< Ezekiel 37 >

1 There came over me the inspiration of the Lord, and he carried me out in the spirit of the Lord, and set me down in the midst of the valley which was full of bones;
Hannun Ubangiji yana a kaina, ya kuma fitar da ni ta wurin Ruhun Ubangiji ya sa ni a tsakiyar kwarin; yana cike da ƙasusuwa.
2 And he caused me to pass by them all round about; and, behold, there were very many of them on the surface of the valley; and, lo, they were very dry.
Ya sa na kai na komo a ciki, na kuma ga ƙasusuwa masu girma da yawa a ƙasar kwarin, ƙasusuwan da suka bushe ƙwarai.
3 And he said unto me, Son of man, can these bones live! And I said, O Lord Eternal, thou alone knowest this.
Sai ya tambaye ni cewa, “Ɗan mutum, waɗannan ƙasusuwa za su iya rayu?” Ni kuwa na ce, “Ya Ubangiji Mai Iko Duka, kai kaɗai ka sani.”
4 And he said unto me, Prophesy over these bones, and say unto them, O ye dry bones, hear ye the word of the Lord.
Sai ya ce mini, “Ka yi wa waɗannan ƙasusuwa annabci ka ce musu, ‘Busassun ƙasusuwa, ku ji maganar Ubangiji!
5 Thus hath said the Lord Eternal unto these bones, Behold, I will bring a spirit into you, and ye shall live;
Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka ya ce wa waɗannan ƙasusuwa. Zan sa numfashi ya shiga muku, za ku kuwa rayu.
6 And I will lay sinews upon you, and bring up flesh upon you, and draw over you a skin, and put a spirit in you, and ye shall live: and ye shall experience that I am the Lord.
Zan harhaɗa muku jijiyoyi in sa muku tsoka in kuma rufe ku da fata; zan sa numfashi a cikinku, za ku kuwa rayu. Sa’an nan za ku san cewa ni ne Ubangiji.’”
7 And so I prophesied as I had been commanded: and there was a sound, as I prophesied, and behold there was a rustling noise, and the bones came together, bone to its bone.
Saboda haka sai na yi annabci yadda aka umarce ni. Da nake annabcin, sai aka ji motsi, ƙarar girgiza, sai ƙasusuwan suka harhaɗu, ƙashi ya haɗu da ƙashi.
8 And I looked, and behold, there were sinews upon them, and the flesh came up, and the skin was drawn over them above; but no spirit was in them.
Na duba, sai ga jijiyoyi da nama suka bayyana a kansu fata kuma ta rufe su, amma ba numfashi a cikinsu.
9 Then said he unto me, Prophesy unto the spirit; prophesy, son of man, and say to the spirit, Thus hath said the Lord Eternal, From the four winds come, O spirit, and breathe into these slain ones, that they may live.
Sa’an nan ya ce mini, “Ka yi annabci wa numfashi; ka yi annabci, ɗan mutum, ka ce masa, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa ka fito daga kusurwoyi huɗu, ya numfashi, ka kuma numfasa cikin waɗannan matattu, don su rayu.’”
10 And I prophesied as he had commanded me, and there came into them the spirit, and they lived, and stood up upon their feet, an exceedingly great army.
Saboda haka na yi annabci yadda aka umarce ni, sai numfashi ya shiga musu; suka rayu suka kuma miƙe tsaye a ƙafafunsu babbar runduna ce ƙwarai.
11 Then said he unto me, Son of man, these bones are the whole house of Israel: behold, they say, Dried are our bones, and lost is our hope; we are quite cut off.
Sa’an nan ya ce mini, “Ɗan mutum, waɗannan ƙasusuwa su ne dukan gidan Isra’ila. Suna cewa, ‘Ƙasusuwanmu sun bushe, sa zuciyarmu duk ya tafi; an share mu ƙaf.’
12 Therefore prophesy and say unto them, Thus hath said the Lord Eternal, Behold, I will open your graves, and I will cause you to come up out of your graves, O my people, and I will bring you into the land of Israel.
Saboda haka yi annabci ka ce musu, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa ya mutanena, zan buɗe kaburburanku in fitar da ku daga cikinsu; zan mai da ku ƙasar Isra’ila.
13 And ye shall know that I am the Lord, when I open your graves, and when I cause you to come up out of your graves, O my people.
Sa’an nan ku, mutanena, za ku san cewa ni ne Ubangiji, sa’ad da na buɗe kaburburanku na fitar da ku daga cikinsu.
14 And I will put my spirit in you, and ye shall live, and I will place you in your own land: and ye shall acknowledge that I the Lord have spoken it, and done it, saith the Lord.
Zan sa Ruhuna a cikinku za ku kuwa rayu, zan kuma zaunar da ku a ƙasarku. Sa’an nan za ku san cewa Ni Ubangiji na faɗa, zan kuma aikata, in ji Ubangiji.’”
15 And the word of the Lord came unto me, saying,
Maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
16 But thou, son of man, take unto thyself one stick of wood, and write upon it, “For Judah, and for the children of Israel his companions;” then take another stick, and write upon it, “For Joseph, —the stick of Ephraim, and for all the house of Israel his companions:”
“Ɗan mutum, ka ɗauki sanda ka rubuta a kansa, ‘Na Yahuda da Isra’ilawan da suke tare da shi.’ Sa’an nan ka ɗauki wani sanda, ka rubuta a kansa, ‘Sandan Efraim, na Yusuf da dukan gidan Isra’ilan da suke tare da shi.’
17 And join them one to the other unto thee as one stick; and they shall become one in thy hand.
Ka haɗa su su zama sanda guda saboda su kasance ɗaya a hannunka.
18 And if the children of thy people should say unto thee, saying, Wilt thou not tell us what thou meanest by these?
“In mutanen ƙasarka suka tambaye ka cewa, ‘Ba za ka faɗa mana abin da kake nufi da wannan ba?’
19 [Then] speak unto them, Thus hath said the Lord Eternal, Behold, I will take the stick of Joseph, —which is in the hand of Ephraim, —and the tribes of Israel his companions, and will lay them upon him, even the stick of Judah, and make them into one stick, and they shall be one in my hand.
Ka ce musu, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa, Zan ɗauki sandan Yusuf, wanda yake a hannun Efraim, da na kabilan Isra’ilawan da suke tare da shi, in haɗa shi da sandan Yahuda, in mai da su sanda guda, za su kuwa zama ɗaya a hannuna.’
20 And the sticks whereon thou shalt have written shall be in thy hand before their eyes.
Ka riƙe sandunan da ka yi rubutun a gabansu
21 And speak unto them, Thus hath said the Lord Eternal, Behold, I will take the children of Israel from among the nations, whither they are gone, and I will gather them from every side, and bring them unto their own land;
ka ce musu, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa zan fitar da Isra’ilawa daga al’ummai inda suka tafi. Zan tattara su daga dukan kewaye in komo da su ƙasarsu.
22 And I will make them into one nation in the land, on the mountains of Israel; and one king shall be to them all for king; and they shall not be any more two nations, nor shall they at any time be divided into two kingdoms any more:
Zan mai da su al’umma ɗaya a cikin ƙasar, a kan duwatsun Isra’ila. Za a kasance da sarki guda a kan dukansu ba za su ƙara zama al’ummai biyu ko su rabu su zama masarautai biyu ba.
23 Neither shall they defile themselves any more with their idols, and with their detestable things, and with all their transgressions; but I will save them out of all their dwelling-places, wherein they have sinned, and I will cleanse them, and they shall be unto me for a people, and I will be to them for a God.
Ba za su ƙara ƙazantar da kansu da gumaka da mugayen siffofi ko kuma da wani daga laifofinsu ba, gama zan cece su daga dukan zunubinsu na ridda, zan kuma tsarkake su. Za su zama mutanena, ni kuma zan zama Allahnsu.
24 And my servant David shall be king over them; and one shepherd shall be for them all: and in my ordinances shall they walk, and my statutes shall they observe, and do them.
“‘Bawana Dawuda zai zama sarki a kansu, dukansu kuwa za su kasance da makiyayi guda. Za su bi dokokina su kuma kiyaye ƙa’idodina.
25 And they shall dwell in the land that I have given unto my servant, unto Jacob, wherein your fathers have dwelt; and they shall dwell therein, they, and their children, and their children's children for ever: and David my servant shall be prince unto them for ever.
Za su zauna a ƙasar da na ba wa bawana Yaƙub, ƙasar da kakanninsu suka zauna. Su da’ya’yansu da’ya’ya’ya’yansu za su zauna a can har abada, kuma Dawuda bawana zai zama sarkinsu har abada.
26 And I will make with them a covenant of peace, an everlasting covenant shall it be with them: and I will multiply them, and I will set my sanctuary in the midst of them for evermore.
Zan yi alkawarin salama da su; zai zama madawwamin alkawari. Zan kafa su in ƙara yawansu, zan kuma sa wuri mai tsarkina a cikinsu har abada.
27 My dwelling also shall be with them, and I will be unto them for a God; and they shall be unto me as a people.
Mazaunina zai kasance da su; zan kuwa zama Allahnsu, za su kuma zama mutanena.
28 And the nations shall know that I am the Lord who sanctify Israel, when my sanctuary will be in the midst of them for evermore.
Sa’an nan al’ummai za su san cewa Ni Ubangiji na mai da Isra’ila mai tsarki, sa’ad da wuri mai tsarkina yana a cikinsu har abada.’”

< Ezekiel 37 >