou blasphemed the Lord, and hast said, With the multitude of my chariots am I indeed come up to the height of the mountains, to the sides of Lebanon; and I will cut down its tall cedars, the choice of its fir-trees: and I will enter into the height of its summit, the forest of its fruitful soil.
Ta wurin jakadunka ka jibge zage-zage a kan Ubangiji. Ka kuma ce, ‘Da kekunan yaƙina masu yawa na hau ƙwanƙolin duwatsu, ƙwanƙolin mafi tsayi na Lebanon. Na sassare al’ul mafi tsayi fir mafi kyau. Na kai can wuri mafi nisa na kurminsa.
25 I have dug, and drunk water; and I will dry up with the sole of my feet all the streams of besieged places.
Na haƙa rijiyoyi a baƙuwar ƙasa na kuma sha ruwa a can. Da tafin ƙafafuna na busar da dukan rafuffukan Masar.’
26 Hadst thou not heard, that in distant ages I had prepared this? in the times of antiquity when I formed it? now have I brought it along, and it came to pass to desolate into ruinous heaps fortified cities.
“Ba ka ji ba cewa tun dā can na shirya ya zama haka? A kwanakin dā na kafa shi; yanzu na sa ya faru, cewa ka mai da birane masu mafaka zuwa tsibin ɓuraguzai.
27 And thus their inhabitants were of short power, they were discouraged and confounded: they were as the herbs of the field, and as the green grass; as the moss on the housetops, and as corn blasted before the ear appeareth.
Mutanensu, suka rasa ƙarfi, sun firgita suka kuma sha kunya. Suka zama kamar tsire-tsire a gona, kamar tsire-tsiren ta suka tohu, kamar ciyawar da ya tsiro a kan rufi, wadda zafi ya yi wa ƙuna kafin tă yi girma.
28 But thy abiding, and thy going out, and thy coming in do I know, and thy raging against me.
“Amma na san inda kake zama da sa’ad da kakan fita ka kuma koma da yadda ka harzuƙa gāba da ni.
29 Because of thy raging against me, and thy tumult, that is come up into my ears, will I put my hook in thy nose, and my bridle between thy lips, and I will cause thee to turn back on the way by which thou camest.
Saboda ka harzuƙa gāba da ni kuma saboda girmankanka ya kai kunnuwana, zan sa ƙugiya a hancinka linzamina a bakinka, zan kuma sa ka koma ta hanyar da ka zo.
30 And this shall be unto thee the sign, Ye shall eat this year what groweth of itself, and in the second year what springeth after the same; and in the third year sow, and reap, and plant vineyards, and eat their fruit.
“Wannan zai zama alama gare ka, ya Hezekiya, “Wannan shekara za ka ci abin da ya yi girma da kansa, shekara ta biyu kuma abin da ya tsiro daga wancan. Amma a shekara ta uku za ka yi shuki ka kuma girba, za ka dasa gonakin inabi ka kuma ci’ya’yansu.
31 And the remnant of the house of Judah that is escaped shall yet strike root downward, and bear fruit upward.
Sauran da suka rage na gidan Yahuda kuwa za su yi saiwa a ƙarƙashi su kuma ba da’ya’ya a bisa.
32 For out of Jerusalem shall go forth a remnant, and that which escapeth out of Mount Zion: the zeal of the Lord of hosts will do this.
Gama daga Urushalima raguwa za tă fito, kuma daga Dutsen Sihiyona ƙungiyar waɗanda suka tsira. Himmar Ubangiji Maɗaukaki zai cika wannan.
33 Therefore thus hath said the Lord concerning the king of Assyria, He shall not come into this city, and he shall not shoot an arrow thereon, nor come before it with shields, nor cast up an embankment against it.
“Saboda haka ga abin da Ubangiji yana cewa game da sarkin Assuriya, “Ba zai shiga wannan birni ba ya harbe kibiya a nan. Ba zai zo gabansa da garkuwa ba ko ya gina mahaurai kewaye a kansa ba.
34 On the way by which he came, by the same shall he return, and into this city shall he not come, saith the Lord.
Ta hanyar da ya zo da ita zai koma; ba zai shiga wannan birni ba,” in ji Ubangiji.
35 And I will shield this city to save it for my own sake, and for the sake of David my servant.
“Zan kāre wannan birni in kuma cece shi, saboda girmana da kuma saboda sunan Dawuda bawana!”
36 Then went out an angel of the Lord, and smote in the camp of the Assyrians one hundred and eighty and five thousand men; and when people arose early in the morning, behold, they were all dead corpses.
Sai mala’ikan Ubangiji ya fita ya kuma karkashe mutane dubu ɗari da dubu tamanin da dubu biyar a sansanin Assuriya. Sa’ad da mutane suka farka kashegari, sai ga gawawwaki duk a kwance!
37 And Sennacherib the king of Assyria departed, and went and returned, and dwelt at Nineveh.
Saboda haka Sennakerib sarkin Assuriya ya janye. Ya koma zuwa Ninebe ya zauna a can.
38 And it came to pass, as he was prostrating himself in the house of Nisroch his god, that Adrammelech and Sharezer his sons smote him with the sword; and they escaped into the land of Ararat. And Essar-chaddon his son became king in his stead.
Wata rana, yayinda yake yin sujada a haikalin allahnsa Nisrok,’ya’yansa maza Adrammelek da Sharezer suka kashe shi da takobi, suka kuma gudu zuwa ƙasar Ararat. Esar-Haddon ɗansa kuwa ya gāje shi a matsayin sarki.