< Ezekiel 47 >
1 And he brought me back again unto the door of the house: and, behold, water was issuing out from under the threshold of the house eastward; for the front of the house stood toward the east; and the water came down from under [the threshold], from the right side of the house, to the south of the altar.
Mutumin ya komo da ni zuwa mashigin haikalin, sai na kuwa ga ruwa yana malalowa daga ƙarƙashin madogarar ƙofar haikalin wajen gabas (gama haikalin yana fuskantar gabas). Ruwan yana malalowa daga ƙarƙashin gefen kudun haikalin, kudu da bagaden.
2 Then did he bring me out by the way of the gate northwards and led me about the way without unto the outer gate by the way that looked eastward: and, behold, the water was running on the right side.
Sai ya fitar da ni ta ƙofar arewa ya kewaye da ni ta waje zuwa ƙofar da take waje mai fuskantar gabas, ruwan kuwa yana malalowa daga wajen kudu.
3 When the man went forth eastward, having the measuring-line in his hand, he measured a thousand cubits, and he led me through the water, the water reaching to the ankles.
Yayinda mutumin ya yi wajen gabas da karan awo a hannunsa, sai ya auna kamu dubu ya kuma bi da ni ta ruwan da zurfinsa ya kama ni a idon ƙafa.
4 Again he measured a thousand [cubits], and led me through the water, the water reaching to the knees. Again he measured a thousand [cubits], and led me through, the water reaching to the loins.
Ya auna wani kamu dubu ya kuma bi da ni a ruwan da zurfinsa ya kai ni gwiwa. Ya sāke auna kamu dubu ya kuma bi da ni a ruwan da zurfinsa kama ni a gindi.
5 And he measured again a thousand [cubits], it being a stream that I could not wade through; for the water was increased, being water fit to swim in, a stream that could not be waded through.
Ya auna wani kamu dubu, amma a yanzu ruwan ya zama kogin da ban iya hayewa ba, domin ruwan ya taso ya kuma yi zurfin da ya isa a yi iyo a ciki, kogin da ba za a iya hayewa ba.
6 And he said unto me, Son of man, hast thou seen this: Then did he lead me, and caused me to return to the bank of the stream.
Sai ya ce mini, “Ɗan mutum, ka ga wannan?” Sa’an nan ya komo da ni zuwa bakin kogin.
7 Now when I returned, behold, there were at the banks of the stream very many trees, on the one side and on the other.
Sa’ad da na iso can, sai na ga itatuwa masu yawa a kowane gefen kogin.
8 Then said he unto me, These waters issue out toward the eastern district, and go down into the plain, and fall into the sea, [the waters] being carried forth into the sea, so that the waters shall be healed.
Sai ya ce mini, “Wannan ruwa yana malalowa zuwa yankin gabas ya kuma gangaro zuwa cikin Araba, inda zai shiga Teku. Sa’ad da ya shiga cikin Tekun sai ruwan a can ya zama mai daɗi.
9 And it shall come to pass, that every thing that liveth, which moveth, whithersoever the double-stream shall come, shall live: and the fish shall be [therein] in great abundance; for when this water shall have come thither, [the waters of the sea] shall be healed, and every thing shall live whither the stream cometh.
Tarin halittu masu rai za su rayu a duk inda ruwan ya malalo. Za a kasance da kifi masu yawa, domin wannan ruwa yana malalowa a can yana kuma mai da ruwan gishiri yă zama ruwa mai daɗi; saboda haka duk inda ruwan ya malalo, kome zai rayu.
10 And it shall come to pass, that the fishers shall stand by it; from 'En-gedi even unto 'En-'eglayim, there shall be places for the spreading out of nets: after their various kinds shall the fish thereof be, like the fish of the great sea, exceedingly many.
Masunta za su tsaya a gaɓar; daga En Gedi zuwa En Eglayim, za a kasance da wuraren jefa abin kamun kifi. Za a sami kifayen iri-iri, kamar kifaye Bahar Rum.
11 But its swamps and its lagoons shall not be healed, for [the production of] salt are they destined.
Amma fadamun da tafkunan ba za su zama masu daɗi ba; za a bar su a gishirinsu.
12 And by the stream upon its banks, on this side and on that side, shall grow up all kinds of trees for food, the leaves of which shall not fade, and the fruit of which shall not come to an end, every month shall they bring forth new ripe fruit; because its water is that which issueth out of the sanctuary; and their fruit shall serve for food, and their leaves for remedies.
’Ya’yan itatuwa na kowane iri za su yi girma a kowane gefen kogin. Ganyayensu ba su bushe ba, ba kuwa za su fasa yin’ya’ya ba. Kowane wata za su ba da’ya’ya domin ruwa daga wuri mai tsarki yana malalo musu.’Ya’yansu za su zama abinci, ganyayensu kuma za su zama magani.”
13 Thus hath said the Lord Eternal, This shall be the boundary, whereby ye shall divide out the land unto the twelve tribes of Israel: Joseph shall have two portions.
Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa, “Waɗannan su ne iyakokin da za ku raba ƙasar gādo cikin kabilan Isra’ila goma sha biyu, da rabo biyu don Yusuf.
14 And ye shall inherit it, every one like the other, [the land] concerning which I lifted up my hand to give it unto your fathers: and this land shall fall unto you for an inheritance.
Za ku raba ta daidai a cikinsu. Gama na ɗaga hannu na rantse zan ba da ita ga kakanninku, wannan ƙasa za tă zama gādonku.
15 And this shall be the boundary of the land: On the north side, from the great sea, the road to Chethlon, as far as to Zedad;
“Wannan ce za tă zama iyakar ƙasa. “A wajen arewa za tă fara daga Bahar Rum ta hanyar Hetlon ta wuce Lebo Hamat zuwa Zedad,
16 Chamath, Berothah, Sibrayim, which is between the boundary of Damascus and the boundary of Chamath; Chazar-hattichon, which is by the boundary of Chavran.
Berota da Sibrayim (wadda take a iyaka tsakanin Damaskus da Hamat), har zuwa Hazer-Hattikon, wadda take a iyakar Hauran.
17 And the boundary shall be from the sea to Chazar-'enon, the boundary of Damascus, and the northern part on the north, and the boundary of Chamath. And this is the north side.
Iyakar za tă miƙe daga teku zuwa Hazar-Enon, ta iyakar Damaskus, da iyakar Hamat a arewa. Wannan ita ce iyakar a wajen arewa.
18 And the east side shall ye measure between Chavran and Damascus [on the one side], and between Gil'ad and the land of Israel [on the other side] by the Jordan, from the [north] boundary unto the east sea. And this is the east side.
A wajen gabas iyakar za tă kama tsakanin Hauran da Damaskus, ta bi ta Urdun tsakanin Gileyad da ƙasar Isra’ila, zuwa tekun gabas har zuwa Tamar. Wannan ita ce iyakar a wajen gabas.
19 And the south side; on the south, from Thamar even to the waters of contention at Kadesh, toward the brook [flowing] into the Great Sea. And this is the south side on the south.
A wajen kudu za tă fara daga Tamar har zuwa ruwan Meriba Kadesh, sa’an nan ta bi Rafin Masar zuwa Bahar Rum. Wannan ita ce iyakar a wajen kudu.
20 And the west side shall be the great sea from the [southern] boundary, as far as straight up to Chamath. This is the west side.
A wajen yamma, Bahar Rum ne zai zama iyakar zuwa wani wuri ɗaura da Lebo Hamat. Wannan ita ce iyakar a wajen yamma.
21 And ye shall divide this land among yourselves according to the tribes of Israel.
“Za ku rarraba wannan ƙasa a tsakaninku bisa ga kabilan Isra’ila.
22 And it shall come to pass, that ye shall divide it by lot for an inheritance among yourselves, and to the strangers that sojourn in the midst of you, who shall have begotten children in the midst of you; and they shall be unto you as the native born among the children of Israel: with you shall they obtain an inheritance in the midst of the tribes of Israel.
Za ku raba ta kamar gādo wa kanku da kuma wa baƙin da suka zauna a cikinku waɗanda suke da’ya’ya. Za ku ɗauka su kamar’yan ƙasa haifaffun Isra’ilawa; za su yi gādo tare da ku a cikin kabilan Isra’ila.
23 And it shall come to pass that in whatever tribe the stranger sojourneth, there shall ye give him his inheritance, saith the Lord Eternal.
A duk kabilar da baƙon yake zama, a can za ku ba shi gādonsa,” in ji Ubangiji Mai Iko Duka.