< Hosea 8 >
1 Set the cornet to thy mouth. [Let the enemy come] like the eagle against the house of the Lord: because they have transgressed my covenant, and against my law have they trespassed.
“Ka sa kakaki a leɓunanka! Gaggafa tana a bisan gidan Ubangiji domin mutane sun tā da alkawarina suka kuma tayar wa dokata.
2 To me will they then cry, My God, we, Israel, know thee.
Isra’ila ta yi mini kuka, ‘Ya Allahnmu, mun yarda da kai!’
3 [But] Israel did reject the good; so let the enemy pursue him.
Amma Isra’ila sun ƙi abin da yake mai kyau; abokin gāba zai fafare su.
4 They set up kings, but not my advice: they chose princes and I knew it not: of their silver and their gold have they made themselves idols so that they will be cut off.
Suna naɗa sarakuna, ba da izinina ba; sun zaɓa shugabanni ba da yardanta ba. Da azurfa da zinariya sun ƙera gumaka wa kansu wanda zai kai zuwa ga hallakarsu.
5 Thy calf, O Samaria, hath caused thy rejection; my anger is kindled against them: how long will it be that they cannot cleanse themselves?
Ku zubar da gunkin maraƙinku, ya Samariya! Fushina yana ƙuna a kansu. Sai yaushe za su rabu da gumaka?
6 For whom Israel did also that [idol] spring; an artisan made it, and no God is it: so then shall it become broken in splinters— that calf of Samaria.
Su daga Isra’ila ne! Wannan maraƙi, mai aikin hannu ne ya yi shi; gunki ne ba Allah ba. Za a farfashe shi kucu-kucu, waccan maraƙin Samariya.
7 For the wind do they sow, and the whirlwind shall they reap: [their seed] bringeth no standing corn; the plant yieldeth no meal; but should it yield it, strangers would swallow it up.
“Gama sun shuka iska don haka za su girbe guguwa. Hatsin da yake tsaye ba shi da kai, ba zai yi tsaba ba. Ko da ya yi tsaba ma, baƙi ne za su ci.
8 Swallowed up is Israel: now are they among the nations as a vessel without any value.
An haɗiye Isra’ila; yanzu tana cikin al’ummai kamar abin da ba shi da amfani.
9 For they are needs gone up to Assyria, they who like a wild ass should dwell alone: Ephraim spendeth lovers' gifts.
Gama sun haura zuwa Assuriya kamar jakin jejin da yake yawo shi kaɗai. Efraim ya sayar da kansa ga maza.
10 But even though they should spend gifts among the nations, now will I gather them: and they shall be humbled a little through the burden of the king of princes.
Ko da yake sun sayar da kansu a cikin al’ummai, yanzu zan tattara su wuri ɗaya. Za su fara lalacewa a ƙarƙashi danniyar babban sarki.
11 Because Ephraim hath multiplied altars to sin, the altars have been unto him the means of sinning.
“Ko da yake Efraim ya gina bagadai masu yawa don hadayun zunubi, waɗannan sun zama bagade don yin zunubi.
12 I ever wrote down for him the great things of my law; but as a strange thing are they accounted.
Na rubuta musu abubuwa masu yawa na dokata, amma suka ɗauke su tamƙar wani baƙon abu ne.
13 My sacrificial offerings they slay as common flesh that they may eat it; the Lord accepteth them not in favor: now will he remember their iniquity, and visit their sins; they shall indeed return to Egypt.
Suna miƙa hadayun da aka ba ni su kuma ci nama, amma Ubangiji ba ya jin daɗinsu. Yanzu zai tuna da muguntarsu yă kuma hukunta zunubansu. Za su koma Masar.
14 For Israel forgot his Maker, and built palaces; and Judah multiplied fortified cities; but I will send a fire among his cities, and it shall devour their fine edifices.
Isra’ila ya manta da Mahaliccinsa ya kuma gina fadodi; Yahuda ya gina katanga a yawancin garuruwansa. Amma zan aiko da wuta a bisa biranensu da zai cinye kagaransu.”