< Genesis 50 >

1 And Joseph fell upon his father's face, and wept upon him, and kissed him.
Yusuf kuwa ya fāɗa a kan mahaifinsa, ya yi kuka a kansa, ya kuma sumbace shi.
2 And Joseph commanded his servants the physicians to embalm his father: and the physicians embalmed Israel.
Sa’an nan Yusuf ya umarci masu maganin da suke yin masa hidima, su shafe mahaifinsa Isra’ila da maganin hana ruɓa. Saboda haka masu maganin suka shafe shi da maganin hana ruɓa.
3 And they fulfilled for him forty days: for so they fulfill the days of those that are embalmed; and the Egyptians wept for him seventy days.
Suka ɗauki kwana arba’in cif suna yin wannan, gama kwanakin da ake bukata ke nan don shafewa da maganin hana ruɓa. Masarawa kuwa suka yi makoki dominsa kwana saba’in.
4 And when the days of his mourning were past, Joseph spoke unto the house of Pharaoh, saying, If now I have found grace in your eyes, speak, I pray you, in the ears of Pharaoh, saying,
Sa’ad da kwanakin makoki suka wuce, sai Yusuf ya ce wa iyalin gidan Fir’auna, “In na sami tagomashi a idanunku, ku yi magana da Fir’auna domina. Ku faɗa masa,
5 My father made me swear, saying, Lo, I die; in my grave, which I have dug for me in the land of Canaan, there shalt thou bury me: now therefore let me go up, I pray thee, and I will bury my father, and return again.
‘Mahaifina ya sa na yi rantsuwa, ya kuma ce, “Ina gab da mutuwa, ka binne ni a kabarin da na haƙa wa kaina a ƙasar Kan’ana.” Yanzu fa bari in haura in binne mahaifina, sa’an nan in dawo.’”
6 And Pharaoh said, Go up, and bury thy father, as he hath made thee swear.
Fir’auna ya ce, “Haura ka binne mahaifinka, kamar yadda ya sa ka rantse za ka yi.”
7 And Joseph went up to bury his father, and there went up with him all the servants of Pharaoh, the elders of his house, and all the elders of the land of Egypt,
Saboda haka Yusuf ya haura don yă binne mahaifinsa. Dukan hafsoshin Fir’auna suka yi masa rakiya tare da manyan mutanen gidan Fir’auna, da kuma dukan manyan mutanen Masar
8 And all the house of Joseph, and his brothers, and his father's house; only their little ones, and their flocks, and their herds, they left behind in the land of Goshen.
da kuma dukan membobin gidan Yusuf, da’yan’uwansa da kuma waɗanda suke na gidan mahaifinsa. Yara kaɗai da garkunansu da kuma shanunsu ne aka bari a Goshen.
9 And there went up with him both chariots and horsemen; and the encampment was very great.
Kekunan yaƙi da mahayan dawakai su ma suka haura tare da shi. Babbar ƙungiya jama’a ce ƙwarai.
10 And they came to the thrashing-floor of Atad, which is beyond Jordan, and they held there a great and very sore lamentation; and he made for his father a mourning of seven days.
Sa’ad da suka kai masussukar Atad, kusa da Urdun, sai suka yi kuka da ƙarfi da kuma mai zafi, a can Yusuf ya yi makoki kwana bakwai saboda mahaifinsa.
11 And when the inhabitants of the land, the Canaanites, saw the mourning at the thrashing-floor of Atad, they said, This is a grievous mourning to the Egyptians; wherefore the name of it was called Abel-mizrayim, which is beyond the Jordan.
Sa’ad da Kan’aniyawa waɗanda suke zama a can suka ga makokin a masussukan Atad, sai suka ce, “Masarawa suna bikin makoki na musamman.” Shi ya sa ake kira wannan wurin da yake kusa da Urdun, Abel-Mizrayim.
12 And his sons did unto him according as he had commanded them;
Haka fa’ya’yan Yaƙub maza suka yi yadda ya umarce su.
13 And his sons carried him into the land of Canaan, and buried him in the cave of the field of Machpelah, which field Abraham bought for a possession, as a burying-place, of Ephron the Hittite, before Mamre.
Suka ɗauke shi zuwa ƙasar Kan’ana suka kuma binne shi a kogon da yake cikin filin Makfela, kusa da Mamre, wanda Ibrahim ya saya tare da filin, ya zama makabarta daga Efron mutumin Hitti.
14 And Joseph returned unto Egypt, he, and his brothers, and all that were gone up with him to bury his father, after he had buried his father.
Bayan ya binne mahaifinsa, sai Yusuf ya koma Masar, tare da’yan’uwansa da kuma dukan waɗanda suka tafi tare da shi don binne mahaifinsa.
15 And when Joseph's brothers saw that their father was dead, they said, Peradventure Joseph may now hate us: and then he would certainly requite us all the evil which we have done unto him.
Sa’ad da’yan’uwan Yusuf suka ga cewa mahaifinsu ya mutu, sai suka ce, “Mai yiwuwa Yusuf yana riƙe da mu a zuciya, wataƙila zai rama dukan abubuwa marasa kyau da muka yi masa?”
16 And they sent word unto Joseph, saying, Thy father did command before his death, saying,
Saboda haka suka aika wa Yusuf suna cewa, “Mahaifinka ya bar waɗannan umarnai kafin yă rasu.
17 So shall ye say unto Joseph, O forgive, I pray thee, the trespass of thy brothers, and their sin; for evil have they done unto thee: and now, we pray thee, forgive the trespass of the servants of the God of thy father; and Joseph wept when they spoke unto him.
Ga abin da za ku ce wa Yusuf, ‘Na roƙe ka, ka gafarta wa’yan’uwanka zunubai da laifofin da suka aikata na abubuwa marasa kyau da suka yi maka.’ Yanzu muna roƙonka ka gafarta zunuban bayin Allah na mahaifinka.” Sa’ad da saƙonsu ya zo masa, sai Yusuf ya yi kuka.
18 And his brothers also went and fell down before him; and they said, Behold, we will be thy servants.
’Yan’uwansa kuwa suka zo suka fāɗi a gabansa suka ce, “Mu bayinka ne.”
19 And Joseph said unto them, Fear not; for am I in the place of God?
Amma Yusuf ya ce musu, “Kada ku ji tsoro. Ni Allah ne?
20 But as for you, though ye thought evil against me, God meant it unto good; in order to bring to pass, as it is this day, to save alive a numerous people.
Kun yi niyya ku yi mini lahani, amma Allah ya nufe wannan ya zama alheri don yă cika abin da yanzu yake faruwa, ceton rayuka masu yawa.
21 Now therefore fear ye not, I will support you, and your little ones; and he comforted them, and spoke kindly unto them.
Saboda haka, kada ku ji tsoro. Zan tanada muku da kuma’ya’yanku.” Ya sāke tabbatar musu, ya kuma yi musu magana ta alheri.
22 And Joseph dwelt in Egypt, he, and his father's house; and Joseph lived one hundred and ten years.
Yusuf ya zauna a Masar tare da dukan iyalin mahaifinsa. Ya rayu shekara ɗari da goma.
23 And Joseph saw of Ephraim children of the third generation; the children also of Machir the son of Menasseh were brought up upon Joseph's knees.
Ya kuma ga tsara ta uku ta’ya’yan Efraim. Haka ma’ya’yan Makir ɗan Manasse, an haife su aka sa a gwiwoyin Yusuf.
24 And Joseph said unto his brothers, I shall die; but God will surely visit you, and bring you up out of this land unto the land which he hath sworn to Abraham, to Isaac, and to Jacob.
Sai Yusuf ya ce wa’yan’uwansa, “Ina gab da mutuwa. Amma tabbatacce Allah zai taimake ku, yă fid da ku daga wannan ƙasa zuwa ƙasar da ya alkawarta da rantsuwa wa Ibrahim, Ishaku da kuma Yaƙub.”
25 And Joseph caused the children of Israel to swear, saying, God will surely visit you, and then shall ye carry up my bones from here.
Yusuf kuwa ya sa’ya’yan Isra’ila maza suka yi rantsuwa, ya kuma ce, “Tabbatacce Allah zai taimake ku, ku kuma dole ku ɗauki ƙasusuwana, ku haura da su daga wannan wuri.”
26 So Joseph died, being one hundred and ten years old; and they embalmed him, and he was put in a coffin in Egypt.
Yusuf kuwa ya rasu yana da shekara ɗari da goma. Bayan an shafe shi da maganin hana ruɓa, sai aka sa shi a akwatin gawa a Masar.

< Genesis 50 >