< Isaiah 11 >

1 And there shall come forth a shoot out of the stem of Jesse, and a sprout shall spring out of his roots.
Toho zai fito daga kututturen Yesse; daga saiwarsa Reshe zai ba da’ya’ya.
2 And there shall rest upon him the spirit of the Lord, the spirit of wisdom and understanding, the spirit of counsel and might, the spirit of knowledge and of the fear of the Lord;
Ruhun Ubangiji zai kasance a kansa, Ruhun hikima da na fahimta, Ruhun shawara da na iko, Ruhun sani da na tsoron Ubangiji,
3 And he shall be animated by the fear of the Lord; and not after the sight of his eyes shall he judge, and not after the hearing of his ears shall he decide;
zai kuwa ji daɗin tsoron Ubangiji. Ba zai yi hukunci ta wurin abin da ya gani da idanunsa ba, ba zai kuwa yanke shawara ta wurin abin da ya ji da kunnuwansa ba;
4 But he shall judge with righteousness the poor, and decide with equity for the suffering ones of the earth; and he shall smite the earth with the rod of his mouth, and with the breath of his lips shall he slay the wicked.
amma da adalci zai yi wa masu bukata shari’a, da gaskiya zai yanke shawarwari saboda matalautan duniya. Kamar sanda zai bugi duniya da maganar bakinsa; da numfashin leɓunansa zai yanke mugaye.
5 And righteousness shall be the girdle of his loins, and faithfulness the girdle of his hips.
Adalci ne zai zama abin ɗamararsa aminci kuma igiyar da zai ɗaura kewaye da gindinsa.
6 And the wolf shall dwell with the sheep, and the leopard shall lie down with the kid; and the calf and the young lion and the fatling [shall be] together, and a little boy shall lead them.
Kyarkeci zai zauna tare da ɗan rago damisa za tă kwanta tare da akuya, ɗan maraƙi da zaki da ɗan saniya za su yi kiwo tare; ɗan yaro ne zai lura da su.
7 And the cow and the she-bear shall feed, together shall their young ones lie down: and the lion shall like the ox eat straw.
Saniya da beyar za su yi kiwo tare, ƙananansu za su kwanta tare, zaki kuma zai ci ciyawa kamar saniya.
8 And the sucking child shall play on the hole of the asp, and on the basilisk's den shall the weaned child stretch out his hand.
Jariri zai yi wasa kurkusa da ramin gamsheƙa, ɗan yaro kuma zai sa hannunsa a ramin maciji mai mugun dafi.
9 They shall not do hurt nor destroy on all my holy mountain: for the earth shall be full of the knowledge of the Lord, as the waters cover the sea.
Ba za su yi lahani ko su hallaka wani a dutsena mai tsarki ba, gama duniya za tă cika da sanin Ubangiji kamar yadda ruwaye suka rufe teku.
10 And it shall happen on that day, that [he of] the root of Jesse, who shall stand as an ensign of the people, to him shall nations [come to] inquire: and his resting-place shall be glorious.
A wannan rana Saiwar Yesse zai miƙe kamar tuta don mutanenta; al’ummai za su tattaru wurinsa, wurin hutunsa kuma zai zama mai daraja.
11 And it shall happen on that day, that the Lord will put forth his hand again the second time to acquire the remnant of his people, which shall remain, from Asshur and from Egypt, and from Pathros, and from Cush, and from 'Elam, and from Shin'ar, and from Chamath, and from the islands of the sea.
A wannan rana Ubangiji zai miƙa hannunsa sau na biyu don yă maido da raguwar da ta rage na mutanensa daga Assuriya, daga Masar ta Ƙasa, daga Masar ta Bisa, daga Kush, daga Elam, daga Babiloniya, daga Hamat da kuma daga tsibiran teku.
12 And he will lift up an ensign unto the nations, and will assemble the outcasts of Israel; and the dispersed of Judah will he collect together from the four corners of the earth.
Zai tā da tuta saboda al’ummai yă kuma tattara masu zaman bauta na Isra’ila; zai tattara mutanen Yahuda da suke a warwatse kusurwoyi huɗu na duniya.
13 And then shall depart the envy of Ephraim, and the adversaries of Judah shall be cut off: Ephraim shall not envy Judah, and Judah shall not assail Ephraim.
Kishin Efraim zai ɓace, za a kuma kau da abokan gāban Yahuda; Efraim ba zai yi kishin Yahuda ba, haka ma Yahuda ba zai yi gāba da Efraim ba.
14 But they shall fly upon the shoulders of the Philistines toward the west; together shall they spoil the children of the east: upon Edom and Moab shall they lay their hands; and the children of 'Ammon shall obey them.
Tare za su fāɗa wa Filistiyawa da yaƙi daga yamma; tare za su washe mutane wajen gabas. Za su ɗibiya hannuwa a kan Edom da Mowab, Ammonawa kuma za su yi musu biyayya.
15 And the Lord will destroy the tongue of the Egyptian sea; and swing his hand over the river with his mighty wind, and will smite it into seven streams, and render it passable with shoes.
Ubangiji zai busar da bakin tekun Masar; da iska mai zafi zai share hannunsa a bisa Kogin Yuferites Zai rarraba shi yă zama ƙanana rafuffuka bakwai saboda mutane su iya hayewa da ƙafa.
16 And there shall be a highway for the remnant of his people, which shall remain from Asshur, like as it was to Israel on the day that they came up out of the land of Egypt.
Za a yi babbar hanya saboda raguwa mutanensa da ta rage daga Assuriya, kamar yadda ta kasance wa Isra’ila sa’ad da suka fito daga Masar.

< Isaiah 11 >