< Ezekiel 9 >
1 And he called before my ears with a loud voice, saying, Let those come near that have charge to punish the city, and every man with his destroying weapon in his hand.
Sai na ji ya yi kira da babbar murya yana cewa, “Kawo matsaran birni a nan, kowanne da makami a hannunsa.”
2 And, behold, six men came from the direction of the upper gate, which is turned toward the north, and every man with his weapon of destruction in his hand; and one man in the midst of them was clothed in linen, with a writer's materials by his side: and they went in, and placed themselves beside the copper altar.
Na kuma ga mutane shida suna zuwa daga kowane gefen ƙofar ta bisa, wadda take fuskantar arewa, kowanne da makamin kisa a hannunsa. Tare da su akwai mutum saye da lilin yana rataye da jaka ƙunshe da kayan rubutu a gefensa. Suka shiga suka tsaya kusa da bagaden tagulla.
3 And the glory of the God of Israel ascended up from the cherub, whereupon it had been, to the threshold of the house. And he called to the man clothed in linen, who had the writer's materials by his side.
To, fa, ɗaukakar Allah na Isra’ila ta haura daga bisa kerubobi, inda ta kasance, ta tashi zuwa bakin madogarar ƙofar haikali. Sai Ubangiji ya kira mutumin da yake saye da lilin wanda ya rataye jaka ƙunshe da kayan rubutu a gefensa
4 And the Lord said unto him, Pass through the midst of the city, through the midst of Jerusalem, and inscribe a mark upon the foreheads of the men who sigh and who complain because of all the abominations which are done in the midst of it.
ya ce masa, “Ka ratsa birnin Urushalima ka sa shaida a goshin waɗanda suke baƙin ciki da kuma makoki a kan dukan abubuwan banƙyamar da ake yi a cikinsa.”
5 And to the others he said before my ears, Pass ye through the city after him, and smite: let your eye not look with pity, and do not spare;
Yayinda nake saurara, sai ya ce wa waɗansu, “Ku bi shi ta birnin ku kuma kashe, babu tausayi ko kuwa jinƙai.
6 The aged, youth, and virgin, and little children, and women shall ye slay and destroy; but come not near any man upon whom the mark is; and at my sanctuary shall ye begin. Then they began with the ancient men who were before the house.
Ku kashe tsofaffi da samari da’yan mata, mata da yara, amma kada ku taɓa wani wanda yake da shaida. Ku fara a wuri mai tsarkina.” Saboda haka suka fara da dattawan da suke gaban haikali.
7 And he said unto them, Make unclean the house, and fill the courts with the slain: go forth. And they went forth, and they smote in the city.
Sa’an nan ya ce musu, “Ku ƙazantar da haikalin ku kuma cika filayen da kisassu. Ku tafi!” Saboda haka suka fita suka kuma fara kisa a duk birnin.
8 And it came to pass, while they were smiting them, and I alone was left, that I fell upon my face, and cried out, and said, Ah Lord Eternal! wilt thou destroy all the residue of Israel when thou pourest out thy fury over Jerusalem?
Yayinda suke kisan sai aka bar ni kaɗai, na fāɗi rubda ciki, na yi kuka na ce, “Kash, Ubangiji Mai Iko Duka! Za ka hallaka dukan raguwar Isra’ila a wannan zafin fushinka a Urushalima?”
9 Then said he unto me, The iniquity of the house of Israel and of Judah is exceedingly great, and the land is full of blood-guiltiness, and the city full of injustice; for they have said, The Lord hath forsaken the land, and the Lord seeth not.
Ya amsa mini ya ce, “Zunubin gidan Isra’ila da Yahuda ya yi girma ainun; ƙasar ta cika da rashin adalci. Suna cewa, ‘Ubangiji ya yashe ƙasar; Ubangiji ba ya gani.’
10 And as for me also, my eye shall not look with pity, and I will not spare; but I will bring their course upon their own head.
Saboda haka ba zan dube su da tausayi ko kuwa in ƙyale su ba, amma zan kawo wa kansu abin da suka yi.”
11 And, behold, the man clothed in linen, who had the writing materials by his side, brought back word, saying, I have done according to all that thou hast commanded me.
Sai mutumin da yana saye da lilin yake kuma rataye da jaka ƙunshe da kayan rubutu a gefensa ya mayar da magana, yana cewa, “Na yi yadda ka umarci ni.”