< Hosea 13 >
1 When once Ephraim spoke, [all] trembled, so high was he exalted in Israel; but he offended through Ba'al, and he died.
Sa’ad da Efraim ya yi magana, mutane sun yi rawan jiki; an girmama shi a cikin Isra’ila. Amma sai ya zama mai laifi na yin wa Ba’al sujada, ya kuwa mutu.
2 And now they yet continue to sin, and have made themselves molten images of their silver, idols according to their own imagining, every one of them the work of the artisan: they say to them, They that sacrifice men may kiss the calves.
Yanzu sai yin zunubi a kai a kai suke; suna yin gumaka wa kansu daga azurfansu, da wayo suna sarrafa siffofi, dukansu aikin masu aikin hannu ne. Ana magana waɗannan mutane cewa, “Suna miƙa hadayar mutum su kuma sumbaci gumakan maruƙa.”
3 Therefore shall they be as the morning cloud, and as the dew that early passeth away, as the chaff that is driven by the whirlwind out of the threshing-floor, and as smoke out of a window.
Saboda haka za su zama kamar hazon safiya, kamar raɓar safen da yakan kakkaɓe, kamar ƙaiƙayin da ake tankaɗe daga masussuka, kamar hayaƙin da yake fita daga taga.
4 Yet I am the Lord thy God from the land of Egypt: and no god but me shalt thou know, and there is no saviour beside me.
“Amma ni ne Ubangiji Allahnku, wanda ya fitar da ku daga Masar. Ba za ku yarda da wani Allah ba sai ni, ba wani Mai Ceto in ban da ni.
5 I myself did provide for thee in the wilderness, in the land of great drought.
Na lura da ku a hamada, cikin ƙasar mai ƙunar zafi.
6 When they came to their pasture, they became sated; they were sated, and their heart was lifted up: therefore have they forgotten me.
Sa’ad da na ciyar da su sun ƙoshi; sa’ad da suka ƙoshi, sai suka fara taƙama; sai suka manta da ni.
7 And now I will be unto them as a lion: as a leopard will I lie in wait by the way.
Saboda haka zan hau kansu kamar zaki, zan ɓuya a bakin hanya kamar damisa.
8 I will meet them as a bear bereaved of her whelps, and I will rend their closed-up heart; and I will devour them there like a lioness, the beasts of the field shall rend them.
Kamar beyar da aka ƙwace mata’ya’yanta, zan fāɗa musu in ɓarke su. Kamar zaki zan cinye su; kamar naman jeji zan yayyage su.
9 Thou hast destroyed thyself, O Israel; for against me, against thy helper [didst thou rebel.]
“An hallaka ku, ya Isra’ila, domin kun tayar mini, kun tayar wa mai taimakonku.
10 Where then is now thy king, that he may save thee in all thy cities? and thy judges, since thou saidst, Give me a king, and princes?
Ina sarkinku, da zai cece ku? Ina masu mulkinku cikin dukan garuruwanku, waɗanda kuka ce, ‘Ba mu sarki da shugabanni’?
11 I give thee a king in my anger, and take him away in my wrath.
Saboda haka cikin fushina na ba ku sarki, kuma cikin hasalata na ɗauke shi.
12 Bound up is the iniquity of Ephraim, treasured up is his sin.
An yi ajiyar laifin Efraim, aka lissafta zunubansa.
13 The pains of a travailing woman shall come upon him; he is an unwise son; for he will not remain steadfast at the time of the breaking forth of the child.
Naƙuda ta zo masa kamar a mace mai haihuwa, amma shi yaro ne marar hikima; sa’ad da lokaci ya kai, ba ya zuwa inda mahaifa ta buɗe.
14 From the power of the grave would I ransom them, from death would I redeem them; [but now] where are thy plagues, O death, where is thy pestilence, O grave? compassion shall be hidden from my eyes. (Sheol )
“Zan fanshe su daga ikon kabari; zan cece su daga mutuwa. Ina annobanki, ya mutuwa? Ina hallakarka, ya kabari? “Ba zan ji tausayi ba, (Sheol )
15 Though he grow luxuriantly in the green meadows, the east wind shall come, the wind of the Lord, rising up from the wilderness, and his spring shall become dry, and his fountain shall be dried up: the same shall plunder the treasure of all precious vessels.
ko da ma ya ci gaba cikin’yan’uwansa. Iskar gabas daga Ubangiji za tă zo, tana hurawa daga hamada; maɓulɓularsa za tă kafe rijiyarsa kuma ta bushe. Za a kwashi kaya masu daraja na ɗakin ajiyarsa ganima.
16 Samaria shall meet her punishment; for she hath rebelled against her God: by the sword shall they fall; their infants shall be dashed in pieces, and their pregnant women shall be ripped up.
Dole mutanen Samariya su ɗauki laifinsu, domin sun tayar wa Allahnsu. Za a kashe su da takobi; za a fyaɗa ƙananansu da ƙasa, za a ɓarke matansu masu ciki.”