< Ezekiel 36 >

1 But thou, son of man, prophesy unto the mountains of Israel, and say, O mountains of Israel, hear ye the word of the Lord.
“Ɗan mutum, ka yi annabci wa duwatsun Isra’ila ka ce, ‘Ya duwatsun Isra’ila, ku ji maganar Ubangiji.
2 Thus hath said the Lord Eternal, Because the enemy hath said regarding you, Aha, even the ancient high-places are become ours as a possession:
Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa abokin gāba yana magana game da ku cewa, “Yauwa! Tsofaffin tuddai sun zama mallakarmu yanzu.”’
3 Therefore prophesy and say, Thus hath said the Lord Eternal, Because, even because men have made you desolate, and sought to swallow you up on every side, that ye might become a possession unto the residue of the nations, and ye are taken up as a talk for tongues, and an evil report of the people:
Saboda haka ka yi annabci ka ce, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa domin sun lalace ku suka kuma maishe ku kufai marar amfani a kowane gefe saboda ku zama mallakar sauran al’ummai da kuma abin magana da tsegumi ga mutane,
4 Therefore, O mountains of Israel, hear ye the word of the Lord Eternal, Thus hath said the Lord Eternal to the mountains, and to the hills, to the ravines, and to the valleys, to the desolate ruins, and to the cities that are forsaken, which are become a prey and derision to the residue of the nations that are round about:
saboda haka, ya duwatsun Isra’ila, ku ji maganar Ubangiji Mai Iko Duka, ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana faɗa wa duwatsu da tuddai, wa kwazazzabai da kwaruruka, wa kufai da garuruwan da suka zama kango waɗanda aka washe aka wulaƙanta suka zama ganimar sauran al’ummai da suke kewaye da ku,
5 Therefore thus hath said the Lord Eternal, Surely in the fire of my jealousy have I spoken against the residue of the nations, and against all Idumea, that have appropriated my land unto themselves as a possession with the joy of all their heart, with derision in their soul, in order to drive it out that it may be for a prey.
ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa cikin kishina mai ƙuna na yi magana gāba da sauran al’ummai, da kuma gāba da Edom, gama da farin ciki da reni a zukatansu suka mai da ƙasata mallakarsu don su washe wuraren kiwonta.’
6 Therefore prophesy concerning the land of Israel, and say unto the mountains, and to the hills, to the ravines, and to the valleys, Thus hath said the Lord Eternal, Behold, In my zealousness and in my fury have I spoken, because ye have borne the reproach of the nations:
Saboda haka ka yi annabci game da ƙasar Isra’ila ka kuma ce wa duwatsu da tuddai, wa kwazazzabai da kwaruruka, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa ga shi, na yi magana da kishina da hasalata saboda sun sha zargi wurin al’ummai.
7 Therefore thus hath said the Lord Eternal, I have indeed lifted up my hand, that the nations who are round about you— these shall bear their shame.
Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa na ɗaga hannuna sama na rantse cewa al’ummai da suke kewaye da ku za su sha ba’a.
8 But ye, O mountains of Israel, ye shall send forth your boughs, and your fruit shall ye bear for my people Israel, for they are near at hand to come.
“‘Amma ku, ya duwatsun Isra’ila, za ku miƙa rassanku ku ba da amfani ga mutanena Isra’ila, gama ba da daɗewa ba za su komo gida.
9 For, behold, I will be for you, and I will turn unto you, and ye shall be tilled and ye shall be sown;
Na damu da ku kuma zan dube ku da tausayi; za ku nome ku kuma shuka,
10 And I will multiply upon you men, all the house of Israel— altogether; and the cities shall be inhabited again, and the ruins shall be rebuilt;
zan kuma riɓaɓɓanya mutane a kanku, dukan gidan Isra’ila ke nan. Za a zauna a birane a kuma sāke gina rusassun wurare.
11 And I will multiply upon you men and beast, and they shall increase and be fruitful; and I will cause you to be inhabited after your old estates, and will do more good unto you than at your beginnings: and ye shall know that I am the Lord.
Zan sa mutane da dabbobi su yi yawa a kanku, za su kuma ba da’ya’ya su kuma yi yawa. Zan zaunar da mutane a kanku kamar dā zan kuma sa ku wadaita fiye da dā. Sa’an nan za ku san cewa ni ne Ubangiji.
12 Yea, I will cause to walk upon you men, even my people Israel, and they shall possess thee, and thou shalt be unto them as an inheritance, and thou shalt not any more henceforth cast them out.
Zan sa mutanena Isra’ila su yi tafiya a kanku. Za su mallake ku, za ku kuma zama gādonsu; ba za ku ƙara sa su rasa’ya’yansu ba.
13 Thus hath said the Lord Eternal, Because they say unto you, Thou land devourest up men, and hast been one that hath ever cast out thy nations:
“‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa domin mutane suna magana game da ku cewa, “Kun cinye mutane kuka kuma sa al’ummarku ta rasa’ya’yanta,”
14 Therefore shalt thou not devour up men any more, and thy nations shalt thou not cast out any more, saith the Lord Eternal.
saboda haka ba za ku ƙara cinye mutane ko ku sa al’ummarku ta rasa’ya’ya ba, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.
15 And I will not let be heard against thee any more the reproach of the nations, and the disgrace of the people shalt thou not bear any more, and thy nations shalt thou not cast out any more, saith the Lord Eternal.
Ba zan ƙara bari ku ji maganar banza ta al’ummai ba, ba kuwa za ku ƙara shan ba’ar mutane ko in sa al’ummarku ta fāɗi ba, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.’”
16 And the word of the Lord came unto me, saying,
Maganar Ubangiji ta sāke zuwa mini cewa,
17 Son of man, the house of Israel, when they dwelt in their own land, defiled it through their way and through their doings: like the uncleanness of a woman in her separation was their way before me.
“Ɗan mutum, sa’ad da mutanen Isra’ila suke zama a ƙasarsu, sun ƙazantar da ita ta wurin halinsu da kuma ayyukansu. Halinsu ya yi kamar rashin tsarkin mace a lokacin al’adarta a gabana.
18 And I poured out my fury over them because of the blood that they had shed in the land, and because through their idols they had polluted it;
Saboda haka na husata da su domin sun yi kisankai a ƙasar kuma domin sun ƙazantar da ita da gumakansu.
19 And I scattered them among the nations, and they were dispersed through the countries: according to their way and according to their doings did I judge them.
Na warwatsa su cikin al’ummai, suka kuwa warwatsu cikin dukan ƙasashe; na hukunta su gwargwadon halinsu da ayyukansu.
20 And when they were come unto the nations, whither they were gone, they profaned my holy name; because they said of them, These are the people of the Lord, and out of his land are they gone forth.
Kuma ko’ina da suka tafi a cikin al’ummai sun ɓata sunana mai tsarki, gama an yi magana a kansu cewa, ‘Waɗannan mutanen Ubangiji ne, duk da haka dole su bar ƙasarsa.’
21 But I had pity for my holy name, which the house of Israel had profaned among the nations, whither they were gone.
Na damu saboda sunana mai tsarki, wanda gidan Isra’ila ya ɓata a cikin al’ummai inda suka tafi.
22 Therefore say unto the house of Israel, Thus hath said the Lord Eternal, Not for your sake do I this, O house of Israel, but for the sake of my holy name, which ye have profaned among the nations, whither ye are gone.
“Saboda haka ka faɗa musu cewa, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa ba dominku ba ne, ya gidan Isra’ila da nake yin waɗannan abubuwa, amma saboda sunana ne mai tsarki, wanda kuka ɓata a cikin al’ummai inda kuka tafi.
23 And I will sanctify my great name, which was profaned among the nations, which ye have profaned in the midst of them; and the nations shall know that I am the Lord, saith the Lord Eternal, when I will be sanctified through you before your eyes.
Zan nuna tsarkin girman sunana, wanda aka ɓata a cikin al’umma, sunana da kuka ɓata a cikinsu. Sa’an nan al’ummai za su san cewa ni ne Ubangiji, in ji Ubangiji Mai Iko Duka, sa’ad da na nuna kaina mai tsarki ta wurinku a idanunsu.
24 And I will take you from among the nations, and I will gather you out of all the countries, and I will bring you unto your own land.
“‘Gama zan fitar da ku daga al’ummai; zan tattara ku daga dukan ƙasashe in komo da ku zuwa ƙasarku.
25 And I will sprinkle upon you clean water, and ye shall be clean: from all your impurities, and from all your idols, will I cleanse you.
Zan yayyafa muku ruwa mai tsabta, zan kuwa tsarkake ku daga dukan ƙazantarku daga kuma dukan gumakanku.
26 And I will give you a new heart, and a new spirit will I put within you; and I will remove the heart of stone out of your body, and I will give you a heart of flesh.
Zan ba ku sabuwa zuciya in kuma sa sabon ruhu a cikinku; zan fid da zuciyar dutse in kuma ba ku zuciyar nama.
27 And my spirit I will put within you, and I will cause that you shall walk in my statutes, and that my ordinances ye shall keep, and do them.
Zan kuma sa Ruhuna a cikinku in kuma motsa ku ku bi ƙa’idodina ku kuma kiyaye dokokina.
28 And ye shall dwell in the land which I gave to your fathers; and ye shall be unto me for a people, and I truly will be unto you as a God.
Za ku zauna a ƙasar da na ba wa kakanninku; za ku zama mutanena, ni kuwa zan zama Allahnku.
29 And I will save you from all kinds of your impurities; and I will call unto the corn, and increase it, and I will not lay famine upon you.
Zan cece ku daga dukan rashin tsabtarku. Zan sa hatsi ya yi yalwa ba zan kawo yunwa a kanku ba.
30 And I will multiply the fruit of the trees, and the products of the field: in order that ye may receive no more reproach on account of famine among the nations.
Zan ƙara’ya’yan itatuwa da amfanin gona, saboda kada ku ƙara shan kunya a cikin al’ummai saboda yunwa.
31 Then shall ye remember your ways that they were evil, and your doings that were not good; and ye shall loathe yourselves on account of your iniquities and on account of your abominations.
Sa’an nan za ku tuna mugayen hanyoyinku da mugayen ayyukanku, za ku kuwa ji ƙyamar kanku saboda zunubanku da kuma ayyukanku na banƙyama.
32 Not for your sake do I this, saith the Lord Eternal, be it known unto you: be ashamed and confounded because of your ways, O house of Israel.
Ina so ku san cewa ba na yi wannan saboda ku, in ji Ubangiji Mai Iko Duka. Ku ji kunya ku kuma giggita saboda halinku, ya gidan Isra’ila!
33 Thus hath said the Lord Eternal, On the day of my cleansing you from all your iniquities, when I cause the cities to be inhabited, and when the ruins are built up,
“‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa a ranar da na tsarkake ku daga dukan zunubanku, zan sāke zaunar da ku a garuruwanku, a kuma sāke gina kufai.
34 And when the desolate land is tilled, instead that it was a waste before the eyes of every passer by:
Ƙasar da take kango a dā za ku nome ta a maimakon zama kango a idon dukan masu ratsawa a cikinta.
35 Then shall they say, This land, that was desolate, is become like the garden of 'Eden; and the cities that were ruined, and desolate, and broken down, are become fortified, and inhabited.
Za su ce, “Wannan ƙasar da take kango a dā ta zama kamar lambu Eden; biranen da dā suke kufai, kango da kuma aka lalata, yanzu suna da katanga ana kuma zama a ciki.”
36 And the nations that are left round about you shall know that I the Lord have built up the broken-down [places], have planted the desolate [land]: I the Lord have spoken this, and have done it.
Sa’an nan al’ummai kewaye da ku da suka rage za su san cewa Ni Ubangiji na sāke gina abin da aka lalace na kuma sāke shuka abin da yake kango. Ni Ubangiji na faɗa, kuma zan aikata.’
37 Thus hath said the Lord Eternal, Also in this will I yet suffer myself to be entreated of by the house of Israel, to do it for them, I will increase them with men like flocks [in multitude].
“Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa har yanzu zan ji roƙon gidan Isra’ila in kuma yi musu wannan. Zan sa mutanensu su yi yawa kamar tumaki,
38 As the flocks of the holy things, as the flocks of Jerusalem on her appointed feasts, so shall the ruined cities be full of flocks of men: and they shall know that I am the Lord.
yawansu ya yi kamar garken tumaki don hadaya a Urushalima a ƙayyadaddun lokuta bukukkuwarta. Haka biranen da suke kufai za su cika da ɗumbun mutane. Sa’an nan za su san cewa ni ne Ubangiji.”

< Ezekiel 36 >