< Ezekiel 8 >

1 And it came to pass in the sixth year, in the sixth month, on the fifth day of the month, that I was sitting in my house, and the elders of Judah were sitting before me; and there fell upon me there the inspiration of the Lord Eternal.
A shekara ta shida, a wata shida a ranar ta biya, yayinda nake zaune a gidana dattawan Yahuda kuma suna zaune a gabana, hannun Ubangiji Mai Iko Duka ya zo a kaina a can.
2 And I saw, and, behold, there was a likeness similar to the appearance of fire; from the appearance of his loins downward, it was fire; and from his loins upward, it was similar to the appearance of a bright light, like the glitter of amber.
Na duba, sai na ga siffa kamar na mutum. Daga kwankwaso zuwa ƙasa ya yi kamar wuta, kuma daga kwankwaso zuwa sama kamanninsa ya yi haske yana ƙyalli kamar ƙarfe mai haske.
3 And he stretched forth the form of a hand, and took me by the locks of my head; and a spirit bore me between the earth and the heaven, and brought me in the visions of God to Jerusalem, to the door of the inner gate that looketh toward the north, where was the seat of the image of jealousy, which provoketh to wrath.
Ya miƙa abin da ya yi kamar hannu ya kama a gashin kaina. Ruhu ya ɗaga ni tsakanin sama da ƙasa, a cikin wahayoyi kuma Allah ya ɗauke ni zuwa Urushalima, zuwa ƙofa zuwa gabas na cikin fili, inda gunki mai tsokanar kishi yake tsaye.
4 And, behold, there was the glory of the God of Israel, like the appearance which I had seen in the valley.
A can gabana kuwa ga ɗaukakar Allah na Isra’ila, kamar a wahayin da na gani a fili.
5 And he said unto me, Son of man, do but lift up thy eyes in the direction toward the north. So I lifted up my eyes in the direction toward the north, and behold northward at the gate of the altar [there was] this image of jealousy at the entrance.
Sai ya ce mini, “Ɗan mutum, duba waje arewa.” Sai na duba, a mashigin arewa na ƙofar bagaden kuwa na ga wannan gunki na tsokanar kishi.
6 Then said he unto me, Son of man, seest thou what they are doing? great abominations are they that the house of Israel commit here, to make me go far away from my sanctuary; but thou shalt yet see still other great abominations.
Ya kuma ce mini, “Ɗan mutum, ka ga abin da suke yi, abubuwan banƙyamar da gidan Isra’ila ke yi a nan, abubuwan da za su kore ni daga wuri mai tsarkina? Amma za ka ga abubuwan da suka ma fi banƙyama.”
7 And he brought me to the door of the court: and I looked, and behold there was a hole in the wall.
Sa’an nan ya kawo ni mashigin filin. Na duba, na kuma ga rami a bango.
8 Then said he unto me, Son of man, do break [an opening] in the wall: and I broke [an opening] in the wall, and, behold, there was a door.
Ya ce mini, “Ɗan mutum, yanzu ka haƙa cikin bangon.” Da na haƙa cikin bangon sai na ga ƙofar shiga a can.
9 And he said unto me, Go in, and see the wicked abominations which they are doing here.
Sai ya ce mini, “Shiga ka ga mugaye da kuma abubuwa banƙyamar da suke yi a can.”
10 So I went in and saw; and behold there was every form of creeping things, and cattle, abominations, and all the idols of the house of Israel, engraven upon the wall all round about.
Na kuwa shiga na duba, sai na ga zāne-zāne ko’ina a bangon na kowane irin abubuwa masu rarrafe da kuma dabbobi masu ƙazanta da dukan gumakan gidan Isra’ila.
11 And seventy men of the elders of the house of Israel, and Yaazanyahu the son of Shaphan standing in the midst of them, were standing before them, and every man had his censer in his hand; and a thick curling cloud of incense was ascending upward.
A gabansu ga dattawa saba’in na gidan Isra’ila tsaye a cikinsu, Ya’azaniya ɗan Shafan kuwa yana tsaye a cikinsu. Kowa yana da farantin ƙona turare a hannunsa, tulin hayaƙin turare mai ƙanshi ya tunnuƙe zuwa sama.
12 Then said he unto me, Son of man, hast thou seen what the elders of the house of Israel are doing in the dark, every man in his image-chambers? for they say, The Lord seeth us not: the Lord hath forsaken the earth.
Ya ce mini, “Ɗan mutum, ka ga abin da dattawan gidan Isra’ila suke yi a cikin duhu, kowa yana a ɗakin tsafin gunkinsa? Suna cewa, ‘Ubangiji ba ya ganinmu; Ubangiji ya yashe ƙasar.’”
13 And he said unto me, Thou shalt yet again see still other great abominations that they are doing.
Ya kuma ce, “Za ka gan su suna yin abubuwan da suka fi waɗannan banƙyama.”
14 And he brought me to the entrance of the gate of the Lord's house which was on the north side: and, behold, there sat the women weeping for Thammuz.
Sa’an nan ya kawo ni mashigin arewa na ƙofar gidan Ubangiji, sai na ga mata zaune a can, suna makokin Tammuz.
15 Then said he unto me, Hast thou seen this, O son of man? Thou shalt yet again see still other greater abominations than these.
Ya ce mini, “Ɗan mutum, ka ga wannan? Za ka ga abubuwan da suke masu banƙyama fiye da wannan.”
16 And he brought me into the inner court of the Lord's house, and, behold, at the door of the temple of the Lord, between the porch and the altar, were about five and twenty men, with their backs toward the temple of the Lord, and their faces toward the east; and they were prostrating themselves eastward to the sun.
Sa’an nan ya kawo ni cikin fili na cikin gidan Ubangiji, a can kuwa a ƙofar haikali, tsakanin shirayi da bagade, akwai kamar mutum ashirin da biyar. Suka ba haikalin Ubangiji baya suna fuskanta wajen gabas, suna rusuna wa rana a gabas.
17 Then said he unto me, Hast thou seen this, O son of man? Is it too light a thing for the house of Judah to commit the abominations which they commit here? for they have filled the land with violence, and they constantly repeat to provoke me to anger; and, lo, they stretch forth the branch to their nose.
Ya ce mini, “Ka ga wannan, ɗan mutum? Ƙaramin abu ne gidan Yahuda su yi abubuwan banƙyamar da suke yi a nan? Dole ne su cika ƙasar da rikici su kuma ci gaba da tsokane ni in yi fushi? Dube su suna tsokanata!
18 Therefore I also will deal in fury; my eye shall not look with pity, and I will not spare: and though they call before my ears with a loud voice, will I still not hear them.
Saboda haka zan hukunta su cikin fushi; Ba zan dube su da tausayi ko kuwa in ƙyale su ba. Ko da yake suna ihu a kunnuwana, ba zan saurare su ba.”

< Ezekiel 8 >