+ Genesis 1 >

1 In the beginning God created the heaven and the earth.
A farko-farko, Allah ya halicci sama da ƙasa.
2 And the earth was without form and void, and darkness was upon the face of the deep; and the spirit of God was waving over the face of the waters.
To, ƙasa dai ba ta da siffa, babu kuma kome a cikinta, duhu ne kawai ya rufe ko’ina, Ruhun Allah kuwa yana yawo a kan ruwan.
3 And God said, Let there be light; and there was light.
Sai Allah ya ce, “Bari haske yă kasance,” sai kuwa ga haske.
4 And God saw the light that it was good; and God divided between the light and the darkness.
Allah ya ga hasken yana da kyau, sai ya raba tsakanin hasken da duhu.
5 And God called the light Day, and the darkness he called Night. And it was evening and it was morning, the first day.
Allah ya kira hasken “yini,” ya kuma kira duhun “dare.” Yamma ta kasance, safiya kuma ta kasance, kwana ta fari ke nan.
6 And God said, Let there be an expansion in the midst of the waters, and let it divide between waters and waters.
Allah ya ce, “Bari sarari yă kasance tsakanin ruwaye domin yă raba ruwa da ruwa.”
7 And God made the expansion, and divided between the waters which were under the expansion and the waters which were above the expansion: and it was so.
Saboda haka Allah ya yi sarari ya raba ruwan da yake ƙarƙashin sararin da ruwan da yake bisansa. Haka kuwa ya kasance.
8 And God called the expansion Heaven. And it was evening and it was morning, the second day.
Allah ya kira sararin “sama.” Yamma ta kasance, safiya kuma ta kasance, kwana ta biyu ke nan.
9 And God said, Let the waters under the heaven be gathered together unto one place, and let the dry land be visible: and it was so.
Allah ya ce, “Bari ruwan da yake ƙarƙashin sama yă tattaru wuri ɗaya, bari kuma busasshiyar ƙasa tă bayyana.” Haka kuwa ya kasance.
10 And God called the dry land Earth; and the gathering together of the waters he called Seas: and God saw that it was good.
Allah ya kira busasshiyar ƙasar “doron ƙasa,” ruwan da ya taru kuma, ya kira “tekuna.” Allah ya ga yana da kyau.
11 And God said, Let the earth bring forth grass, herbs yielding seed, fruit-trees yielding fruit after their kind, in which its seed is upon the earth: and it was so.
Sa’an nan Allah ya ce, “Bari ƙasa tă fid da tsire-tsire, da shuke-shuke, da itatuwa a bisa ƙasa masu ba da amfani da’ya’ya a cikinsu, bisa ga irinsu.” Haka kuwa ya kasance.
12 And the earth brought forth grass, herbs yielding seed after their kind, and trees yielding fruit, in which its seed is after their kind: and God saw that it was good.
Ƙasar ta fid da tsire-tsire, da shuke-shuke masu ba da’ya’ya bisa ga irinsu, ta fid kuma da itatuwa masu ba da’ya’ya da iri a cikinsu bisa ga irinsu. Allah ya ga yana da kyau.
13 And it was evening and it was morning, the third day.
Yamma ta kasance, safiya kuma ta kasance, kwana ta uku ke nan.
14 And God said, Let there be lights in the expansion of the heaven to divide between the day and the night; and let them be for signs, and for seasons, and for days, and years;
Allah kuma ya ce, “Bari haskoki su kasance a sararin sama domin su raba yini da dare, bari su zama alamu domin su nuna yanayi, da ranaku, da kuma shekaru,
15 And let them be for lights in the expansion of the heaven, to give light upon the earth: and it was so.
bari kuma haskokin su kasance a sararin sama domin su ba da haske a duniya.” Haka kuwa ya kasance.
16 And God made the two great lights; the greater light to rule the day, and the lesser light to rule the night; and the stars.
Allah ya yi manyan haskoki biyu, babban hasken yă mallaki yini, ƙaramin kuma yă mallaki dare. Ya kuma yi taurari.
17 And God set them in the expansion of the heaven to give light upon the earth,
Allah ya sa su a sararin sama domin su ba da haske a duniya,
18 And to rule by day and by night, and to divide between the light and the darkness: and God saw that it was good.
su mallaki yini da kuma dare, su kuma raba haske da duhu. Allah kuwa ya ga yana da kyau.
19 And it was evening and it was morning, the fourth day.
Yamma ta kasance, safiya kuma ta kasance, kwana ta huɗu ke nan.
20 And God said, Let the waters bring forth abundantly moving creatures that have life, and fowl that may fly above the earth in the open expansion of the heaven.
Allah ya ce, “Bari ruwa yă cika da halittu masu rai, bari tsuntsaye kuma su tashi sama a bisa duniya a sararin sama.”
21 And God created the great sea-monsters, and every living creature that moveth, which the waters brought forth abundantly after their kind, and every winged fowl after its kind: and God saw that it was good.
Allah ya halicci manyan halittun teku, da kowane mai rai da abin da yake motsi a ruwa, bisa ga irinsu, da kuma kowane tsuntsu mai fiffike bisa ga irinsa. Allah kuwa ya ga yana da kyau.
22 And God blessed them, saying, Be fruitful and multiply, and fill the waters in the seas, and let the fowl multiply on the earth.
Allah ya albarkace su ya ce, “Ku yi ta haihuwa ku kuma ƙaru da yawa, ku cika ruwan tekuna, bari kuma tsuntsaye su yi yawa a bisa duniya.”
23 And it was evening and it was morning, the fifth day.
Yamma ta kasance, safiya kuma ta kasance, kwana ta biyar ke nan.
24 And God said, Let the earth bring forth living creatures after their kind, cattle, and creeping things, and beasts of the earth after their kind: and it was so.
Allah kuwa ya ce, “Bari ƙasa tă ba da halittu masu rai bisa ga irinsu; dabbobi da halittu masu rarrafe, da kuma namun jeji, kowane bisa ga irinsa.” Haka kuwa ya kasance.
25 And God made the beasts of the earth after their kind, and the cattle after their kind, and every thing that creepeth upon the earth after its kind: and God saw that it was good.
Allah ya halicci namun jeji bisa ga irinsu, dabbobi bisa ga irinsu, da kuma dukan halittu masu rarrafe a ƙasa bisa ga irinsu. Allah kuwa ya ga yana da kyau.
26 And God said, Let us make man in our image, after our likeness; and they shall have dominion over the fish of the sea, and over the fowl of the heaven, and over the cattle, and over all the earth, and over every creeping thing that creepeth upon the earth.
Sa’an nan Allah ya ce, “Bari mu yi mutum cikin siffarmu, cikin kamanninmu, bari kuma su yi mulki a bisa kifin teku, tsuntsayen sama, da kuma dabbobi, su yi mulki a bisa dukan duniya, da kuma a bisa dukan halittu, da masu rarrafe a ƙasa.”
27 And God created man in his image, in the image of God created he him; male and female created he them.
Saboda haka Allah ya halicci mutum cikin siffarsa. Cikin kamannin Allah, Allah ya halicci mutum. Miji da mace ya halicce su.
28 And God blessed them, and God said unto them, Be fruitful and multiply, and fill the earth, and subdue it; and have dominion over the fish of the sea, and over the fowl of the heaven, and over every living thing that moveth upon the earth.
Allah ya albarkace su, ya kuma ce musu, “Ku yi ta haihuwa ku ƙaru da yawa, ku mamaye duniya, ku mallake ta. Ku yi mulki a bisa kifin teku, da tsuntsayen sararin sama, da kuma bisa kowace halitta mai rai wadda take rarrafe a ƙasa.”
29 And God said, Behold I have given unto you every herb bearing seed, which is upon the face of all the earth, and every tree on which is the fruit of a tree yielding seed; to you it shall be for food.
Sa’an nan Allah ya ce, “Ga shi, na ba ku kowane tsiro mai ba da’ya’ya masu kwaya da suke a fāɗin duniya, da dukan itatuwa masu ba da’ya’ya, don su zama abinci a gare ku.
30 And to every beast of the earth, and to every fowl of the heaven, and to every thing that creepeth upon the earth, wherein there is life, [I have given] every green herb for food: and it was so.
Na kuma ba da dukan dabbobin ƙasa, da dukan tsuntsayen sama, da dukan abin da yake rarrafe a ƙasa, da dai iyakar abin da yake numfashi; haka kuma na ba da ganyaye su zama abinci.” Haka kuwa ya kasance.
31 And God saw every thing that he had made, and behold, it was very good. And it was evening and it was morning, the sixth day.
Allah ya ga dukan abin da ya yi, yana da kyau ƙwarai. Yamma ta kasance, safiya kuma ta kasance, kwana ta shida ke nan.

+ Genesis 1 >