< Hosea 9 >

1 Rejoice not, O Israel, for gladness, as other people; for thou art gone astray, unfaithful to thy God: thou hast loved the wages of sin upon every corn-filled threshing-floor.
Kada ku yi farin ciki, ya Isra’ila; kada ku yi murna kamar waɗansu al’ummai. Gama kun yi rashin aminci ga Allahnku; kuna son hakkokin karuwa a kowace masussuka.
2 The threshing-floor and the wine-press shall not feed them, and the new wine shall deceive them.
Masussukai da wuraren matsin inabi ba za su ciyar da mutane ba; sabon ruwan inabi zai kāsa musu.
3 They shall not dwell in the land of the Lord; but Ephraim shall return to Egypt, and in Assyria will they eat unclean things.
Ba za su ci gaba da zama a ƙasar Ubangiji ba; Efraim zai koma Masar yă kuma ci abinci marar tsarki a Assuriya.
4 They shall not pour out wine to the Lord, and [their offerings] shall not be pleasing unto him; their sacrifices shall be unto them as the bread of mourners; all that eat thereof shall be polluted: for this their food can only be for themselves, it shall not come into the house of the Lord.
Ba za su zuba hadayun ruwan inabi ga Ubangiji ba, ba kuwa hadayunsu za su gamshe shi ba. Irin hadayun nan za su zama musu kamar burodin masu makoki; duk wanda ya ci su zai ƙazantu. Wannan abincin zai zama na kansu ne; ba zai zo cikin haikalin Ubangiji ba.
5 What will ye do on the day of the appointed festival, and on the day of the feast of the Lord?
Me za ku yi a ƙayyadaddiyar ranar bukukkuwarku, a ranakun bikin Ubangiji?
6 For, lo, they are gone forth because of the desolation: Egypt will gather them up, Moph will bury them: the pleasant chambers for their silver, —these shall nettles take possession of; thorns shall [grow] in their tents.
Ko da sun kuɓuta daga hallaka, Masar za tă tattara su, Memfis kuma za tă binne su. Sarƙaƙƙiya za tă mamaye kayan azurfansu, ƙayayyuwa su tsiro a cikin tentunansu.
7 Come are the days of the visitation, come are the days of thy recompense; this shall Israel experience: a fool was the prophet, mad the inspired man, because of the greatness of thy iniquity, and the great hatefulness.
Kwanakin hukunci suna zuwa, kwanakin ba da lissafi suna a kusa. Bari Isra’ila su san da wannan. Saboda zunubanku sun yi yawa ƙiyayyarku kuma ta yi yawa, har ake ɗauka annabi wawa ne, mutumin da aka iza kuwa mahaukaci.
8 The watchman of Ephraim with my God, the prophet, was a snare of the fowler on all his ways, a hateful thing in the house of his god.
Annabi, tare da Allahna, su ne masu tsaro a bisa Efraim, duk da haka tarko na jiransa a dukan hanyoyi, da kuma ƙiyayya a cikin gidan Allahnsa.
9 They are deeply corrupt, as in the days of Gib'ah: he will remember their iniquity, he will visit their sins.
Sun nutse da zurfi cikin lalaci, kamar a kwanakin Gibeya. Allah zai tuna da muguntarsu yă kuma hukunta su saboda zunubansu.
10 Like grapes in the wilderness had I found Israel; as the first ripe fruit on the fig-tree in the first of the season had I seen your fathers; but they too went to Ba'al-pe'or: and devoted themselves unto that shameful idol, and became abominations as those they loved.
“Sa’ad da na sami Isra’ila, ya zama kamar samun inabi a hamada; sa’ad da na ga kakanninku, ya zama kamar ganin’ya’yan itace na farko a itacen ɓaure. Amma sa’ad da suka zo Ba’al-Feyor, suka keɓe kansu wa gumaka bankunya sai suka zama abubuwan banƙyama kamar abubuwan da suke ƙauna.
11 As for Ephraim, their glory shall fly away like a bird: there is no more birth, and no pregnancy, and no conception.
Darajar Efraim za tă yi firiya tă tafi kamar tsuntsu, ba haihuwa, ba juna biyu, ba ɗaukar ciki.
12 But though they were to bring up their children, yet would I bereave them, that there should be no man: yea, woe also to themselves, when I depart from them!
Ko da sun yi renon’ya’ya, zan sa su yi baƙin cikin kowannensu. Kaitonsu sa’ad da na juya musu baya!
13 Ephraim, as I have seen him like Tyre, planted in a pleasant meadow, —yet this Ephraim shall lead forth to the murderer his children.
Na ga Efraim, kamar birnin Taya, da aka kafa a wuri mai daɗi. Amma Efraim zai fitar da’ya’yansu ga masu yanka.”
14 Give them, O Lord, what thou wilt give! give them a miscarrying womb and dried-up breasts.
Ka ba su, ya Ubangiji Me za ka ba su? Ka ba su mahaifar da za su yi ɓarin ciki da busassun nono.
15 All their wickedness is in Gilgal; for there I [learnt to] hate them; for the wickedness of their doings will I drive them out of my house: I will love them no farther; all their princes are rebels.
“Saboda dukan muguntarsu a Gilgal, na ƙi su a can. Saboda ayyukansu na zunubi, zan kore su daga gidana. Ba zan ƙara ƙaunace su ba; dukan shugabanninsu’yan tawaye ne.
16 Smitten is Ephraim, their root is dried up, they shall bear no fruit; yea, though they should bring forth, yet would I slay the beloved fruit of their body.
An ka da Efraim, saiwarsu ta bushe, ba sa ba da amfani. Ko da sun haifi’ya’ya zan kashe waɗanda suka fi ƙauna.”
17 My God will reject them, because they did not hearken unto him: and they shall be wanderers among the nations.
Allahna zai ƙi su saboda ba su yi masa biyayya ba; za su zama masu yawo a cikin al’ummai.

< Hosea 9 >