< Ezekiel 10 >

1 Then I saw, and, behold, on the vault that was above the head of the cherubim, there appeared over them something like a sapphire stone, something similar in appearance to the likeness of a throne.
Na duba, sai na ga kamannin kursiyin saffaya a kan sararin da yake a bisa kawunan kerubobi.
2 And he said unto the man clothed in linen, and said, Go in between the wheels, under the cherub, and fill thy hands with coals of fire from between the cherubim, and throw [them] over the city. And he went in before my eyes.
Sai Ubangiji ya ce wa mutumin da yake saye da lilin, “Ka shiga cikin da’irorin da suke ƙarƙashin kerubobi. Ka cika hannuwanka da garwashin wuta wanda yake tsakanin kerubobin ka kuma watsar da su a kan birnin.” Yayinda nake dubawa, sai ya shiga.
3 Now the cherubim were standing on the right side of the house, when the man went in: and the cloud filled the inner court.
Kerubobin kuwa suna tsaye a gefen kudu na haikali sa’ad da mutumin ya shiga, sai girgije ya cika filin da yake can ciki.
4 Then the glory of the Lord rose upward from the cherub, toward the threshold of the house: and the house was filled with the cloud, and the court was full of the brightness of the Lord's glory.
Sai ɗaukakar Ubangiji ya tashi daga bisa kerubobi ya tafi zuwa madogarar ƙofar haikali. Girgijen ya cika haikali, filin kuwa ya cika da hasken ɗaukakar Ubangiji.
5 And the sound of the wings of the cherubim was heard as far as the outer court, like the voice of the Almighty God when he speaketh.
Sai aka ji ƙarar fikafikan kerubobin har a filin waje, kamar muryar Allah Maɗaukaki sa’ad da ya yi magana.
6 And it came to pass, when he commanded the man clothed in linen, saying, Take fire from between the wheels, from between the cherubim, that he went in, and stood beside the wheel.
Sa’ad da Ubangiji ya umarci mutumin da yake saye da lilin cewa, “Ka ɗibi wuta daga cikin tsakanin da’irorin, daga tsakanin kerubobin,” sai mutumin ya shiga ya tsaya kusa da da’irar.
7 And the one cherub stretched forth his hand from between the cherubim unto the fire that was between the cherubim, and lifted it up, and placed it into the hands of the one clothed in linen; who took it, and went out.
Sa’an nan ɗaya daga cikin kerubobin ya miƙa hannu zuwa wurin wutar da take tsakaninsu. Ya ɗebo wutar daga ciki ya zuba a hannuwan mutumin da yake saye da lilin, shi kuwa ya karɓa ya fita.
8 And there became visible on the cherubim the form of a man's hand beneath their wings.
(A ƙarƙashin fikafikan kerubobin ana iya ganin abin da ya yi kamar hannuwan mutum.)
9 And I saw, and, behold, there were four wheels by the cherubim, one wheel by the one cherub, and another wheel by the other cherub: and the appearance of the wheels was like the glitter of a chrysolite stone.
Na duba, sai na ga kusa da kerubobin akwai da’irori huɗu, kowanne kusa da kerub guda; da’irorin suna ƙyalli kamar wani dutse mai daraja.
10 And as for their appearances, the whole four had one likeness, as if a wheel were in the midst of another wheel.
Game da kamanninsu kuwa, huɗu a cikinsu sun yi kama da juna; kowanne ya yi kamar da da’ira a cikin da’ira.
11 In their going, they went toward their four sides, they turned not round in their going; but to the place whither the head was turned they followed it, they turned not round in their going.
Yayinda suke tafiya, sukan tafi kowane gefe huɗun da kerubobin suka nufa; da’irorin ba sa juyawa yayinda kerubobin suke tafiya. Kerubobin suka tafi kowane gefen da kan ya nufa, ba tare da juyawa ba sa’ad da suke tafiya.
12 And their whole body, and their back, and their hands, and their wings, as also the wheels, were full of eyes round about, [even] the wheels that belonged to all four of them.
Jikunansu gaba ɗaya, har da bayansu, hannuwansu da fikafikansu, sun cika gaba ɗaya da idanu, kamar yadda suke a da’irori huɗun.
13 As for the wheels, they were called Galgal before my ears.
Na ji ana kiran da’irorin “da’irorin guguwa.”
14 And every one had four faces: the one face was the face of a cherub, and the second face was the face of a man, and the third face was the face of a lion, and the fourth the face of an eagle.
Kowane daga kerubobin yana da fuskoki huɗu. Fuska ɗaya na kerub ne, na biyun fuskar mutum ne, na ukun fuskar zaki ne, na huɗun kuwa fuskar gaggafa ce.
15 And the cherubim lifted themselves up. This is the living creature that I saw by the river Kebar.
Sai kerubobin suka tashi sama. Waɗannan ne halittu masu ran da na gani kusa da Kogin Kebar.
16 And when the cherubim went forward, the wheels went close by them; and when the cherubim lifted up their wings to mount up from the earth, the wheels also did not turn away from beside them.
Sa’ad da kerubobin suka motsa, sai da’irorin da suke kusa da su su motsa; kuma sa’ad da kerubobin suka buɗe fikafikansu don su tashi daga ƙasa, da’irorin ba sa barin wurarensu.
17 When those halted, these halted; and when those lifted themselves up, these lifted themselves up with them; for the spirit of the living creature was in them.
Sa’ad da kerubobin suka tsaya cik, su ma sukan tsaya cik; kuma sa’ad da kerubobin suka tashi, sai su ma su tashi tare da su, domin ruhun rayayyun halittun yana a cikinsu.
18 And the glory of the Lord went forth from off the threshold of the house, and halted over the cherubim.
Sai ɗaukakar Ubangiji ya tashi daga bisa madogarar ƙofar haikali ya kuma tsaya a bisa kerubobi.
19 And the cherubim lifted up their wings, and mounted up from the earth before my eyes as they went forth, and the wheels at the same time with them, and halted at the entrance of the east gate of the house of the Lord: and the glory of the God of Israel was over them above.
Yayinda nake duba, kerubobin suka buɗe fikafikansu suka kuma tashi daga ƙasa, yayinda suka tafi kuwa, da’irorin suka tafi tare da su. Suka tsaya a mashigin ƙofar gabas na gidan Ubangiji, ɗaukakar Allah na Isra’ila kuwa yana a kansu.
20 This is the living creature that I saw under the God of Israel by the river Kebar; and I understood that they were cherubim.
Waɗannan ne rayayyun halittun da na gani a ƙarƙashin Allah na Isra’ila kusa da Kogin Kebar, na kuma gane cewa su kerubobi ne.
21 Every one had four faces apiece, and every one had four wings; and the likeness of the hands of a man was under their wings.
Kowanne yana da fuskoki huɗu da fikafikai huɗu, a ƙarƙashin kuwa akwai wani abin da ya yi kamar hannuwan mutum.
22 And the likeness of their faces was the same as the faces which I had seen by the river Kebar, their appearances and themselves: they went every one in the direction of his face.
Fuskokinsu suna da kamanni ɗaya da waɗanda na gani kusa da Kogin Kebar. Kowanne ya tafi kai tsaye sosai.

< Ezekiel 10 >