< Genesis 39 >

1 And Joseph was brought down to Egypt; and Potiphar, an officer of Pharaoh, the captain of the guards, an Egyptian, bought him of the hands of the Ishmaelites, who had brought him down thither.
To, aka kai Yusuf Masar, Fotifar wani mutumin Masar wanda yake ɗaya daga cikin hafsoshin Fir’auna, shugaban masu tsaro, ya saye shi daga mutanen Ishmayel waɗanda suka kai shi can.
2 And the Lord was with Joseph, and he was a prosperous man; and he was thus in the house of his master the Egyptian.
Ubangiji kuwa yana tare da Yusuf, Yusuf kuwa yi nasara, ya zauna a gidan mutumin Masar maigidansa.
3 And when his master saw that the Lord was with him, and that the Lord caused all that he did to prosper in his hand:
Sa’ad da maigidansa ya ga cewa Ubangiji yana tare da Yusuf, kuma cewa Ubangiji ya ba shi nasara a kome da ya yi,
4 Joseph found grace in his eyes, and he served him; and he made him overseer over his house, and all that he had he put into his hand.
sai Yusuf ya sami tagomashi a idanunsa, ya kuma zama mai hidimarsa. Fotifar ya sa shi yă zama shugaba a gidansa, ya kuma danƙa masa kome da yake da shi.
5 And it came to pass from the time he had made him overseer in his house, and over all that he had, that the Lord blessed the Egyptian's house for the sake of Joseph; and the blessing of the Lord was upon all that he had, in the house and in the field.
Daga lokacin da ya sa shi shugaban gidansa da kuma a kan dukan abin da yake da shi, sai Ubangiji ya albarkaci gidan mutumin Masar saboda Yusuf. Albarkar Ubangiji tana a kan kome da Fotifar yake da shi a gida da kuma a jeji.
6 And he left all that he had in Joseph's hand; and he troubled himself not about aught he had, save the bread which he did eat. And Joseph was handsome in form and handsome in appearance.
Saboda haka sai ya bar kome a ƙarƙashin kulawar Yusuf, bai dame kansa a wani abu ba sai dai abincin da yake ci. To, fa, Yusuf ƙaƙƙarfa ne, kyakkyawa kuma,
7 And it came to pass after these things, that his master's wife cast her eyes upon Joseph; and she said, Lie with me.
bayan an ɗan jima sai matar maigidansa ta fara sha’awar Yusuf, sai ta ce, “Zo ka kwana da ni!”
8 But he refused, and said unto his master's wife, Behold, Thy master troubleth himself not about what is with me in the house, and he hath committed all that he hath into my hand;
Amma ya ƙi. Ya ce mata, “Ga shi kome yana a ƙarƙashina, don haka ne ma maigidana bai dami kansa da wani abu a cikin gidan nan ba; kome da ya mallaka, ya danƙa ga kulawata.
9 There is none greater in this house than I; neither hath he kept back any thing from me but thee, because thou art his wife: how then can I do this great evil, and sin against God?
Babu wani da ya fi ni a wannan gida. Maigidana bai hana ni kome ba sai ke, saboda ke matarsa ce. Yaya fa, zan yi irin wannan mugun abu, in yi zunubi wa Allah?”
10 And it came to pass, as she spoke to Joseph day by day, and he hearkened not unto her, to lie by her, or to be with her;
Ko da yake ta yi ta yin wa Yusuf maganar kowace rana, amma ya ƙi yă kwana da ita, ko ma yă zauna da ita.
11 That it came to pass one particular day, that he went into the house to do his business; and there was none of the men of the house there within.
Wata rana, ya shiga cikin gida don yă yi ayyukansa, ba wani daga cikin bayin gidan da yake ciki.
12 And she caught him by his garment, saying, Lie with me; and he left his garment in her hand, and fled, and ran out into the street.
Sai ta cafke shi a riga, ta ce, “Zo ka kwana da ni!” Amma ya bar rigarsa a hannunta, ya gudu ya fita daga gidan.
13 And it came to pass, when she saw that he had left his garment in her hand, and was fled forth,
Sa’ad da ta ga ya bar rigarsa a hannunta ya gudu ya fita daga gidan,
14 That she called unto the men of her house, and spoke unto them, saying, See, he hath brought in unto us a Hebrew man to have his sport with us; he came in unto me to lie with me, and I cried with a loud voice:
sai ta kira bayin gidan ta ce musu, “Duba, an kawo mana wannan mutumin Ibraniyawa don yă ci mutuncinmu! Ya zo nan don yă kwana da ni, amma na yi ihu.
15 And it came to pass, when he heard that I lifted up my voice and cried, that he left his garment with me, and fled, and ran out into the street.
Sa’ad da ya ji na yi ihu neman taimako, sai ya bar rigarsa kusa da ni, ya gudu ya fita daga gida.”
16 And she laid up his garment by her until his lord came home.
Ta ajiye rigar kusa da ita sai da maigidansa ya dawo gida.
17 And she spoke unto him according to these words, saying, The Hebrew servant whom thou hast brought unto us, came in unto me to have his sport with me.
Sa’an nan ta faɗa masa wannan labari, “Mutumin Ibraniyawan, bawan da ka kawo mana, ya zo wurina don yă ci mutuncina.
18 And it came to pass, as I lifted up my voice and cried, that he left his garment with me, and fled forth.
Amma da zarar na yi ihu neman taimako, sai ya bar rigarsa kusa da ni, ya gudu ya fita daga gida.”
19 And it came to pass, when his master heard the words of his wife, which she spoke unto him, saying, After this manner hath thy servant done to me; that his wrath was kindled.
Sa’ad da maigidansa ya ji labarin da matarsa ta faɗa masa cewa, “Ga yadda bawanka ya yi da ni,” sai ya husata.
20 And Joseph's master took him, and put him into the prison, the place where the king's prisoners were imprisoned: and he was there in the prison.
Maigidan Yusuf ya ɗauke shi ya sa a kurkuku, wurin da ake tsare’yan kurkukun sarki. Amma yayinda Yusuf yake can a cikin kurkuku,
21 But the Lord was with Joseph, and caused him to find kindness, and gave him favor in the eyes of the superintendent of the prison.
Ubangiji ya kasance tare da shi; ya nuna masa alheri, ya kuma sa ya sami tagomashi a idanun mai gadin kurkukun.
22 And the superintendent of the prison committed into Joseph's hand all the prisoners that were in the prison; and whatsoever they did there, was done through him.
Saboda haka mai gadin ya sa Yusuf ya zama shugaban dukan waɗanda aka tsare a kurkukun, Yusuf ne kuma yake lura da dukan abin da ake yi a can.
23 The superintendent of the prison looked not after the least that was under his hand, because the Lord was with him; and that which he did, the Lord made to prosper.
Mai gadin ba ya sa kansa game da kome da yake ƙarƙashin kulawar Yusuf, gama Ubangiji yana tare da Yusuf, ya kuma ba shi nasara a cikin dukan abin da ya yi.

< Genesis 39 >