< Ezekiel 4 >

1 But thou, O son of man, take thyself a tile, and lay it before thee, and engrave upon it a city, [namely, ] Jerusalem:
“Yanzu, ɗan mutum, ka ɗauki tubalin yumɓu, ka ajiye shi a gabanka ka kuma zāna birnin Urushalima a kansa.
2 And place around it a siege, and build works of attack against it, and cast up a mound against it; and arrange around it encampments, and place against it battering rams round about.
Sa’an nan ka yi mata ƙawanya. Ka kafa mata katangar ƙawanya, ka gina katangar da ɗan tudu ka kewaye ta da dundurusai.
3 Moreover take thou unto thyself an iron pan, and set it up as a wall of iron between thee and the city: and direct thy face against it, that it may be placed in a state of siege, and lay siege against it. This shall be a sign for the house of Israel.
Sa’an nan ka ɗauki kwanon ƙarfe, ka shirya shi kamar katangar ƙarfe tsakaninka da birnin ka kuma zuba mata ido. Za tă kasance a ƙarƙashin ƙawanya, kai kuwa za ka yi mata ƙawanya. Wannan zai zama alama ga gidan Isra’ila.
4 And as for thyself, lie upon thy left side, and lay the iniquity of the house of Israel upon it: [after] the number of the days that thou shalt lie upon it shalt thou bear their iniquity.
“Sa’an nan ka kwanta a hagunka ka kuma sa zunubin gidan Isra’ila a kanka. Za ka ɗauki zunubinsu na waɗansu kwanakin da kake kwance a gefenka.
5 But as for myself, I lay upon thee the years of their iniquity, after the number of the days, three hundred and ninety days: so shalt thou bear the iniquity of the house of Israel.
Na ɗora maka kwanaki bisa ga shekarun zunubinsu. Saboda haka cikin kwana 390 za ka ɗauki zunubin gidan Isra’ila.
6 And when thou hast made an end of them, thou shalt lie on thy right side, the second time, and thou shalt bear the iniquity of the house of Judah forty days: a day each for a year, a day for a year do I lay it on thee.
“Bayan ka gama haka, ka sāke kwantawa, a wannan lokaci a gefen damarka, ka kuma ɗauki zunubin gidan Yahuda. Na ɗora maka kwanaki 40, kwana guda a madadin shekara guda.
7 And toward the siege of Jerusalem shalt thou direct thy face with thy arm uncovered, and thou shalt prophesy against it.
Ka juya fuskarka wajen ƙawanyar Urushalima da hannunka a buɗe ka yi annabci a kanta.
8 And, behold, I will lay ropes upon thee, that thou mayest not turn thyself from one side to the other, till thou hast made an end of the days of thy siege.
Zan ɗaura ka da igiyoyi don kada ka juya daga wannan gefe zuwa wani gefe sai ka gama kwanakin ƙawanyarka.
9 But thou take unto thee wheat, and barley, and beans, and lentiles, and millet, and spelt, and put them in one vessel, and make thyself bread thereof, [after] the number of the days that thou shalt lie upon thy side, three hundred and ninety days, shalt thou eat it.
“Ka ɗauki alkama da sha’ir, wake da acca, gero da maiwa; ka sa su a tulun ajiya ka kuma yi amfani da su don yin burodi wa kanka. Za ka ci shi a kwanaki 390 da za ka kwanta a gefenka.
10 And thy food which thou shalt eat shall be by weight, twenty shekels for every day: from one time to the other time shalt thou eat it.
Ka auna shekel ashirin na abinci don kowace rana ka kuma ci shi a ƙayyadadden lokaci.
11 And water shalt thou drink by measure, the sixth part of a hin: from one time to the other time shalt thou drink [it].
Haka ma ka auna kashi ɗaya bisa shida na garwan ruwa ka sha shi a ƙayyadadden lokaci.
12 And in form of a barley-cake shalt thou eat it, and this shalt thou bake with balls of human excrement before their eyes.
Ka ci abinci yadda za ka ci ƙosai sha’ir, ka gasa shi a gaban mutane, ka yi amfani da najasar mutane kamar itacen wuta.”
13 And the Lord said, Even thus shall the children of Israel eat their bread unclean among the nations whither I will drive them.
Ubangiji ya ce, “Ta haka mutanen Isra’ila za su ci ƙazantaccen abinci a cikin al’ummai inda zan kore su in kai.”
14 Then said I, Ah Lord Eternal! behold, my soul hath not been defiled; and that which dieth of itself, or is torn in pieces, have I never eaten from my youth up even until now; and never is flesh of abomination come into my mouth.
Sai na ce, “Ba haka ba ne, Ubangiji Mai Iko Duka! Ban taɓa ƙazantar da kaina ba. Daga ƙuruciyata har zuwa yanzu ban taɓa cin wani abin da aka samu ya mutu ko abin da namun jeji suka kashe ba. Ba nama marar tsabtan da ya taɓa shiga bakina.”
15 Then said he unto me, Lo, I have given thee cow's dung instead of human excrement; and thou shalt prepare thy bread thereupon.
Sai ya ce, “To da kyau, zan bari ka gasa burodin a kan kashin shanu a maimakon najasar mutane.”
16 And he said unto me, Son of man, behold, I will break the staff of bread in Jerusalem; and they shall eat bread by weight, and with anxious care; and they shall drink water by measure, and in confusion;
Sa’an nan ya ce mini, “Ɗan mutum, zan yanke tanadin abinci a Urushalima. Mutane za su auna abincin da za su ci da tsoro su kuma auna ruwan da za su sha cikin fargaba,
17 In order that they may want bread and water, and be confounded one with the other, and pine away for their iniquity.
domin abinci da ruwa za su kāsa. Za su damu da ganin juna za su kuma lalace saboda zunubinsu.

< Ezekiel 4 >