< Genesis 26 >

1 And there was a famine in the land, beside the first famine that was in the days of Abraham; and Isaac went unto Abimelech, the king of the Philistines, unto Gerar.
Aka yi yunwa a ƙasar; ban da yunwar da aka yi da fari a zamanin Ibrahim, sai Ishaku ya tafi wurin Abimelek sarkin Filistiyawa a Gerar.
2 And the Lord appeared unto him, and said, Go not down into Egypt; dwell in the land which I shall tell thee of.
Ubangiji kuwa ya bayyana ga Ishaku ya ce, “Kada ka gangara zuwa Masar; ka yi zauna a ƙasar da zan faɗa maka.
3 Sojourn in this land, and I will be with thee, and will bless thee; for unto thee, and unto thy seed, will I give all these countries, and I will perform the oath which I swore unto Abraham thy father;
Ka zauna a wannan ƙasa na ɗan lokaci, zan kuwa kasance tare da kai, zan kuma albarkace ka. Gama zan ba da waɗannan ƙasashe gare ka da kuma zuriyarka. Zan kuma cika rantsuwar da na yi wa mahaifinka Ibrahim.
4 And I will cause thy seed to multiply as the stars of heaven, and I will give unto thy seed all these countries; and in thy seed shall all the nations of the earth bless themselves.
Zan sa zuriyarka ta yi yawa kamar taurari a sararin sama zan kuwa ba su dukan waɗannan ƙasashe, ta wurin’ya’yanka kuma za a albarkaci dukan al’umman duniya,
5 Because that Abraham obeyed my voice, and kept my charge, my commandments, my statutes, and my laws.
domin Ibrahim ya yi mini biyayya ya kuma kiyaye umarnaina, ƙa’idodina da kuma dokokina.”
6 And Isaac dwelt in Gerar.
Sai Ishaku ya zauna a Gerar.
7 And the men of the place asked [him] concerning his wife; and he said, She is my sister; for he feared to say, She is my wife; lest, [said he, ] the men of the place should kill me for Rebekah, because she is of a handsome appearance.
Sa’ad da mutanen wurin suka tambaye shi game da matarsa, sai ya ce, “’Yar’uwata ce,” gama yana tsoro yă ce, “Ita matata ce.” Ya yi tunani, “Mutane wannan wuri za su kashe ni ta dalili Rebeka, domin kyakkyawa ce.”
8 And it came to pass, when he had been there a long time, that Abimelech, the king of the Philistines, looked out at a window, and saw, and behold, Isaac was sporting with Rebekah his wife.
Sa’ad da Ishaku ya daɗe a can, sai Abimelek sarkin Filistiyawa ya duba daga taga ya ga Ishaku yana rungumar matarsa Rebeka.
9 And Abimelech called Isaac, and said, Behold, of a surety she is thy wife: and how saidst thou, She is my sister? And Isaac said unto him, Because I thought, Perhaps I may die for her.
Saboda haka Abimelek ya aika Ishaku yă je, sa’an nan ya ce, “Tabbatacce ita matarka ce! Me ya sa ka ce, ‘Ita’yar’uwata ce?’” Ishaku ya amsa masa ya ce, “Don na yi tsammani zan rasa raina saboda ita.”
10 And Abimelech said, What is this thou hast done unto us? How easily might one of the people have lain with thy wife, and thou wouldst have brought guiltiness upon us.
Sa’an nan Abimelek ya ce, “Me ke nan ka yi mana? Da a ce wani daga mazanmu ya kwana da matarka, ai, da ka jawo laifi a kanmu.”
11 And Abimelech charged all his people, saying, He that toucheth this man or his wife shall surely be put to death.
Saboda haka Abimelek ya yi umarni ga dukan mutane. “Duk wanda ya fitine wannan mutum ko matarsa, tabbatacce za a kashe shi.”
12 Then Isaac sowed in that land, and received in the same year a hundred-fold: so the Lord blessed him.
Ishaku ya shuka hatsi a wannan ƙasa, a shekaran nan ya yi girbi ninki ɗari, domin Ubangiji ya albarkace shi.
13 And the man became great, and went forward and grew, until he became very great;
Mutumin ya arzuta, arzikinsa ya yi ta haɓaka har ya zama attajiri.
14 And he had possession of flocks, and possession of herds, and great store of servants; and the Philistines envied him.
Ya kasance da garkunan tumaki da na shanu da bayi masu yawa, har Filistiyawa suka yi ƙyashinsa.
15 And all the wells which his father's servants had dug in the days of Abraham his father, these the Philistines stopped, and filled them with earth.
Saboda haka dukan rijiyoyin da bayin mahaifinsa suka haƙa a kwanakin da mahaifinsa Ibrahim yake da rai, Filistiyawa sun toshe su, suka kuma ciccike su da ƙasa.
16 And Abimelech said unto Isaac, Go away from us; for thou hast become much mightier than we.
Sai Abimelek ya ce wa Ishaku, “Fita daga cikinmu; ka fi ƙarfinmu.”
17 And Isaac departed thence, and pitched his tent in the valley of Gerar, and dwelt there.
Saboda haka Ishaku ya fita daga can, ya yi sansani a Kwarin Gerar, ya kuma zauna a can.
18 And Isaac dug again the wells of water, which they had dug in the days of Abraham his father, and which the Philistines had stopped after the death of Abraham; and he called their names after the names by which his father had called them.
Ishaku ya sāke tona rijiyoyi waɗanda dā aka haƙa a zamanin Ibrahim mahaifinsa, gama Filistiyawa suka tattoshe bayan mutuwar Ibrahim, ya kuma sa musu sunayen da mahaifinsa ya ba su.
19 And the servants of Isaac dug in the valley, and found there a well of springing water.
Barorin Ishaku suka haƙa cikin kwarin suka kuwa sami rijiya mai ruwa mai kyau a can.
20 And the herdmen of Gerar did strive with Isaac's herdmen, saying, The water is ours: and he called the name of the well Essek; because they strove with him.
Amma makiyayan Gerar suka yi faɗa da na Ishaku suka ce, “Ruwan namu ne!” Saboda haka Ishaku ya ba wa rijiyar suna Esek, domin sun yi faɗa da shi.
21 And they dug another well, and they strove for that also: and he called the name of it Sitnah.
Sai suka haƙa wata rijiya, amma suka yi faɗa a kanta ita ma, saboda haka ya ce da ita Sitna.
22 And he removed from there, and dug another well; and for that they strove not: and he called the name of it Rechoboth, and he said, For now the Lord hath made room for us, and we shall increase in the land.
Sai Ishaku ya matsa daga can ya sāke haƙa wata rijiyar, babu wani kuma da yi faɗa a kanta. Sai ya ba ta suna Rehobot, yana cewa, “Yanzu Ubangiji ya ba mu wuri, za mu kuwa yi ta haihuwa a ƙasar.”
23 And he went up from there to Beer-sheba.
Daga can ya haura zuwa Beyersheba.
24 And the Lord appeared unto him the same night, and said, I am the God of Abraham thy father; fear not, for I am with thee, and I will bless thee, and multiply thy seed for the sake of Abraham my servant.
A wannan dare Ubangiji ya bayyana gare shi ya ce, “Ni ne Allah na mahaifinka Ibrahim. Kada ka ji tsoro, gama ina tare da kai, zan albarkace ka, zan kuma ƙara yawan zuriyarka saboda bawana Ibrahim.”
25 And he built there an altar, and called upon the name of the Lord, and pitched there his tent: and the servants of Isaac dug there a well.
Sai Ishaku ya gina bagade a can, ya kuma kira bisa sunan Ubangiji. A can ya kafa tentinsa, a can kuma bayinsa suka haƙa wata rijiya.
26 Then Abimelech went to him from Gerar, and Achuzzath his friend, and Phichol the chief captain of his army.
Ana cikin haka, sai Abimelek ya zo wurinsa daga Gerar, tare da Ahuzzat mai ba shi shawara da Fikol shugaban mayaƙansa.
27 And Isaac said unto them, Wherefore come ye to me, seeing that ye do hate me, and have sent me away from you?
Ishaku ya tambaye su, “Me ya kawo ku gare ni, da yake kun yi gāba da ni, kuka kuma kore ni?”
28 And they said, We saw clearly that the Lord was with thee; and we said, Let there be now an oath between us and thee; and we will make a covenant with thee;
Suka amsa, “Mun ga a zahiri cewa Ubangiji yana tare da kai; saboda haka muka ce, ‘Dole rantsuwa ta kasance tsakaninmu da kai.’ Bari mu yi yarjejjeniya da kai
29 That thou shalt do us no hurt, as we have not touched thee, and as we have done unto thee nothing but good, and have sent thee away in peace: thou art now one blessed of the Lord.
cewa ba za ka cuce mu ba, kamar yadda ba mu fitine ka ba, amma muka yi maka kirki, muka kuma sallame ka cikin salama. Yanzu kuwa kai albarkatacce ne na Ubangiji.”
30 And he made them a feast, and they ate and drank.
Sai Ishaku ya shirya musu liyafa, suka ci suka kuma sha.
31 And they rose up betimes in the morning, and they swore one to the other; and Isaac sent them away, and they departed from him in peace.
Kashegari da sassafe sai mutanen suka yi wa juna rantsuwa. Sa’an nan Ishaku ya sallame su, suka kuwa tafi cikin salama.
32 And it came to pass the same day, that Isaac's servants came, and told him concerning the well which they had dug, and they said unto him, We have found water.
A wannan rana bayin Ishaku suka zo suka faɗa masa game da rijiyar da suka haƙa. Suka ce, “Mun sami ruwa!”
33 And he called it Shibah: therefore is the name of the city Beer-sheba unto this day.
Sai ya kira ta Shiba, don haka har wa yau ana kira garin Beyersheba.
34 And when Esau was forty years old he took to wife Judith the daughter of Beeri, the Hittite, and Bahsemath the daughter of Elon the Hittite.
Sa’ad da Yaƙub ya kai shekaru arba’in da haihuwa, sai ya auri Yudit’yar Beyeri mutumin Hitti, da kuma Basemat’yar Elon mutumin Hitti.
35 And they were a grief of mind unto Isaac and to Rebekah.
Su ne suka zama sanadin baƙin ciki ga Ishaku da Rebeka.

< Genesis 26 >