< Genesis 12 >
1 Now the Lord had said unto Abram, Get thee out of thy country, and out of thy birthplace, and from thy father's house, unto the land that I will show thee.
Ubangiji ya ce wa Abram, “Tashi ka bar ƙasarka, da mutanenka, da iyalin mahaifinka, ka tafi ƙasar da zan nuna maka.
2 And I will make of thee a great nation, and I will bless thee, and make thy name great; and thou shalt be a blessing:
“Zan mai da kai al’umma mai girma, zan kuma albarkace ka; zan sa sunanka yă zama mai girma, ka kuma zama sanadin albarka.
3 And I will bless those that bless thee, and him that curseth thee, will I curse; and in thee shall all families of the earth be blessed.
Zan albarkaci duk wanda ya albarkace ka, in kuma la’anci duk wanda ya la’anta ka, dukan mutanen duniya za su sami albarka ta wurinka.”
4 So Abram departed, as the Lord had spoken unto him, and Lot went with him; and Abram was seventy and five years old at his departure out of Charan.
Saboda haka Abram ya tashi yadda Ubangiji ya faɗa masa; Lot ma ya tafi tare da shi. Abram yana da shekaru 75, sa’ad da ya tashi daga Haran.
5 And Abram took Sarai his wife, and Lot his brother's son, and all their substance that they had acquired, and the persons that they had obtained in Charan; and they went forth to go into the land of Canaan; and they came into the land of Canaan.
Abram ya ɗauki matarsa Saira da Lot ɗan ɗan’uwansa, da dukan mallakar da suka tattara, da kuma mutanen da suka samu a Haran, suka kama hanya zuwa ƙasar Kan’ana.
6 And Abram passed through the land unto the place of Shechem, unto the plain of Moreh; and the Canaanite was then in the land.
Abram ya ratsa ƙasar har zuwa wurin babban itace na More a Shekem. A lokacin Kan’aniyawa suna a ƙasar.
7 And the Lord appeared unto Abram, and said, Unto thy seed will I give this land. And he built there an altar unto the Lord, who had appeared unto him.
Ubangiji ya bayyana ga Abram ya ce, “Ga zuriyarka ne zan ba da wannan ƙasa.” Saboda haka Abram ya gina bagade a can ga Ubangiji, wanda ya bayyana gare shi.
8 And he removed from there unto the mountain on the east of Beth-el, and pitched his tent, having Beth-el on the west, and 'Ai on the east; and he built there an altar unto the Lord, and called upon the name of the Lord.
Daga can, ya ci gaba zuwa wajen tuddai a gabashin Betel ya kafa tentinsa, Betel yana yamma, Ai, kuma a gabas. A can ya gina bagade ga Ubangiji ya kuma kira bisa sunan Ubangiji.
9 And Abram journeyed farther, still going on toward the south.
Sa’an nan Abram ya tashi ya ci gaba da tafiya zuwa wajen Negeb.
10 And there arose a famine in the land: and Abram went down into Egypt to sojourn there; for the famine was grievous in the land.
To, a lokacin, an yi yunwa a ƙasar, sai Abram ya gangara zuwa Masar don yă zauna a can na ɗan lokaci, domin yunwa ta yi tsanani.
11 And it came to pass, when he was come near to enter into Egypt, that he said unto Sarai his wife, Behold now, I know that thou art a woman of handsome appearance:
Yayinda yana gab da shiga Masar, sai ya ce wa matarsa Saira, “Na sani ke kyakkyawar mace ce.
12 And it may come to pass, when the Egyptians shall see thee, that they will say, This is his wife; and they may kill me, but thee they will save alive.
Sa’ad da Masarawa suka ganki, za su ce, ‘Wannan matarsa ce.’ Za su kuwa kashe ni, su bar ki da rai.
13 Say then, I pray thee, thou art my sister, that it may go well with me for thy sake, and my soul live because of thee.
Saboda haka ki ce ke’yar’uwata ce, domin ta dalilinki a mutunta ni, a kuma bar ni da rai.”
14 And it came to pass, when Abram was come into Egypt, that the Egyptians beheld the woman that she was very fair.
Sa’ad da Abram ya isa Masar, Masarawa suka ga cewa Saira kyakkyawa mace ce ƙwarai.
15 The princes also of Pharaoh saw her, and commended her to Pharaoh; and the woman was taken into Pharaoh's house.
Sa’ad da fadawan Fir’auna suka gan ta kuwa, sai suka yabe ta wajen Fir’auna, aka kuwa kawo ta cikin fadarsa.
16 And he did well to Abram for her sake; and he received sheep, and oxen, and he-asses, and men-servants, and maid-servants, and she-asses, and camels.
Ya mutunta Abram sosai saboda ita, Abram kuwa ya mallaki tumaki da shanu, da jakuna maza da mata, da bayi maza da mata, da kuma raƙuma.
17 But the Lord plagued Pharaoh and his house with great plagues because of Sarai, Abram's wife.
Amma Ubangiji ya wahalar da Fir’auna da gidansa da cututtuka masu zafi saboda Saira, matar Abram.
18 And Pharaoh called Abram, and said, What is this thou hast done unto me? Why didst thou not tell me that she is thy wife?
Saboda haka Fir’auna ya kira Abram ya ce, “Me ke nan ka yi mini? Me ya sa ba ka faɗa mini cewa ita matarka ce ba?
19 Why saidst thou, She is my sister? and so I took her to me for a wife; now, therefore, behold, here is thy wife, take her, and go thy way.
Don me ka ruɗe ni cewa, ‘Ita’yar’uwata ce,’ har na ɗauke ta tă zama matata? To, ga matarka. Ɗauke ta ka tafi.”
20 And Pharaoh commanded some men concerning him, who accompanied him and his wife, and all that he had.
Sa’an nan Fir’auna ya yi wa mutanensa umarni a kan Abram, suka kuwa sallame shi tare da matarsa da kuma dukan abin da yake da shi.