< Genesis 49 >
1 And Jacob called unto his sons, and said, Gather yourselves together, that I may tell you that which shall befall you in the last days.
Sai Yaƙub ya kira’ya’yansa maza ya ce, “Ku tattaru don in faɗa muku abin da zai faru gare ku, a kwanaki masu zuwa.
2 Gather yourselves together, and hear, ye sons of Jacob; and hearken unto Israel your father.
“Ku tattaru, ku saurara,’ya’yan Yaƙub maza; ku saurari mahaifinku, Isra’ila.
3 Reuben, thou art my first-born, my might, and the beginning of my strength; the excellency of dignity, and the excellency of power [should be thine].
“Ruben, kai ne ɗan farina, ƙarfina, alamar farko ta ƙarfina, mafi matsayi, kuma mafi iko.
4 Unstable as water, thou shalt not have the excellence; because thou wentest up to thy father's bed; then defiledst thou the one who ascended my couch.
Mai tumbatsa kamar ruwa, amma ba za ka ƙara zama mai daraja ba, gama ka hau gadon mahaifinka ka hau kujerata, ka kuma ƙazantar da shi.
5 Simeon and Levi are brethren; weapons of violence are their swords.
“Simeyon da Lawi’yan’uwa ne, takubansu makamai ne na tā da hankali.
6 Into their secret shall my soul not come; unto their assembly my spirit shall not be united; for in their anger they slew the man, and in their self-will they lamed the ox.
Ba zan shiga shawararsu ba, ba zan shiga taronsu ba, gama sun kashe maza cikin fushinsu cikin ganin dama suka kashe bijimai.
7 Cursed be their anger, for it is fierce; and their wrath, for it is cruel: I will divide them in Jacob, and scatter them in Israel.
La’ananne ne fushinsu, mai tsanani ne ƙwarai, hasalarsu kuwa, muguwa ce ƙwarai! Zan warwatsa su cikin Yaƙub in kuma daidaita su cikin Isra’ila.
8 Judah, thou art the one thy brothers shall praise, thy hand shall be on the neck of thy enemies; thy father's children shall bow down unto thee.
“Yahuda,’yan’uwanka za su yabe ka; hannuwanka za su kasance a wuyan abokan gābanka,’ya’yan mahaifinka maza za su rusuna maka.
9 Like a lion's whelp, O Judah, from the prey, my son, thou risest: he stoopeth down, he croucheth as a lion, and as a lioness, who shall rouse him up?
Kai ɗan zaki ne, ya Yahuda, ka dawo daga farauta, ɗana. Kamar zaki, yakan kwanta a miƙe, kamar zakanya, wa yake da ƙarfin halin tashe shi?
10 The sceptre shall not depart from Judah, nor a lawgiver from between his feet; until Shiloh come, and unto him shall the gathering of the people be.
Kursiyi ba zai tashi daga Yahuda ba, ba kuwa sandan mulki daga tsakani ƙafafunsa ba, sai ya zo ga wanda yake mai shi. Biyayyar al’umma kuwa tasa ce.
11 He bindeth unto the vine his foal, and to the vine-branch his ass's colt; he washeth his garments in wine, and in the blood of grapes his clothes;
Zai daure jakinsa a kuringa, aholakinsa a rassa mafi kyau; zai wanke tufafinsa cikin ruwan inabi rigunansa cikin inabi ja wur kamar jini.
12 His eyes shall be red from wine, and his teeth white from milk.
Idanunsa za su duhunce fiye da ruwan inabi, haƙorarsa farare kamar madara.
13 Zebulun shall dwell at the margin of the seas; and he shall be at the haven of ships; and his border shall be near to Zidon.
“Zebulun zai zauna a bakin teku, yă zama tasar jiragen ruwa; iyakarsa za tă nausa zuwa Sidon.
14 Issachar is a strong-boned ass, couching down between the stables.
“Issakar doki mai ƙarfi, kwance tsakanin buhunan sirdi.
15 And when he saw the resting-place that it was good, and the land that it was pleasant, he bent his shoulder to bear, and became a servant unto tribute.
Sa’ad da ya ga yadda wurin hutunsa yana da kyau da kuma daɗin da ƙasarsa take, zan tanƙware kafaɗarsa ga nauyi yă miƙa kai ga aikin dole.
16 Dan shall judge his people, as one of the tribes of Israel.
“Dan zai tanada adalci wa mutanensa kamar ɗaya cikin kabilan Isra’ila.
17 Dan shall be a serpent by the way, an adder on the path, that biteth the horse in the heels, so that his rider falleth backward.
Dan zai zama maciji a gefen hanya, kububuwa a bakin hanya, da take saran ɗiɗɗigen doki domin mahayinsa yă fāɗi da baya.
18 For thy salvation, I hope, O Lord.
“Ina zuba ido ga cetonka, ya Ubangiji.
19 Gad, troops will band against him; but he shall wound their heel.
“Masu fashi za su fāɗa wa Gad, amma zai runtume su.
20 Out of Asher cometh fat bread, and he shall yield royal dainties.
“Abincin Asher zai zama a wadace, zai yi tanadin abinci iri-iri da suka dace don sarki.
21 Naphtali is [like] a fleet hind; he bringeth pleasant words.
“Naftali sakakkiyar barewa ce da take haihuwar kyawawan’ya’ya.
22 Joseph is a fruitful bough, a fruitful bough by a spring; the branches of which run over the wall.
“Yusuf kuringa ce mai ba da amfani. Kuringa mai ba da amfani kusa da rafi wadda rassanta na hawan bango.
23 And they embittered his life, and they shot at him, and they hated him, the men of the arrows.
Da ɗaci rai mahara suka fāɗa masa; suka harbe shi babu tausayi.
24 But his bow abode in strength, and his arm and his hands remained firm; from the hands of the mighty God of Jacob, from there thou becamest the shepherd, the stone of Israel.
Amma bakansa yana nan daram hannuwansa masu ƙarfi ba sa jijjiguwa saboda hannun Maɗaukaki na Yaƙub, saboda Makiyayi, Dutsen Isra’ila,
25 From the God of thy father, who will help thee; and from the Almighty, who will bless thee, with blessings of heaven above, with blessings of the deep that coucheth beneath, with blessings of the breasts, and of the womb;
saboda Allah na mahaifinka, wanda ya taimake ka, saboda Maɗaukaki, wanda yake albarkace ka da albarkar sama da take bisa albarkun zurfafa da suke ƙarƙashin ƙasa albarkun mama da kuma mahaifa.
26 With the blessings of thy father that have excelled the blessings of my progenitors unto the utmost bound of the everlasting hills: these shall be on the head of Joseph, and on the crown of the head of him that was separated from his brothers.
Albarkun mahaifi suna da girma fiye da albarkun daɗaɗɗun duwatsu fiye da yalwar madawwaman tuddai. Bari dukan waɗannan su zauna a kan Yusuf, a goshin ɗan sarki a cikin’yan’uwansa.
27 Benjamin shall be as a wolf that rendeth: in the morning he shall devour the prey, and at evening he shall divide the spoil.
“Benyamin kyarkeci ne mai kisa; da safe yakan cinye abin da ya farauto da yamma yakan raba ganima.”
28 All these are the tribes of Israel, twelve in number; and this is what their father spoke unto them, and wherewith he blessed them; every one according to his proper blessing blessed he them.
Dukan waɗannan su ne kabilu goma sha biyu na Isra’ila, kuma abin da mahaifinsu ya faɗa musu ke nan sa’ad da ya albarkace su, yana ba kowane albarkar da ta dace da shi.
29 And he charged them and said unto them, I am to be gathered unto my people; bury me near my fathers in the cave that is in the field of Ephron the Hittite,
Sa’an nan ya ba su waɗannan umarnai ya ce, “Ina gab da a tara ni ga mutanena. Ku binne ni tare da kakannina a kogon da yake cikin filin Efron mutumin Hitti,
30 In the cave that is in the field of Machpelah, which is before Mamre, in the land of Canaan, which field Abraham bought of Ephron the Hittite, for a possession as a burying-place,
kogon da yake cikin filin Makfela, kusa da Mamre a Kan’ana, wanda Ibrahim ya saya tare da filin, yă zama makabarta daga Efron mutumin Hitti.
31 (There they buried Abraham and Sarah his wife; there they buried Isaac and Rebekah his wife; and there I buried Leah, )
A can aka binne Ibrahim da matarsa Saratu, a can aka binne Ishaku da matarsa Rebeka, a can kuma na binne Liyatu.
32 Purchasing the field and the cave that is therein from the children of Heth.
Filin tare da kogon da yake ciki, an saya daga Hittiyawa.”
33 And when Jacob had made an end of commanding his sons, he gathered up his feet into the bed; and he departed this life, and was gathered unto his people.
Sa’ad da Yaƙub ya gama ba da umarnan ga’ya’yansa maza, sai ya ɗaga ƙafafunsa zuwa gado, ya ja numfashinsa na ƙarshe, aka kuwa tara shi ga mutanensa.