< Ezekiel 14 >

1 Then came there unto me certain men of the elders of Israel, and sat down before me.
Waɗansu dattawan Isra’ila suka zo wurina suka zauna a ƙasa a gabana.
2 And the word of the Lord came unto me, saying,
Sai maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
3 Son of man, these men have set up their idols in their heart, and the stumbling-block of their iniquity have they placed before their faces: shall I in any wise let myself be inquired of by them?
“Ɗan mutum, waɗannan mutane sun kafa gumaka a cikin zukatansu suka sa mugayen abubuwan sa tuntuɓe a gabansu. Zan bar su, su taɓa nemi ni?
4 Therefore speak with them and say unto them, Thus hath said the Lord Eternal, Whatever man it be of the house of Israel that setteth up his idols in his heart, and layeth the stumbling-block of his iniquity before his face, and cometh to the prophet: I the Lord will answer him, although he cometh with the multitude of his idols;
Saboda haka ka yi musu magana ka faɗa musu cewa, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa sa’ad da wani mutumin Isra’ila ya kafa gumaka a cikin zuciyarsa ya kuma sa mugun abin tuntuɓe a gabansa sa’an nan ya tafi wurin annabi, Ni Ubangiji zan amsa masa da kaina game da babban bautar gumakarsa.
5 In order that I may grasp the house of Israel by their heart, those who are separated from me through all their idols.
Zan yi haka don in sāke ƙame zukatan mutanen Isra’ila, waɗanda duk suka yashe ni don gumakansu.’
6 Therefore say unto the house of Israel, Thus hath said the Lord Eternal, Return, and cause [your heart] to turn away from your idols: and from all your abominations turn away your faces.
“Saboda haka ka faɗa wa gidan Isra’ila cewa, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa ku tuba! Ku juyo daga gumakanku ku kuma furta dukan ayyukanku masu banƙyama!
7 For whatever man it be of the house of Israel, or of the stranger that sojourneth in Israel, that separateth himself from me, and setteth up his idols in his heart, and layeth the stumbling-block of his iniquity before his face, and then cometh to the prophet to inquire through him of me: I the Lord will answer him through my word;
“‘Duk sa’ad da mutumin Isra’ila ko baƙo mai zama a Isra’ila ya rabu da ni ya kuma kafa gumaka a cikin zuciyarsa ya kuna sa mugun abin tuntuɓe a gabansa sa’an nan ya tafi wurin annabi don yă neme ni, Ni Ubangiji zan amsa masa da kaina.
8 And I will set my face against that man, and will make him an astonishment for a sign and for proverbs, and I will cut him off from the midst of my people; and ye shall know that I am the Lord.
Zan yi gāba da mutumin in kuma sa ya zama misali da kuma abin karin magana. Zan ware shi daga mutanena. Sa’an nan za ku san cewa ni ne Ubangiji.
9 And when the prophet suffereth himself to be deceived, and he speaketh a word: I the Lord have suffered that prophet to be deceived: and I will stretch out my hand against him, and will destroy him from the midst of my people Israel.
“‘In kuma aka ruɗi annabin har ya yi annabci, Ni Ubangiji na rinjayi wannan annabi, zan kuma miƙa hannuna gāba da shi in hallaka shi daga cikin mutanena Isra’ila.
10 And they shall bear their guilt: as the guilt of the inquirer is, so shall the guilt of the prophet be;
Za su ɗauki hakkin laifinsu annabin zai zama mai laifi daidai da wanda ya zo neman shawararsa.
11 In order that the house of Israel may go no more astray by not following me, and not pollute themselves any more with all their transgressions; but that they may become unto me a people, and I may be unto them a God, saith the Lord Eternal.
Sa’an nan mutanen Isra’ila ba za su ƙara kauce daga gare ni ba, ba kuwa za su ƙara ƙazantar da kansu da dukan zunubansu ba. Za su zama mutanena, ni kuma zan zama Allahnsu, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.’”
12 And the word of the Lord came unto me, saying,
Maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
13 Son of man, if a land should sin against me by trespassing grievously, and I stretch out my hand against it, and break unto it the staff of bread, and send out famine against it, and cut off from it man and beast;
“Ɗan mutum, in wata ƙasa ta yi mini zunubi ta wurin rashin aminci na kuma miƙa hannuna gāba da ita don in toshe hanyar samun abincinta na kuma aika da yunwa a kanta na kashe mutanenta da dabbobinta,
14 And if there be these three men, Noah, Daniel, and Job, in the midst of it: these through their righteousness should save but their own soul; saith the Lord Eternal.
ko da waɗannan mutum uku Nuhu, Daniyel da kuma Ayuba suna a cikinta, za su iya ceton kansu ne kawai ta wurin adalcinsu, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.
15 If I cause wild beasts to pass through the land, and they depopulate it, and it becometh desolate, without any one to pass through because of the beasts:
“Ko kuwa in na aika da namun jeji su ratsa cikin wannan ƙasa suka kuma bar ta babu yaro, ta kuma zama kufai har babu wanda zai ratsa cikinta saboda namun jeji,
16 These three men [if they were] in it, as I live, saith the Lord Eternal, should not save either sons or daughters: they only should be saved, but the land should be made desolate.
muddin ina raye, in ji Ubangiji Mai Iko Duka, ko da ma waɗannan mutum uku suna a cikinta, ba za su iya ceton’ya’yansu maza ko mata ba. Su kaɗai za a iya ceto, amma ƙasar za tă zama kufai.
17 Or, if I should bring a sword over that land, and say, The sword shall pass through the land, and I cut off from it man and beast;
“Ko kuma in na kawo takobi a kan wannan ƙasa na kuma ce, ‘Bari takobin ya ratsa cikin dukan ƙasar,’ na kuma kashe mutanenta da dabbobinsu,
18 And if these three men should be in it: as I live, saith the Lord Eternal, they should not save either sons or daughters, but they alone should be saved.
muddin ina raye, in ji Ubangiji Mai Iko Duka, ko da waɗannan mutum uku suna cikinta, ba za su iya ceton’ya’yansu maza ko mata ba. Su kaɗai za a iya ceto.
19 Or, if I should send out the pestilence against that land, and pour out my fury over it in blood, to cut off from it man and beast;
“Ko kuma in na aika da annoba a cikin wannan ƙasa na kuma yi fushi a kanta ta wurin kisa, ina kisan mutanenta da dabbobinsu,
20 And if Noah, Daniel, and Job, should be in the midst of it: as I live, saith the Lord Eternal, they should not save either son or daughter; they through their righteousness should save their own soul.
muddin ina raye, in ji Ubangiji Mai Iko Duka, ko da Nuhu, Daniyel da Ayuba suna a cikinta, ba za su iya ceton ɗansu ko’yarsu ba. Za su iya ceton kansu ne kaɗai ta wurin adalcinsu.
21 For thus hath said the Lord Eternal, Although I send my four dreadful means of punishment over Jerusalem, the sword, and the famine, and the wild beasts, and the pestilence, to cut off from it man and beast:
“Gama ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa balle fa sa’ad da na aika wa Urushalima da hukuntaina guda huɗu masu zafi takobi da yunwa da namun jeji da annoba don su kashe mutanenta da dabbobinsu!
22 Still, behold, there are left therein some that escape who shall be carried forth, both sons and daughters; behold, they are coming forth unto you, and ye will see their way and their doings; and then will ye be comforted concerning the evil that I have brought upon Jerusalem, yea, concerning all that I have brought upon it;
Duk da haka za a sami mutanen da za su ragu’ya’ya maza da matan da za a fitar daga cikinta. Za su zo wurinka, kuma sa’ad da ka gan halinsu da ayyukansu, za ka ta’azantu game da bala’in da na kawo a kan Urushalima kowane bala’in da na kawo a kanta.
23 And they will comfort you, when ye see their way and their doings; and ye shall know that I have not done without cause all that I have executed in it, saith the Lord Eternal.
Za ka ta’azantu sa’ad da ka ga halinsu da kuma ayyukansu, gama za ka san cewa ban aikata wani abu a cikinta ba dalili ba, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.”

< Ezekiel 14 >