< Ezekiel 29 >

1 In the tenth year, in the tenth month, on the twelfth day of the month, came the word of the Lord unto me, saying,
A shekara ta goma, a wata na goma, a rana ta goma sha biyu, maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
2 Son of man, set thy face against Pharaoh the king of Egypt, and prophesy against him, and against all Egypt.
“Ɗan mutum, ka fuskanci Fir’auna sarkin Masar ka kuma yi annabci gāba da shi da dukan Masar.
3 Speak and say, Thus hath said the Lord Eternal, Behold, I will be against thee, O Pharaoh king of Egypt, the great crocodile that lieth in the midst of his streams, who hath said, Mine is my stream, and I have made it for myself.
Yi masa magana ka ce, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa, “‘Ina gāba da kai, Fir’auna sarkin Masar, kai babban mugun dodon ruwa kwance cikin rafuffukanka. Ka ce, “Nilu nawa ne; na yi shi wa kaina.”
4 But I will put hooks in thy jaws, and I will fasten the fish of thy streams on thy scales; and I will bring thee up out of the midst of thy streams, with all the fish of thy streams which shall stick fast on thy scales.
Amma zan sa ƙugiyoyi a muƙamuƙanka in sa kifin rafuffukanka su manne wa kamɓorinka. Zan jawo ka daga cikin tsakiyar rafuffukanka, da dukan kifayen rafuffukanka, waɗanda suka manne a ƙamborinka,
5 And I will cast thee out into the wilderness, thee with all the fish of thy streams; upon the open field shalt thou fall; thou shalt not be brought in, nor gathered up: to the beasts of the field and to the fowls of the heaven have I given thee for food.
Zan bar ka a cikin hamada, kai da dukan kifin rafuffukanka. Za ka fāɗi a fili ba kuwa za a tattara ka ko a kwashe ba. Zan ba da kai kamar abinci ga namun jeji na duniya da tsuntsayen sararin sama.
6 And all the inhabitants of Egypt shall know that I am the Lord; because they have been a reed-staff to the house of Israel.
Ta haka dukan waɗanda suke zama a Masar za su san cewa ni ne Ubangiji. “‘Ka zama sandan iwa domin gidan Isra’ila.
7 When they took hold of thee with the hand, thou wast cracked, and didst rend for them all the shoulder: and when they leaned upon thee, thou wast broken, and madest all their loins to be at a stand.
Sa’ad da suka kama ka da hannuwansu, ka tsattsage, ka kuma buɗu a kafaɗunsu; sa’ad da suka jingina a kanka, sai ka karye, bayansu kuwa ya firgita.
8 Therefore thus hath said the Lord Eternal, Behold, I will bring a sword upon thee, and I will cut off out of thee man and beast.
“‘Saboda haka ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa zan kawo takobi a kanka in kashe mutane da dabbobi.
9 And the land of Egypt shall be changed into a waste and ruin, and they shall know that I am the Lord; because he hath said, The stream is mine, and I have made it.
Masar za tă zama kufai. Sa’an nan za su san cewa ni ne Ubangiji. “‘Domin ka ce, “Nilu nawa ne; ni na yi shi,”
10 Therefore, behold, I will be against thee, and against thy streams, and I will render the land of Egypt a mass of ruins, a waste, and a wilderness, from Migdol to Seveneh even up to the border of Ethiopia.
saboda haka ina gāba da kai da rafuffukanka, zan kuma maishe ƙasar Masar ta lalace ta kuma zama kango daga Migdol zuwa Aswan, har iyakar Kush.
11 There shall not pass through it the foot of man, and the foot of beast shall not pass through it, and it shall not be inhabited forty years.
Ba ƙafar mutum ko ta dabbar da za tă ratsa ta; ba wanda zai zauna a can har shekaru arba’in.
12 And I will render the land of Egypt a desolate land in the midst of desolated countries, and her cities among the cities that are ruined shall be desolate forty years: and I will scatter the Egyptians among the nations, and will disperse them through the countries.
Zan mai da ƙasar Masar kufai a cikin ƙasashen da aka ragargaza, biranenta kuma za su zama kango har shekaru arba’in a cikin biranen da aka lalace. Zan watsar da Masarawa a cikin al’ummai in warwatsa su cikin ƙasashe.
13 For thus hath said the Lord Eternal, [only] at the end of forty years will I gather the Egyptians from the people whither they shall have been scattered;
“‘Duk da haka ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa a ƙarshen shekaru arba’in ɗin zan tattara Masarawa daga al’ummai inda aka warwatsa su.
14 And I will bring back the captivity of Egypt, and will cause them to return into the land of Pathros, into the land of their own origin: and they shall be there an unimportant kingdom.
Zan komo da su daga zaman bauta in mai da su zuwa Masar ta Bisa, ƙasarsu ta ainihi. A can za su zama masarauta marar ƙarfi.
15 Among the kingdoms it shall be the lowest; neither shall it raise itself any more above the nations: and I will diminish them, that they shall no more rule over the nations.
Za tă zama masarauta mafi rarrauna cikin masarautai, ba kuwa za tă ƙara ɗaga kanta a kan sauran al’ummai ba. Zan sa tă zama marar ƙarfi ƙwarai, har da ba za tă ƙara yin mulkin a kan al’ummai ba.
16 And it shall be no more unto the house of Israel for a dependence, bringing [their] iniquity to remembrance, when they turned after them: and they shall know that I am the Lord Eternal.
Masar ba za tă ƙara zama abin dogara ga mutanen Isra’ila ba amma za tă zama abin tunin zunubinsu na juyawa gare ta don taimako. Sa’an nan za su san cewa ni ne Ubangiji Mai Iko Duka.’”
17 And it came to pass in the seven and twentieth year, in the first month, on the first of the month, that the word of the Lord came unto me, saying,
A shekara ta ashirin da bakwai, a wata na fari a rana ta farko, maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
18 Son of man, Nebuchadrezzar the king of Babylon hath caused his army to perform a great service against Tyre; every head hath been made bald, and every shoulder hath been rubbed sore: yet no reward hath come to him or to his army from Tyre, for the service that he hath performed against it.
“Ɗan mutum, Nebukadnezzar sarkin Babilon ya sa sojojinsa su matsa wa Taya; kowane kai ya koɗe, kowace kafaɗa kuma ta goge. Duk da haka shi da sojojinsa ba su sami wani lada daga matsin da suka yi a kan Taya ba.
19 Therefore thus hath said the Lord Eternal, Behold, I will give unto Nebuchadrezzar the king of Babylon the land of Egypt; and he shall carry away its multitude, and take its spoil, and plunder its prey: and this shall be the reward for his army.
Saboda haka ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa zan ba da Masar ga Nebukadnezzar sarkin Babilon, zai washe dukiyarta. Zai kwashe ya washe ƙasar ganima a matsayin abin biyan sojojinsa.
20 As his recompense for that which he hath served against it, have I given him the land of Egypt, for that which they had done against me, saith the Lord Eternal.
Saboda haka na ba shi Masar a matsayin lada don ƙoƙarinsa domin shi da sojojinsa sun yi wannan domina ne, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.
21 On that day will I cause to grow a horn for the house of Israel, and unto thee will I open the mouth in the midst of them: and they shall know that I am the Lord.
“A wannan rana zan sa ƙaho ya tsiro wa gidan Isra’ila, zan kuma buɗe bakinka a cikinsu. Sa’an nan za su san cewa ni ne Ubangiji.”

< Ezekiel 29 >