< Isaiah 29 >

1 Woe to Ariel, to Ariel, the town where David dwelt! add ye year to year; let the festivals come round in order;
Kaitonki, Ariyel, Ariyel birnin da Dawuda ya zauna! Ƙara shekara ga shekara a kuma bar shagulgulanki su yi ta kewayewa.
2 Yet will I distress Ariel, and there shall be groaning and wailing: and it shall be unto me like Ariel.
Duk da haka zan yi wa Ariyel kwanto za tă kuma yi kuka da makoki, za tă zama mini kamar bagaden jini.
3 And I will encamp against thee round about, and will lay siege against thee with hostile posts, and I will raise up entrenchments against thee.
Zan kafa sansani kewaye da ke duka; zan kewaye ki da hasumiyoyi in tasar miki da ayyukan kwantona na yaƙi.
4 And brought down low, shalt thou speak [as though] out of the earth, and out of the dust shall come forth thy speech; and like one of a familiar spirit out of the earth shall be thy voice, and out of the dust shalt thou whisper forth thy speech.
Za a ƙasƙantar da ke, za ki ƙi yin magana daga ƙasa; maganarki za tă yi ƙasa-ƙasa daga ƙura. Muryarki za tă zama kamar fatalwa daga ƙasa; daga ƙura maganarki zai fito ƙasa-ƙasa.
5 And like the small dust shall be the multitude of thy barbarian enemies, and like the passing chaff the multitude of tyrants; and [this] shall be at unawares, suddenly.
Amma abokan gābanki masu yawa za su zama kamar ƙura mai laushi, sojojinsu masu firgitarwa za su yi ta tashi kamar yayin da iska ta hura. Farat ɗaya, cikin ɗan lokaci,
6 From the Lord of hosts shall the visitation come with thunder, and with earthquake, and great noise, with storm and tempest, and the devouring flame of fire.
Ubangiji Maɗaukaki zai zo da tsawa da rawar ƙasa da ƙara mai girma, da hadarin iska da guguwa da harshe na wuta mai ci.
7 And as a dream of a night-vision shall be the multitude of all the nations that go to war against Ariel, even all that fight against her and raise towers against her, and that distress her.
Sa’an nan sojojin dukan al’umman da suka yi yaƙi da Ariyel, da suka fāɗa mata da kagararta suka kuma yi mata kwanto, za su zama kamar yadda yake da mafarki, wahayi da dare,
8 And it shall even be as when a hungry man dreameth, that, behold, he eateth; but he awaketh, and his soul is empty; or as when a thirsty man dreameth, that, behold, he drinketh; but he awaketh, and, behold, he is faint, and his soul yet longeth: so shall it be with the multitude of all the nations, that go to war against mount Zion.
kamar sa’ad da mai yunwa yana mafarki cewa yana cin abinci, amma sai ya farka, yunwan tana nan; kamar sa’ad da mai ƙishirwa yana mafarki cewa yana shan ruwa, amma sai ya farka yana suma, da ƙishinsa. Haka zai zama da sojoji na dukan al’ummai da suka yi yaƙi da Dutsen Sihiyona.
9 Stay but still and wonder; turn your eyes away, and be blinded; they are drunken, but not with wine; they stagger, but not with strong drink.
Ku firgita ku kuma yi mamaki, ku makance kanku ku kuma zama a makance; ku bugu, amma ba da ruwan inabi ba, ku yi tangaɗi, amma ba daga barasa ba.
10 For the Lord hath poured out over you the spirit of deep sleep, and hath closed your eyes: [over] the prophets, and your chiefs, the seers, hath he cast a vail.
Ubangiji ya kawo muku barci mai nauyi, Ya rufe idanunku (annabawa); ya rufe kawunanku (masu duba).
11 And the vision of every thing is become unto you as the words of a book that is sealed, which men deliver to one that can read, saying, Read this, I pray thee; and he saith, I cannot; for it is sealed:
Gare ku duk wannan wahayi ba kome ba ne sai dai maganganun da aka rufe a cikin littafi. In kuma kun ba da littafin ga wani wanda zai iya karanta, kuka kuma ce masa, “Karanta wannan, muna roƙonka,” zai amsa ya ce, “Ba zan iya ba; an rufe shi.”
12 And the book is then delivered to one that cannot read, saying, Read this, I pray thee; and he saith, I cannot read.
Ko kuwa in kun ba da littafin ga wani wanda ba zai iya karantawa ba, kuka kuma ce, “Karanta wannan, muna roƙonka,” zai amsa ya ce, “Ban iya karatu ba.”
13 And the Lord said, Forasmuch as this people draw near with their mouth, and with their lips do honor me, but have removed their heart far from me, and their fear toward me is but the acquired precept of men;
Ubangiji ya ce, “Waɗannan mutane sun zo kusa da ni da bakinsu suka kuma girmama ni da leɓunansu, amma zukatansu suna nesa daga gare ni. Sujadar da suke mini cike take da dokokin da mutane suka koyar.
14 Therefore, behold, I will do yet farther a marvelous work with this people, doing wonder on wonder; so that the wisdom of their wise men shall be lost, and the understanding of their prudent men shall be hidden.
Saboda haka zan firgita waɗannan mutane sau ɗaya da abubuwan banmamaki a kan abubuwan banmamaki; hikimar masu hikima za tă lalace, azancin masu azanci zai ɓace.”
15 Woe unto those that seek to hide deeply their counsel from the Lord, so that their works may be in the dark, and they say, Who seeth us? and who knoweth us?
Kaiton waɗanda suke zuwa manyan zurfafa don su ɓoye shirye-shiryensu daga Ubangiji, waɗanda suke aikinsu cikin duhu su yi tunani, “Wa yake ganinmu? Wa zai sani?”
16 Oh your perverseness! shall the potter be esteemed as the clay? that the work shall say of its maker, He hath not made me? or shall the thing framed say of its framer, He had no understanding?
Kuna birkitar abubuwa, sai ka ce an mayar da mai ginin tukwane ya zama yumɓu! Abin da aka yi zai ce wa wanda ya yi shi, “Ba shi ne ya yi ni ba”? Tukunya za tă iya ce wa mai ginin tukwane, “Ba ka san kome ba”?
17 Lo! but yet a very little while more, and Lebanon shall be turned into a fruitful field, and the fruitful field shall be esteemed as a forest!
Cikin ɗan lokaci, za a mai da Lebanon gona mai taƙi kuma gona mai taƙi za tă zama kamar kurmi?
18 And on that day shall the deaf hear the words of the book, and out of obscurity, and out of darkness, shall the eyes of the blind see.
A wannan rana kurame za su ji maganganun littafi, daga duruduru da duhu kuma idanun makafi za su gani.
19 And the sufferers shall have abundant joy in the Lord, and the needy among men shall be glad in the Holy One of Israel.
Masu tawali’u za su sāke yin farin ciki a cikin Ubangiji; mabukata za su yi farin ciki cikin Mai Tsarkin nan na Isra’ila.
20 For the tyrant is no more, and consumed is the scorner, and cut off are all that watch for injustice;
Masu zalunci za su ƙare, masu ba’a za su ɓace, kuma dukan waɗanda suke da ido don mugunta za su hallaka,
21 That cause mankind to sin by [their] word; and lay a snare for him that reproveth [them] in the gate; and pervert through fraud the cause of the just.
waɗanda ta magana kawai sukan mai da mutum mai laifi, waɗanda suke kafa tarko wa mai ba da kāriya a ɗakin shari’a da shaidar ƙarya kuma su hana marar laifi samun shari’ar adalci.
22 Therefore thus hath said the Lord unto the house of Jacob, he who hath redeemed Abraham, Not now shall Jacob be ashamed, and not now shall his face be made pale.
Saboda haka ga abin da Ubangiji wanda ya fanshi Ibrahim, ya ce wa gidan Yaƙub, “Ba za a ƙara kunyata Yaƙub ba; fuskokinsu kuma ba za su ƙara yanƙwanewa ba.
23 For when he seeth his children, the work of my hands in the midst of him, how they sanctify my name: then will they sanctify the Holy One of Jacob, and the God of Israel will they reverence.
Sa’ad da suka ga’ya’yansu a tsakiyarsu, aikin hannuwansu, za su kiyaye sunana da tsarki; za su san tsarkin Mai Tsarkin nan na Yaƙub, za su kuma ji tsoron Allah na Isra’ila.
24 They also that were erring in spirit shall acquire understanding, and they that murmured shall obtain instruction.
Su da suke marasa azanci a ruhu za su sami fahimtar; waɗanda suke gunaguni za su yarda da koyarwa.”

< Isaiah 29 >