< Isaiah 14 >

1 For the Lord will have mercy on Jacob, and will again make choice of Israel, and replace them in their own land: and the strangers shall be joined unto them, and they shall attach themselves to the house of Jacob.
Ubangiji zai yi wa Yaƙub jinƙai; zai sāke zaɓi Isra’ila yă kuma zaunar da su a ƙasarsu. Baƙi ma za su zo su zauna tare da su su haɗa kai da gidan Yaƙub.
2 And nations shall take them, and bring them to their own place; but the house of Israel shall obtain possession of them in the land of the Lord for men-servants and for maid-servants; and they shall take captive their captors, and they shall rule over their oppressors.
Al’ummai za su ɗauke su su kuma kawo wurin da yake nasu. Gidan Isra’ila kuwa za tă mallaki al’ummai a matsayin bayi maza da mata a ƙasar Ubangiji. Za su mai da waɗanda suka kama su su zama kamammu su kuma yi mulki a kan waɗanda suka taɓa danne su.
3 And it shall come to pass on the day when the Lord will give thee rest from thy trouble, and from thy vexation, and from the hard bondage wherein thou wast made to serve,
A ranar da Ubangiji ya hutashe ku daga wahala da azaba da muguwar bauta,
4 That thou wilt take up this parable against the king of Babylon, and say, How hath ceased the oppressor! ceased the exactress of gold!
za ku yi wa sarkin Babilon wannan ba’a. Mai danniya ya zo ga ƙarshe! Dubi yadda fushinsa ya ƙare!
5 Broken hath the Lord the staff of the wicked, the sceptre of rulers;
Ubangiji ya karye sandar mugaye, sandan mulkin masu mulki,
6 He who smote people in wrath, blows without intermission, he that ruled in anger nations, persecuting without restraint.
wanda cikin fushi ya kashe mutane da bugu marar ƙarewa, kuma cikin fushi ya mamaye al’ummai da fushi ba ƙaƙƙautawa.
7 At rest, quiet is all the earth; men break forth into loud song.
Dukan ƙasashe suna hutawa suna kuma cikin salama; sun ɓarke da waƙa.
8 Also, the fir-trees rejoice at thee, the cedars of Lebanon, “Since thou wast laid low, no feller is come up against us.”
Har itatuwan fir ma da kuma al’ul na Lebanon suna murna a kanka suna cewa, “Yanzu da aka ƙasƙantar da kai, babu wani mai yankan katakon da ya zo yă yanka mu.”
9 The nether world from below is in motion concerning thee to meet thee at thy coming: it stirreth up the departed for thee, all the chief ones of the earth; it hath caused to rise up from their thrones all the kings of nations. (Sheol h7585)
Kabari a ƙarƙashi duk ya shirya don yă sadu da kai a zuwanka; yana tā da ruhohin da suka rasu don su gaishe ka, dukan waɗanda sun taɓa zama shugabanni a duniya; ya sa suka tashi daga kujerun sarauta, dukan waɗanda suke sarakuna a kan al’ummai. (Sheol h7585)
10 They all will commence and say unto thee, “Thou—thou also art become weak like us; similar unto us art thou become!”
Duk za su amsa, za su ce maka, “Ashe kai ma raunana ne, kamar mu; ka zama kamar mu.”
11 Into the nether world is brought down thy pride, the clatter of thy psalteries: beneath thee is spread the worm, and thy cover is the moth. (Sheol h7585)
An yi ƙasa da dukan alfarmarka zuwa kabari, tare da surutan garayunka; tsutsotsi sun bazu a ƙarƙashinka tsutsotsi kuma suka rufe ka. (Sheol h7585)
12 How art thou fallen from heaven, O morning-star, son of the dawn! how art thou hewn down to the ground, crusher of nations!
Yaya aka yi ka fāɗo daga sama Ya tauraron safiya, ɗan hasken asuba! An fyaɗa ka da ƙasa, kai da ka taɓa ƙasƙantar da al’ummai!
13 And thou—thou hadst said in thy heart, “Into heaven will I ascend, above the stars of God will I exalt my throne; and I will sit also upon the mount of the assembly, in the farthest end of the north;
Ka yi tunani a ranka ka ce, “Zan hau zuwa sama; zan ɗaga kursiyina sama da taurarin Allah; zan zauna a kursiyi a kan dutsen taro, a can ƙurewar saman dutse mai tsarki.
14 I will ascend above the heights of the clouds; I will be equal to the Most High.”
Zan haura can bisa gizagizai; zan mai da kaina kamar Mafi Ɗaukaka.”
15 But into the nether world shalt thou be brought down, into the lowest depth. (Sheol h7585)
Amma ga shi an gangara da kai zuwa kabari, zuwa zurfafan rami. (Sheol h7585)
16 They that see thee will gaze at thee, will regard thee well, [saying, ] “Is this the man that caused the earth to tremble, that made kingdoms quake?
Waɗanda suka gan ka sun zura maka ido, suna tunani abin da zai same ka. “Wannan mutumin ne ya girgiza duniya ya kuma sa mulkoki suka razana,
17 That rendered the world as a wilderness, and pulled down its cities: never opened the prison-house of his prisoners?”
mutumin da ya mai da duniya ta zama hamada, wanda ya tumɓuke biranenta bai kuma bar kamammunsa suka tafi ba?”
18 All the kings of nations, all of them, lie in glory, every one in his own [eternal] house.
Dukan sarakunan duniya suna kwance a mace, kowa a kabarinsa.
19 But thou—thou art cast out of thy grave like a discarded offshoot, as a garment of those that are slain, pierced by the sword, that go down to the stones of the pit, as a carcass trodden under foot.
Amma an jefar da kabarinka kamar reshen da aka ƙi; an rufe ka da waɗanda aka kashe, tare da waɗanda aka soke da takobi, waɗanda suka gangara zuwa duwatsun rami. Kamar gawar da aka tattake da ƙafa,
20 Thou shalt not be united with them in burial; because thy land hast thou destroyed, thy people hast thou slain: to eternity shall not be called the seed of evil-doers.
ba za a haɗa ka tare da su a jana’iza ba, gama ka hallaka ƙasarka ka kuma kashe mutanenka. Ba za a ƙara ambaci zuriyarka masu aikata mugunta ba.
21 Prepare for his children the slaughter, for the iniquity of their fathers: that they may not rise, and possess the land, and fill the face of the world with enemies [of mankind].
A shirya wuri don a yayyanka’ya’yansa maza saboda zunuban kakanninsu; kada a reno su su gāji ƙasar su cika duniya da biranensu.
22 And I will rise up against them, saith the Lord of hosts; and I will cut off from Babylon name, and remnant, and son, and grandson, saith the Lord.
“Zan yi gāba da su,” in ji Ubangiji Maɗaukaki. “Zan kau da sunan Babilon da waɗanda suka rage da rai a cikinta,’ya’yanta da zuriyarta,” in ji Ubangiji.
23 I will also make it a possession for the hedgehog, and pools of water: and I will sweep it with the besom of destruction, saith the Lord of hosts.
“Zan mai da ita wuri domin mujiyoyi da kuma fadama; zan share ta da tsintsiyar hallaka,” Ni Ubangiji Maɗaukaki na faɗa.
24 Sworn hath the Lord of hosts, saying, Surely as I have purposed, so doth it come to pass; and as I have resolved, so shall it occur:
Ubangiji Maɗaukaki ya rantse, “Tabbatacce, kamar yadda na riga na shirya, haka zai kasance, kuma kamar yadda na nufa, haka zai zama.
25 To break Asshur in my own land, and upon my mountains will I tread him under foot; then shall his yoke be removed from off them, and his burden from off their shoulders.
Zan ragargazar da Assuriya a cikin ƙasata; a kan duwatsuna zan tattake shi. Za a ɗauke nauyin da ya sa wa mutanena, a kuma ɗauke nauyinsa daga kafaɗunsu.”
26 This is the resolve that is resolved over all the earth: and this is the hand that is stretched out over all the nations.
Wannan shi ne shirin da na yi domin dukan duniya; wannan shi ne hannun da aka miƙa a bisa dukan al’ummai ke nan.
27 For the Lord of hosts hath resolved, and who shall frustrate it? and it is his hand which is stretched out, and who shall turn it back?
Gama Ubangiji Maɗaukaki ya ƙudura ya yi wannan, wa kuwa zai hana shi? Ya riga ya miƙa hannunsa, wa zai komar da shi?
28 In the year king Achaz died was this prophecy [given].
Wannan abin da Allah ya yi magana ya zo ne a shekarar da Sarki Ahaz ya mutu.
29 Rejoice not, thou entire Palestine, because the rod of him that smote thee is broken; for out of the serpent's root shall come forth an adder, and its fruit shall be a flying dragon.
Kada ku yi farin ciki, dukanku Filistiyawa, cewa sandar da ta buge ku ta karye; daga saiwar wannan maciji wani mugun maciji mai dafi zai taso,’ya’yansa za su zama wani maciji masu dafi mai tashi sama.
30 And the first-born of the poor shall feed, and the needy shall rest in safety: and I will kill with famine thy root, and men shall slay thy remnant.
Mafi talauci na matalauta zai sami wurin kiwo, mabukata kuma za su kwana lafiya. Amma zan hallakar da saiwarka da matsananciyar yunwa; za tă kashe naka da suka rage da rai.
31 Wail, O gate; cry out, O city; thou art dissolved, O thou entire Palestine; for from the north a smoke is coming, and there is no one solitary among those that are bidden to come.
Ki yi ihu, ya ke ƙofa! Yi kururuwa, ya ke birni! Ku razana, dukanku Filistiyawa! Ƙunshin hayaƙi yana tasowa daga arewa, kuma babu matsorata a cikin sojojinsa.
32 And what will each one of the messengers of the nation answer? That the Lord hath founded Zion; and that therein shall find protection the poor of his people.
Wace amsa ce za a bayar wa jakadun wannan al’umma? “Ubangiji ya kafa Sihiyona, kuma a cikinta mutanensa masu shan azaba za su sami mafaka.”

< Isaiah 14 >