< Ezra 8 >
1 Now these are the chiefs of their divisions, and this is the genealogy of those that went up with me, in the reign of king Artaxerxes, from Babylon.
Waɗannan su ne shugabannin iyalai, da kuma waɗanda suka dawo tare da ni daga Babilon a zamanin mulkin Sarki Artazerzes.
2 Of these sons of Phinehas, Gershom; of the sons of Ithamar, Daniel; of the sons of David, Chattush;
Daga zuriyar Finehas, Gershom ne shugaba; daga zuriyar Itamar, Daniyel ne shugaba; daga zuriyar Dawuda, Hattush
3 Of the sons of Shechanyah, [who was] of the sons of Par'osh, Zechariah; and with him were recorded by genealogy of males one hundred and fifty.
ɗan zuriyar Shekaniya ne shugaba, daga zuriyar Farosh, Zakariya ne shugaba, tare da shi akwai mutum 150;
4 Of the sons of Pachath-moab, Elyeho'enai the son of Zerachyah, and with him were two hundred males.
daga Fahat-Mowab, Eliyehoyenai ɗan Zerahiya ne shugaba, tare da shi akwai mutum 200;
5 Of the sons of Shechanyah, the son of Yachaziel, and with him were three hundred males.
daga zuriyar Zattu, Shekaniya ɗan Yahaziyel ne shugaba, tare da shi akwai mutum 300;
6 And of the sons of 'Adin, 'Ebed the son of Jonathan, and with him were fifty males.
daga zuriyar Adin, Ebed ɗan Yonatan ne shugaba, tare da shi akwai mutum 50;
7 And of the sons of 'Elam, Jesha'yah the son of 'Athalyah, and with him were seventy males.
daga zuriyar Elam, Yeshahiya ɗan Ataliya ne shugaba, tare da shi akwai mutum 70;
8 And of the sons of Shephatyath, Zebadyah the son of Michael, and with him were eighty males.
daga zuriyar Shefatiya, Zebadiya ɗan Mika’ilu ne shugaba, tare da shi akwai mutum 80;
9 Of the sons of Joab, 'Obadiah the son of Jechiel, and with him were two hundred and eighteen males.
daga iyalin Yowab, Obadiya ɗan Yehiyel ne shugaba, tare da shi akwai mutum 218;
10 And of the sons of Shelomith, the son of Jossiphyah, and with him were one hundred and sixty males.
daga Bani, Shelomit ɗan Yosifiya ne shugaba, tare da shi akwai mutum 160;
11 And of the sons of Bebai, Zechariah the son of Bebai, and with him were twenty and eight males.
daga Bebai, Zakariya ɗan Bebai ne shugaba, tare da shi akwai mutum 28;
12 And the sons of 'Azgad, Jochanan the son of Hakkatan, and with him were one hundred and ten males.
daga iyalin Azgad, Yohanan ɗan Hakkatan ne shugaba, tare da shi akwai mutum 110;
13 And of the sons of Adonikam the last; and those are their names, Eliphelet, Je'iel, and Shema'yah, and with them were sixty males.
zuriya ta Adonikam ne suka zo daga ƙarshe, sunayensu kuwa su ne Elifelet, Yehiyel da Shemahiya, tare da su akwai mutum 60;
14 And of the sons of Bigvai, 'Uthai, and Zabbur, and with them were seventy males.
daga zuriyar Bigwai, Uttai da Zakkur ne shugabanni, tare da su akwai mutum 70.
15 And I gathered them together to the river that runneth into the Ahava, and we encamped there three days: and I looked about among the people, and the priests, but of the sons of Levi I found none there.
Na kuma tattara su a bakin rafi wanda yake gangarawa zuwa Ahawa, muka kafa sansani a can kwana uku. Da na bincika cikin mutane da firistoci, sai na tarar babu Lawiyawa.
16 Then sent I for Eli'ezer, for Ariel, for Shema'yah, and for Elnathan, and for Jarib, and for Elnathan, and for Nathan, and for Zechariah, and for Meshullam, the head men; also for Joyarib, and for Elnathan, men of understanding.
Saboda haka sai na aika a kira Eliyezer, da Ariyel, da Shemahiya, da Elnatan, da Yarib, da Natan, da Zakariya, da Meshullam waɗanda su ne shugabanni. Na kuma sa a kira Yohiyarib da Elnatan waɗanda masana ne.
17 And I sent them with a charge unto Iddo the chief at the place Cassiphia, and I laid the words in their mouth to speak unto Iddo, and to his brother, who were appointed at the place Cassiphia, that they should bring unto us ministers for the house of our God.
Na sa su je wurin Iddo wanda yake shugaba a Kasifiya. Aka gaya musu abin da za su gaya wa Iddo da’yan’uwansa masu aiki a haikali a Kasifiya don su aiko mana waɗanda za su yi mana hidima a haikalin Allahnmu.
18 And they brought unto us according to the good hand of our God upon us a man of intelligence, of the sons of Machli, the son of Levi, the son of Israel, namely, Sherebyah, with his sons and his brothers, eighteen;
Da yake Allah yana tare da mu, sai suka aiko mana da Sherebiya, wanda ya iya aiki, shi daga zuriyar Mali ɗan Lawi ne, ɗan Isra’ila. Sai ya zo tare da’ya’yansa da kuma’yan’uwansa. Dukansu dai mutum 18 ne.
19 And Chashabyah, and with him Jesha'yah of the sons of Merari, his brothers and their sons, twenty.
Suka kuma aika da Hashabiya tare da Yeshahiya daga zuriyar Merari, da’yan’uwansu da kuma’ya’yansu, su kuma mutum 20 ne.
20 Also of the temple-servants, whom David and the princes had assigned for the service of the Levites two hundred and twenty temple-servants, all of whom were expressed by names.
Sun kuma kawo masu aiki a haikali mutum 220, ƙungiyar da Dawuda da abokan aikinsa suka keɓe don su taimaki Lawiyawa aiki. Duk aka rubuta waɗannan da sunayensu.
21 Then did I proclaim a fast there, at the river Ahava, that we might afflict ourselves before our God, to request from him a prosperous journey for us, and for our little ones, and for all our substance.
A can, a bakin rafin Ahawa, na sa mu yi azumi, domin mu ƙasƙantar da kanmu a gaban Allah, mu kuma roƙe shi yă kiyaye mana hanya, da mu da’ya’yanmu da kayanmu duka.
22 For I was ashamed to ask of the king an army and horsemen to assist us against an enemy on the way; because we had spoken unto the king, saying, The hand of our God is upon all those that seek him for good; but his power and his wrath are against all those that forsake him.
Na ji kunya in roƙi sarki yă haɗa mu da sojoji da masu dawakai don su yi mana rakiya su kāre mu daga magabta a kan hanya, gama mun ce wa sarki, “Alherin Allah yana tare da duk wanda yake dogara gare shi, amma kuma fushinsa yana kan duk wanda ya juya masa baya.”
23 So we fasted and besought our God for this, and he suffered himself to be entreated by us.
Saboda haka sai muka yi azumi, muka kai roƙonmu a wurin Allah, ya kuwa amsa mana.
24 Then set I apart of the chiefs of the priests twelve persons, Sherebyah, Chashabyah, and with them ten of their brethren.
Sai na keɓe manyan firistoci guda goma sha biyu tare da Sherebiya, Hashabiya da kuma’yan’uwansu guda goma.
25 And I weighed out unto them the silver, and the gold, and the vessels, the offering for the house of our God, which the king, and his counsellors, and his princes, and all Israel there present, had offered.
Na auna musu zinariya da azurfa, da kwanoni waɗanda sarki da mashawartansa, da sauran abokan aikinsa, da Isra’ilawan da suke can suka bayar domin haikalin Allahnmu.
26 And I weighed out into their hand of silver six hundred and fifty talents, and of silver vessels one hundred talents, of gold one hundred talents;
Na auna musu talenti 650 na azurfa, talenti ɗari na kwanonin azurfa, talenti 100 na zinariya,
27 Also twenty cups of gold, of a thousand drachms; and two vessels of fine polished copper, valuable as gold.
kwanonin zinariya guda 20 da darajarsu ya kai darik 1,000, da kwanoni biyu na gogaggen tagulla, wanda yake darajarsa daidai da zinariya.
28 And I said unto them, Ye are holy unto the Lord; and the vessels are holy; and the silver and the gold are a freewill offering unto the Lord the God of your fathers.
Na ce masa, “Ku da kayan nan tsarkaka ne ga Ubangiji. Azurfa da zinariya ɗin, bayarwa ce ta yardar rai ga Ubangiji, Allah na kakanninku.
29 Watch ye, and guard them, until ye weigh them out before the chiefs of the priests and the Levites, and the chiefs of the divisions of Israel, at Jerusalem, into the chambers of the house of the Lord.
Ku lura da su da kyau har sai kun isa Urushalima. Ku auna su a shirayin haikalin Ubangiji a Urushalima, a gaban manyan firistoci, da Lawiyawa, da shugabannin iyalai na Isra’ila.”
30 And the priests and the Levites accepted what was weighed out of the silver, and the gold, and the vessels, to bring the same to Jerusalem to the house of our God.
Sa’an nan sai firistoci, da Lawiyawa suka karɓi azurfa da zinariya da kuma tsarkakan kwanonin da aka auna don a kai haikalin Allahnmu a Urushalima.
31 And we departed from the river Ahava on the twelfth day of the first month, to go unto Jerusalem: and the hand of our God was over us, and he delivered us from the hand of any enemy, and of such as lie in wait on the way.
A rana ta goma sha biyu ga watan farko, muka tashi daga bakin rafin Ahawa don mu tafi Urushalima. Alherin Allahnmu yana tare da mu, ya kuma kāre mu daga magabta da’yan fashi.
32 And we came to Jerusalem, and remained there three days.
Muka iso Urushalima, inda muka huta kwana uku.
33 And on the fourth day were the silver and the gold and the vessels weighed out in the house of our God into the hand of Meremoth the son of Uriyah the priest; and with him was El'azar the son of Phinehas; and with them was Jozabad the son of Jeshua', and No'adyah the son of Binnui, the Levites;
A rana ta huɗu muka tafi haikalin Allah, muka auna azurfa, da zinariya, da tsarkakan kwanonin, muka ba Meremot ɗan Uriya firist, da Eleyazar ɗan Finehas yana tare da shi, da kuma Lawiyawan nan, wato, Yozabad ɗan Yeshuwa, da Nowadiya ɗan Binnuyi.
34 By number and by weight of everything: and all the weight was written down at the same time.
Aka yi lissafi aka auna kome aka tarar yana nan daidai, aka kuma rubuta yawan nauyin a lokacin.
35 Those that came out of the captivity, the children of the exile, offered burnt-offerings unto the God of Israel, twelve bullocks for all Israel, ninety and six rams, seventy and seven sheep, twelve he-goats for a sin-offering: all as burnt-offerings unto the Lord.
Sa’an nan sai waɗanda suka dawo daga bauta suka miƙa hadaya ta ƙonawa ga Allah na Isra’ila. Wato, bijimai guda goma sha biyu don Isra’ilawa duka, raguna tasa’in da shida,’yan raguna saba’in da bakwai, bunsurai kuma guda goma sha biyu. Aka miƙa su hadaya don zunubi. Wannan duka hadaya ta ƙonawa ce ga Ubangiji.
36 And they delivered the king's commands unto the king's lieutenants, and to the governors on this side of the river; and these endowed the people, and the house of God.
Suka kuma kai saƙon sarki zuwa ga wakilansa, da kuma gwamnoni na Kewayen Kogin Yuferites waɗanda suka taimaki mutane da kuma gidan Allah.