< Ezekiel 20 >

1 And it came to pass in the seventh year, in the fifth month, on the tenth day of the month, that certain men of the elders of Israel came to inquire of the Lord, and they sat down before me.
A shekara ta bakwai, a wata na biyar a rana ta goma, waɗansu dattawan Isra’ila suka zo don su nemi nufin Ubangiji, suka kuwa zauna a ƙasa a gabana.
2 And the word of the Lord came unto me, saying,
Sai maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
3 Son of man, speak unto the elders of Israel, and say unto them, Thus hath said the Lord Eternal, Is it to inquire of me that ye are coming? as I live, I will not let myself be inquired of by you, saith the Lord Eternal.
“Ɗan mutum, ka yi magana da dattawan Isra’ila ka ce musu, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa kun zo ne ku nemi shawarata? Muddin ina raye, ba zan bari ku nemi shawarata ba, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.’
4 Wilt thou take them to task, wilt thou take them to task, son of man? then cause them to know the abominations of their fathers;
“Za ka hukunta su? Za ka hukunta su, ɗan mutum? To, sai ka kalubalance su da ayyukan banƙyamar kakanninsu
5 And say unto them, Thus hath said the Lord Eternal, On the day when I made choice of Israel, I lifted up my hand unto the seed of the house of Jacob, and I made myself known unto them in the land of Egypt: and I lifted up my hand unto them, saying, I am the Lord your God.
ka ce musu, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa a ranar da na zaɓi Isra’ila, na ɗaga hannuna, na rantse wa zuriyar gidan Yaƙub na kuma bayyana kaina gare su a Masar da hannun da na ɗaga na ce musu, “Ni ne Ubangiji Allahnku.”
6 On the same day I lifted up my hand unto them, to bring them forth from the land of Egypt into a land that I had selected for them, flowing with milk and honey, which is an ornament among all the countries.
A ranar na yi musu rantsuwa cewa zan fitar da su daga Masar zuwa ƙasar da na samo musu, ƙasa mai zub da madara da zuma, ƙasa mafi kyau cikin dukan ƙasashe.
7 And I said unto them, Cast ye away every one of the abominations of his eyes, and on the idols of Egypt shall ye not defile yourselves: I am the Lord your God.
Na kuma ce musu, “Kowannenku ya zubar da mugayen siffofin da kuka kafa idanunku a kai, kuma kada ku ƙazantar da kanku da gumakan Masar. Ni ne Ubangiji Allahnku.”
8 But they rebelled against me, and they would not hearken unto me; they did not cast away every one the abominations of their eyes, and the idols of Egypt did they not forsake: and I thought then to pour out my fury over them, to let out all my anger against them in the midst of the land of Egypt.
“‘Amma sai suka yi tawaye a kaina ba su kuwa saurare ni ba; ba su zubar da mugayen siffofin da suka kafa idanunsu a kai ba, balle su ƙi gumakan Masar. Saboda haka zan zubo hasalata a kansu in kuma aukar musu da fushina a Masar.
9 But I acted for the sake of my name, so as not to profane it before the eyes of the nations, in the midst of whom they were; because I had made myself known unto them before their eyes, to bring them forth out of the land of Egypt.
Amma saboda sunana na yi abin da zai kiyaye shi daga ƙazantuwa a idanun al’umman da suka zauna a ciki da kuma a idanun al’ummai da na bayyana kaina ga Isra’ilawa ta wurin fitar da su daga Masar.
10 I therefore caused them to go forth out of the land of Egypt, and brought them into the wilderness.
Saboda haka na fisshe su daga Masar na kawo su cikin hamada.
11 And I gave them my statutes, and my ordinances made I known to them, which a man is to do, that he may live through them.
Na ba su ƙa’idodina na kuma sanar musu da dokokina, gama mutumin da ya yi biyayya da su zai rayu ta wurinsu.
12 And also my sabbaths gave I unto them, to be as a sign between me and between them, that they might know that I am the Lord who sanctify them.
Na kuma ba su Asabbataina kamar alama tsakaninmu, domin su san cewa Ni Ubangiji ne yake tsarkake su.
13 But the house of Israel rebelled against me in the wilderness; in my statutes they walked not, and my ordinances they despised, which a man is to do, that he may live through them; and my sabbaths they greatly profaned: and I then thought to pour out my fury over them in the wilderness, to make an end of them.
“‘Duk da haka mutanen Isra’ila suka yi mini tawaye a cikin hamada. Ba su bi ƙa’idodina ba amma suka ki dokokina, ko da yake mutumin da ya yi biyayya da su zai rayu ta wurinsu, suka ɓata Asabbataina ƙwarai. Saboda haka na ce zan zuba hasalata a kansu in kuma hallaka su a hamada.
14 But I acted for the sake of my name, so as not to profane it before the eyes of the nations, before whose eyes I had brought them forth.
Amma saboda sunana na yi abin da zai kiyaye shi daga ƙazantuwa a idanun al’umman da a idonsu na fisshe su.
15 Yet did I also lift up my hand unto them in the wilderness, that I would not bring them into the land which I had given [them], flowing with milk and honey, which is an ornament among all the countries.
Na kuma ɗaga hannu na rantse musu a hamada cewa ba zan kawo su ƙasar da na ba su ba, ƙasa mai zub da madara da zuma, ƙasa mafi kyau cikin dukan ƙasashe,
16 Because my ordinances they had despised, and in my statutes they had not walked, and my sabbaths they had profaned; for after their idols did their heart go.
domin sun ƙi dokokina ba su kuwa bi ƙa’idodina ba suka kuma ƙazantar da Asabbataina. Gama zukatansu sun fi so su bauta wa gumakansu.
17 Nevertheless my eye looked pityingly on them, so as not to destroy them, and I did not make an end of them in the wilderness.
Duk da haka na dube su ta tausayi ba zan hallaka su ko in kawo ƙarshensu a hamada ba.
18 And I said unto their children in the wilderness, In the statutes of your fathers shall ye not walk, and their ordinances shall ye not keep, and on their idols shall ye not defile yourselves.
Na faɗa wa’ya’yansu a hamada, “Kada ku bi farillai kakanninku ko ku kiyaye dokokinsu ko ku ƙazantar da kanku da gumakansu.
19 I am the Lord your God: in my statutes must ye walk, and my ordinances must ye keep, and do them;
Ni ne Ubangiji Allahnku; ku bi ƙa’idodina ku kuma kula ku kiyaye dokokina.
20 And my sabbaths must ye sanctify; and they shall be as a sign between me and between you, that ye may know that I am the Lord your God.
Ku kiyaye Asabbataina da tsarki, don su zama alama tsakaninmu. Ta haka za ku san cewa ni ne Ubangiji Allahnku.”
21 Nevertheless the children rebelled against me; in my statutes did they not walk, and my ordinances they kept not to do them, which a man is to do, that he may live through them; my sabbaths they profaned: and I then thought to pour out my fury over them, to let out all my anger against them in the wilderness.
“‘Amma’ya’yan suka yi mini tawaye. Ba su bi ƙa’idodina ba, ba su kula su kiyaye dokokina ba, ko da yake mutumin da ya kiyaye su zai rayu ta wurinsu, suka kuma ƙazantar da Asabbataina. Saboda haka na ce zan zuba hasalata a kansu in kuma aukar musu da fushina a hamada.
22 But I withdrew my hand, and acted for the sake of my name, so as not to profane it before the eyes of the nations, before whose eyes I had brought them forth.
Amma na janye hannuna, kuma saboda sunana na yi abin da zai kiyaye shi daga ƙazantuwa a idanun al’umman da a idonsu na fisshe su.
23 I also lifted up my hand unto them in the wilderness, that I would scatter them among the nations, and disperse them through the countries;
Na kuma ɗaga hannu na rantse musu cewa zan watsar da su cikin al’ummai in kuma warwatsa su cikin ƙasashe,
24 Because my ordinances they had not executed, and my statutes they had despised, and my sabbaths they had profaned, and after the idols of their fathers their eyes were directed.
domin ba su kiyaye dokokina ba amma suka ƙi ƙa’idodina suka kuma ƙazantar da Asabbataina, idanunsu suka yi sha’awar gumakan kakanninsu.
25 And I also let them follow statutes that were not good, and ordinances whereby they could not live;
Na kuma ba da su ga farillan da ba su da kyau da dokokin da ba za su rayu ta wurinsu ba;
26 And I let them be defiled through their gifts, in that they caused to pass [through the fire] all that openeth the womb, in order that I might destroy them, to the end that they might know that I am the Lord.
na bari suka ƙazantu ta wurin kyautai, hadayar kowane ɗan fari don in cika su da abin tsoro domin su san cewa ni ne Ubangiji.’
27 Therefore, speak unto the house of Israel, O son of man, and say unto them, Thus hath said the Lord Eternal, Yet in this too did your fathers blaspheme me, by their committing a trespass against me:
“Saboda haka, ɗan mutum, ka yi magana da mutanen Isra’ila ka faɗa musu cewa, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa a wannan kuma kakanninku suka saɓe ni ta wurin yashe ni.
28 When I had brought them into the land, for which I had lifted up my hand to give it to them, they saw every high hill, and all the thick-branched trees, and they offered there their sacrifices, and presented there their provoking offerings, and they brought there their sweet savor, and poured out there their drink-offerings.
Sa’ad da na kawo su cikin ƙasar da na rantse zan ba su suka kuma ga tudu mai tsawo ko itace mai ganye, a can suka miƙa hadayunsu, suka yi sadakokin da suka tsokane ni na yi fushi, suka miƙa turaren ƙanshinsu suka kuma zuba sadakokinsu na sha.
29 Then said I unto them, What is this high-place whereunto ye go? And its name was called “The height” until this day.
Sai na ce musu, Wane ɗakin tsafi kuke tafiya?’” (Ana ce da shi Bama har wa yau.)
30 Therefore say unto the house of Israel, Thus hath said the Lord Eternal, Ha! do you pollute yourselves after the manner of your fathers; and after their abominations do ye go astray?
“Domin haka ka faɗa wa gidan Isra’ila, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa za ku ƙazantar da kanku yadda kakanninku suka yi ne ku yi sha’awar mugayen siffofinsu?
31 And when ye offer up your gifts, when ye make your sons pass through the fire, ye pollute yourselves with all your idols, even until this day: and I should allow myself to be inquired of by you, O house of Israel? As I live, saith the Lord Eternal, I will not let myself be inquired of by you.
Sa’ad da kuka miƙa kyautai naku, hadayar’ya’yanku maza a wuta, kuna cin gaba da ƙazantar da kanku da duka gumakanku har wa yau. Zan bari ku nemi shawarata, ya gidan Isra’ila? Muddin ina raye, in ji Ubangiji Mai Iko Duka, ba zan bari ku nemi shawarata ba.
32 And that which cometh up into your mind shall not at all come to pass, [namely, ] that ye say, We will be like the nations, like the families of the [other] countries, to serve wood and stone.
“‘Kukan ce, “Kuna so ku zama kamar sauran al’ummai, kamar sauran mutanen duniya, waɗanda suke bauta wa itace da dutse.” Amma abin da kuke tunani ba zai taɓa faruwa ba.
33 As I live, saith the Lord Eternal, surely, with a mighty hand, and with an outstretched arm, and with fury poured out, will I rule over you:
Muddin ina raye, in ji Ubangiji Mai Iko Duka, zan yi mulki a kanku da hannu mai iko da kuma hannu mai ƙarfi da kuma fushi.
34 And I will bring you out from the people, and I will gather you out of the countries wherein ye are scattered, with a mighty hand, and with an outstretched arm, and with [my] fury poured out.
Zan fitar da ku daga al’ummai in tattara ku daga ƙasashe inda aka warwatsa ku, da hannu mai iko da kuma hannu mai ƙarfi da kuma fushi.
35 And I will bring you into the wilderness of the people, and I will hold judgment over you there, face to face.
Zan kawo ku cikin hamadar al’ummai a can kuwa, fuska da fuska, zan hukunta ku.
36 As I held judgment over your fathers in the wilderness of the land of Egypt, so will I hold judgment over you, saith the Lord Eternal.
Yadda na hukunta kakanninku a hamadar ƙasar Masar, haka zan hukunta ku, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.
37 And I will cause you to pass under the rod, and I will bring you into the bond of the covenant;
Zan lura da ku yayinda kuke wucewa ƙarƙashin sanda, zan kuma kawo ku cikin daurin alkawari.
38 And I will separate from you those that have rebelled, and those that have transgressed against me: out of the country where they sojourn will I cause them to go forth, but into the land of Israel shall not one [of them] enter; and ye shall know that I am the Lord.
Zan fitar da waɗanda suke mini tayarwa da kuma’yan tawaye. Ko da yake zan fitar da su daga ƙasar da suke zama, duk da haka ba za su shiga ƙasar Isra’ila ba. Sa’an nan za ku san cewa ni ne Ubangiji.
39 As for you, O house of Israel, thus hath said the Lord Eternal, Go ye, serve ye every one his idols, and hereafter [also], if ye will not hearken unto me; but my holy name do not profane any more with your gifts, and with your idols.
“‘Game da ku, ya gidan Isra’ila, ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa ku tafi ku bauta wa gumakanku, kowannenku! Amma daga baya tabbatacce za ku saurare ni ba kuwa za ku ƙara ɓata sunana mai tsarki da hadayunku da gumakanku ba.
40 For on my holy mountain, on the mountain of the height of Israel, saith the Lord Eternal, there shall serve me all the house of Israel, altogether, in the land: there will I accept them in favor, and there will I require your heave-offerings, and the first-fruits of your oblations, with all your holy things.
Gama a kan dutsena mai tsarki, dutse mai tsayi na Isra’ila, in ji Ubangiji Mai Iko Duka, a can a ƙasar gidan Isra’ila gaba ɗaya za su bauta mini, a can kuwa zan karɓe su. A can zan bukaci hadayunku da sadake sadakenku mafi kyau, tare da dukan tsarkakan hadayunku.
41 With your sweet savor will I accept you in favor, when I bring you out from the people, and gather you out of the countries wherein ye have been scattered: and I will be sanctified through you before the eyes of the nations.
Zan karɓe ku kamar turare mai ƙanshi sa’ad da na fitar da ku daga al’ummai na kuma tattara ku daga ƙasashe inda aka warwatsa ku, zan kuma nuna kaina mai tsarki a cikinku a idon al’ummai.
42 And ye shall know that I am the Lord, when I bring you into the land of Israel, into the country for which I have lifted up my hand to give it to your fathers.
Sa’an nan za ku san cewa ni ne Ubangiji sa’ad da na kawo ku cikin ƙasar Isra’ila, ƙasar da na ɗaga hannu na rantse zan ba wa kakanninku.
43 And ye shall remember there your ways, and all your doings, whereby ye have been defiled; and ye shall loathe yourselves, because of all your evil deeds that ye have committed.
A can za ku tuna da halinku da kuma dukan ayyukanku waɗanda kuka ɓata kanku da su, za ku kuwa ji ƙyamar kanku saboda mugayen abubuwan da kuka aikata.
44 And ye shall know that I am the Lord, when I deal with you for the sake of my name, not in accordance with your wicked ways, and in accordance with your corrupt doings, O ye house of Israel, saith the Lord Eternal.
Za ku san cewa ni ne Ubangiji, sa’ad da na yi muku haka saboda sunana ba bisa ga mugayen hanyoyinku da ayyukanku marasa kyau ba, ya gidan Isra’ila, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.’”
45 And the word of the Lord came unto me, saying,
Maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
46 Son of man, set thy face in the direction toward the south, and preach toward the south, and prophesy against the forest of the field in the south.
“Ɗan mutum, ka kafa fuskarka wajen kudu; ka yi wa’azi a kan kudu ka kuma yi annabci a kan kurmin ƙasar kudu.
47 And say to the forest of the south, Hear the word of the Lord, Thus hath said the Lord Eternal, Behold, I will kindle a fire in thee, and it shall devour in thee every green tree, and every dry tree: the glowing flame shall not be quenched, and there shall be burnt therein all faces from the south to the north.
Ka faɗa wa kurmin kudanci, ‘Ji maganar Ubangiji. Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa ina gab da sa maka wuta, za tă kuwa cinye dukan itatuwanki sarai, da ɗanye da busasshe. Ba za a kashe wutar da take ci ba, kuma kowace fuska a kudu zuwa arewa za tă ƙone.
48 And all flesh shall see that I the Lord have kindled it: it shall not be quenched.
Kowa zai san cewa Ni Ubangiji ne ya ƙuna ta; ba za a kashe ta ba.’”
49 Then said I, Ah Lord Eternal! they say of me, Behold, he speaketh but in parables!
Sai na ce, “Kash, Ubangiji Mai Iko Duka! Suna zance a kaina cewa, ‘Ba misalai kawai yake yi ba?’”

< Ezekiel 20 >