< Genesis 6 >

1 And it came to pass, when men began to multiply on the face of the earth, and daughters were born unto them,
Sa’ad da mutane suka fara ƙaruwa a duniya, aka kuma hahhaifi musu’ya’ya mata,
2 That the sons of God saw the daughters of men, that they were fair; and they took themselves wives of all whom they chose.
sai’ya’yan Allah maza suka ga cewa’ya’yan mutane mata suna da bansha’awa, sai suka zaɓi waɗanda suke so, suka aura.
3 And the Lord said, My Spirit shall not always strive for the sake of man, for that he is but flesh; yet his days [of grace] shall be a hundred and twenty years.
Sa’an nan Ubangiji ya ce, “Ruhuna ba zai zauna a cikin mutum har abada ba, saboda shi mai mutuwa ne, kwanakinsa za su zama shekaru ɗari da arba’in ne.”
4 The giants were on the earth in those days; and also after that, when the sons of God came in unto the daughters of men, and they bore children to them; these became the mighty men, who were of old the men of renown.
Nefilimawa suna nan a duniya a waɗancan kwanaki, da kuma kwanakin da suka bi baya, a sa’ad da’ya’yan Allah suka kwana da’ya’yan mutane mata, suka kuma hahhaifi musu’ya’ya. Ai, su ne jarumawan dā, mutanen da suka shahara.
5 And God saw that the wickedness of man was great on the earth, and that every imagination of the thoughts of his heart was only evil continually.
Ubangiji kuwa ya lura cewa muguntar mutum ta yi yawa a duniya, kuma kowane abin da yake tunani a zuciyarsa mugu ne kawai a kowanne lokaci.
6 And it repented the Lord that he had made man on the earth, and it grieved him at his heart.
Ubangiji ya damu da ya yi mutum a duniya, abin ya zafe shi ƙwarai.
7 And the Lord said, I will destroy the man whom I have created from the face of the earth; both man and beast, and the creeping things and the fowls of the heaven; for it repenteth me that I have made them.
Saboda haka Ubangiji ya ce, “Zan kawar da mutum, da dabbobi, da halittu masu rarrafe a ƙasa da kuma tsuntsayen sama waɗanda na halitta, daga doron ƙasa, saboda na damu da na yi su.”
8 But Noah found grace in the eyes of the Lord.
Amma Nuhu ya sami tagomashi a gaban Ubangiji.
9 These are the generations of Noah: Noah was a just, perfect man in his generation; Noah walked with God.
Ga tarihin Nuhu. Nuhu mutum ne mai adalci, marar abin zargi a cikin mutanen zamaninsa, ya kuma yi tafiya tare da Allah.
10 And Noah begat three sons, Shem, Ham, and Japheth.
Nuhu yana da’ya’ya maza uku, Shem, Ham da Yafet.
11 And the earth was corrupt before God; and the earth was filled with violence.
Duniya dai ta lalace sosai a gaban Allah, ta kuma cika da tashin hankali.
12 And God looked upon the earth, and behold, it was corrupt, for all flesh had corrupted his way upon the earth.
Allah ya ga yadda duniya ta lalace, gama dukan mutane a duniya sun lalatar da rayuwarsu.
13 And God said unto Noah, The end of all flesh is come before me; for the earth is filled with violence through them, and I will destroy them with the earth.
Saboda haka, Allah ya ce wa Nuhu, “Zan kawo ƙarshen dukan mutane, gama saboda su duniya ta cika da tashin hankali. Lalle zan hallaka su da kuma duniya.
14 Make thee an ark of gopher-wood, rooms shalt thou make in the ark, and shalt pitch it within and without with pitch.
Saboda haka ka yi wa kanka jirgi da katakon Saifires, ka yi ɗakuna a cikinsa, ka shafe shi da ƙaro ciki da waje.
15 And this is the manner in which thou shalt make it: The length of the ark shall be three hundred cubits, the breadth of it fifty cubits, and the height of it thirty cubits.
Ga yadda za ka gina shi; jirgin zai kasance mai tsawon ƙafa 45, fāɗinsa ƙafa 75, tsayinsa kuma ƙafa 45.
16 A window shalt thou make to the ark, and thou shalt finish it above, to be one cubit broad, and the door of the ark shalt thou set in the side thereof; with lower, second, and third stories shalt thou make it.
Ka yi masa rufi, ka kuma ba da fili inci 18 tsakanin rufin a kowane gefen jirgin. Ka sa ƙofa a gefen jirgin. Ka yi shi hawa uku, ka yi ƙofa a gefe.
17 And as regards myself, behold, I will bring a flood of waters upon the earth, to destroy all flesh, wherein is the breath of life, from under the heavens; every thing that is on the earth shall perish.
Ga shi zan aiko da ambaliya ruwa a duniya, in hallaka dukan mai rai da yake a ƙarƙashin sama, kowace halittar da take numfashi a cikinta. Dukan abin da yake a duniya zai hallaka.
18 But I will establish my covenant with thee; and thou shalt come into the ark, thou, and thy sons, and thy wife, and thy sons' wives with thee.
Amma zan kafa alkawarina da kai, kai kuma za ka shiga jirgin, kai da’ya’yanka maza da matarka da matan’ya’yanka tare da kai.
19 And of every living thing, of all flesh, two of every sort shalt thou bring into the ark, to keep them alive with thee: male and female shall they be.
Za ka shigar da biyu na dukan halittu masu rai, namiji da ta mace a cikin jirgin, domin su rayu tare da kai.
20 Of the fowls after their kind, and of the cattle after their kind, of every creeping thing of the earth after its kind, two of every sort shall come unto thee, to keep them alive.
Biyu na kowane irin tsuntsu, kowace irin dabba da kuma kowace irin halitta mai rarrafe a ƙasa, za su zo wurinka domin a bar su da rai.
21 And thou, for thy part, take unto thee of all food that is eaten, and thou shalt gather it to thee; and it shall be unto thee, and unto them for food.
Za ka ɗauki kowane irin abinci wanda za a ci, ka adana don yă zama abincinka da nasu.”
22 Thus did Noah; according to all that God had commanded him, so he did.
Nuhu ya yi kome kamar yadda Allah ya umarce shi.

< Genesis 6 >

The World is Destroyed by Water
The World is Destroyed by Water