< Ezekiel 38 >

1 And the word of the Lord came unto me, saying,
Maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
2 Son of man, direct thy face against Gog of the land of Magog, the prince of Rosh, Meshech and Thubal, and prophesy against him,
“Ɗan mutum, ka fuskanci Gog, na ƙasar Magog, babban sarkin Meshek da Tubal; ka yi annabci a kansa
3 And say, Thus hath said the Lord Eternal, Behold, I will be against thee, O Gog, the prince of Rosh, Meshech and Thubal;
ka ce, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa ina gāba da kai, ya Gog, babban sarkin Meshek da Tubal.
4 And I will derange thee, and put hooks into thy jaws, and I will bring thee forth, and all thy army, horses and horsemen, all of them clothed in elegant attire, a great assemblage with bucklers and shields, all of them grasping swords.
Zan juyar da kai, in sa ƙugiyoyi a muƙamuƙanka in fitar da kai tare da dukan sojojinka, dawakanka, mahayan dawakanka saye da makamai, da kuma jama’a mai girma masu riƙe da garkuwoyi manya da ƙanana, dukansu da takuba a zāre.
5 Persia, Cush, and Put [shall be] with them; all of them with shield and helmet;
Farisa, Kush da Fut za su kasance tare da su, duka riƙe da garkuwoyi da hulunan kwano,
6 Gomer and all of its armies; the house of Thogarmah out of the farthest north, and all its armies; many people shall be with thee.
haka ma Gomer da dukan sojojinsa, da Bet Togarma daga can arewa tare da dukan sojojinsa, al’ummai masu yawa tare da kai.
7 Be thou ready, and prepare thyself, thou, and all thy assemblages that are assembled about thee, and be thou a guard unto them.
“‘Ka shirya; ka kintsa, kai da dukan jama’arka da suka taru kewaye da kai, ka kuma zama mai ba su umarni.
8 After many days shalt thou be ordered forward; in the end of years shalt thou come into the land that is recovering from the sword, and is gathered together out of many people, against the mountains of Israel, which have been ruined for a very long time: [to a people] that are brought forth out of the nations, and that now dwell in safety, all of them.
Bayan kwanaki masu yawa za a kira ka. A shekaru masu zuwa za ka kai hari a ƙasar da ta farfaɗo daga yaƙi, wadda aka tattara mutanenta daga al’ummai masu yawa zuwa duwatsun Isra’ila, dā kango ne sosai. An fitar da su daga al’ummai, yanzu kuwa dukansu suna zama lafiya.
9 Thou wilt ascend and come like a tempest, like a cloud to cover the earth wilt thou be, thou, and all thy armies, and the many people with thee.
Kai da dukan sojojinka da kuma al’ummai masu yawa da suke tare da kai za ku haura, kuna cin gaba kamar hadari; za ku zama kamar girgijen da yake rufewa ƙasa.
10 Thus hath said the Lord Eternal, It will also come to pass, at the same time, that things will come into thy mind, and thou wilt entertain an evil device;
“‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa a ranar, tunani zai shiga cikin zuciyarka za ka kuma ƙirƙiro muguwar dabara.
11 And thou wilt say, I will go up over the land of open towns; I will come against those that are careless, that dwell in safety, all of whom dwell without walls, and have neither bars nor gates,
Za ka ce, “Zan kai hari wa ƙasar da ƙauyukanta ba su da katanga; zan fāɗa wa mutanen da suke zamansu kurum cikin salama, dukansu suna zama babu katanga babu ƙofofi ko ƙyamare.
12 To snatch up the spoil, and to take away the prey; to turn thy hand against the ruined places now inhabited, and against the people that are gathered out of the nations, that have gotten cattle and goods, that dwell in the highest part of the land.
Zan washe in kwashe ganima in kuma juye hannuna gāba da kufai da aka sāke zaunar da mutanen da aka tattara daga al’ummai, masu yawan shanu da kayayyaki, masu zama a tsakiyar ƙasa.”
13 Sheba, and Dedan, and the traders of Tharshish, with all her young lions, will say unto thee, Art thou come to plunder the spoil? hast thou gathered thy company to carry off the prey? to bear away silver and gold, to take away cattle and goods, to plunder a great spoil?
Sheba da Dedan da’yan kasuwar Tarshish da dukan ƙauyukanta za su ce maka, “Ka zo ka kwashe ganima ne? Ka tattara jama’arka don ka yi waso, ka kuma kwashe azurfa da zinariya, ka kwashe shanu da kayayyaki ka kuma ƙwace ganima mai yawa?”’
14 Therefore, prophesy, son of man, and say unto Gog, Thus hath said the Lord Eternal, Behold, on the day when my people of Israel dwelleth in safety, shalt thou know [my power].
“Saboda haka ɗan mutum, ka yi annabci ka ce wa Gog, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa a ranar, sa’ad da mutanena Isra’ila suna zaman lafiya, ba za ka sani ba?
15 And thou wilt come from thy place out of the farthest ends of the north, thou, and many people with thee, all of them riding upon horses, a great assemblage, and a mighty army;
Za ka zo daga wurinka a can arewa, kai da al’ummai masu yawa tare da kai, dukansu suna hawan dawakai, jama’a mai yawa, babbar runduna.
16 And thou wilt come up against my people of Israel, like a cloud to cover the land; in the latter days will this be, and I will bring thee over my land, in order that the nations may know me, when I am sanctified on thee, before their eyes, O Gog.
Za ka ci gaba a kan mutanena Isra’ila kamar yadda girgijen yakan rufe ƙasa. A kwanaki masu zuwa, ya Gog, zan kawo ka, ka yi yaƙi da ƙasata, domin al’ummai su san ni sa’ad da na nuna kaina mai tsarki ta wurinka a gabansu.
17 Thus hath said the Lord Eternal, Art thou [not] he of whom I have spoken in ancient days through means of my servants the prophets of Israel, who prophesied in those days [many] years, that I would bring thee against them?
“‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa ba kai ba ne na yi magana da kai a kwanakin dā ta wurin bayina annabawan Isra’ila? A lokacin sun yi annabci shekaru masu yawa cewa zan kawo ka, ka yaƙe su.
18 And it shall come to pass at the same time, on the day of Gog's coming over the land of Israel, saith the Lord Eternal, that my fury shall be kindled in my nose.
Ga abin da zai faru a ranar. Sa’ad da Gog ya fāɗa wa ƙasar Isra’ila, fushina mai zafi zai ƙuna, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.
19 And in my zealousness, in the fire of my wrath, have I spoken, Surely on that day there shall be a great earthquake in the country of Israel;
Cikin kishina da hasalata mai zafi zan furta cewa a wannan lokaci za a yi babbar girgizar ƙasa a ƙasar Isra’ila.
20 And there shall quake at my presence the fishes of the sea, and the fowls of the heaven, and the beasts of the field, and every creeping thing that creepeth upon the earth, and all the men that are upon the face of the earth, and the mountains shall be thrown down, and the cliffs shall fall, and every wall shall fall to the ground.
Kifin teku, tsuntsayen sarari, namun jeji, kowace halitta mai rarrafe da kuma dukan mutane a duniya za su yi rawar jiki a gabana. Za a tumɓuke duwatsu, a ragargaza tsaunuka, kuma kowane bango zai fāɗi ƙasa.
21 And I will call against him throughout all my mountains for the sword, saith the Lord Eternal: every man's sword shall be against his brother.
Zan kira takobi a kan Gog a dukan duwatsuna, in ji Ubangiji Mai Iko Duka. Kowane takobin mutum zai yi gāba da ɗan’uwansa.
22 And I will hold judgment over him with pestilence and with blood [-shedding]; and an overflowing rain, and great hailstones, fire, and sulfur will I let rain over him and his armies, and over the many people that are with him.
Zan yi hukunci a kansa da annoba da kuma zub da jini; zan yi ruwa mai yawa da ƙanƙara da kibiritu mai cin wuta a kansa da a kan sojojinsa da kuma a kan al’ummai masu yawa da suke tare da shi.
23 Thus will I magnify myself, and sanctify myself, and make myself known before the eyes of many nations: and they shall know that I am the Lord.
Ta haka zan nuna girmana da kuma tsarkina, zan sanar da kaina a gaban al’ummai masu yawa. Sa’an nan za su san cewa ni ne Ubangiji.’

< Ezekiel 38 >