< Exodus 9 >

1 And the Lord said unto Moses, Go in unto Pharaoh, and speak to him, Thus hath said the Eternal, the God of the Hebrews, Let my people go, that they may serve me.
Sai Ubangiji ya ce wa Musa, “Ka je wurin Fir’auna ka ce masa, ‘Ga abin da Ubangiji Allah na Ibraniyawa ya ce, “Ka bar mutanena su tafi, domin su yi mini sujada.”
2 For if thou refusest to let them go, and still holdest on to them,
In ka ƙi ka bar su su tafi, kana ta riƙonsu,
3 Behold, the hand of the Lord will be sent against thy cattle which is in the field, against the horses, against the asses, against the camels, against the oxen, and against the sheep; —a very grievous pestilence.
hannun Ubangiji zai kawo muguwar annoba a kan dabbobinka a gona, a kan dawakanka, da jakuna da raƙuma, da kuma a kan shanunka da tumaki da awaki.
4 And the Lord will distinguish between the cattle of Israel and the cattle of Egypt; and not one head shall die of all that belongeth to the children of Israel.
Amma Ubangiji zai raba tsakanin dabbobin Isra’ila da na Masar, saboda kada wata dabbar Isra’ilawa ta mutu.’”
5 And the Lord appointed a set time, saying, Tomorrow will the Lord do this thing in the land.
Sai Ubangiji ya sa lokaci ya ce, “Gobe Ubangiji zai yi wannan a ƙasar.”
6 And the Lord did this thing on the morrow, and all the cattle of Egypt died; but of the cattle of the children of Israel there died not one.
Kashegari Ubangiji ya yi haka. Dukan dabbobin Masarawa suka mutu, amma babu dabba guda ta Isra’ilawan da ta mutu.
7 And Pharaoh sent, and, behold, there had not died of the cattle of the Israelites even one; but the heart of Pharaoh remained hardened, and he did not let the people go.
Fir’auna ya aiki mutane su bincika, sai suka tarar babu dabba guda ta Isra’ilawan da ta mutu. Duk da haka zuciyar Fir’auna ta taurare, bai kuwa bar mutanen su tafi ba.
8 And the Lord said unto Moses and unto Aaron, Take unto yourselves your hands full of soot of the furnace, and let Moses throw it heavenward before the eyes of Pharaoh.
Sa’an nan Ubangiji ya ce wa Musa da Haruna, “Ɗibi tokar matoya cike da tafin hannuwanku, Musa kuwa zai watsa tokar sama a gaban Fir’auna.
9 And it shall become small dust over all the land of Egypt, and shall become upon man and beast an inflammation, producing boils, throughout all the land of Egypt.
Za tă zama ƙura bisa dukan ƙasar Masar, sai marurai masu zafi su fiffito bisa mutane da dabbobi a dukan ƙasar.”
10 And they took the soot of the furnace, and stood before Pharaoh; and Moses threw it up heavenward; and it became an inflammation, producing boils, upon man, and upon beast.
Sai suka ɗibi tokar matoya, suka tsaya a gaban Fir’auna, Musa ya watsa ta a iska, sai marurai masu zafi suka fiffito bisa mutane da dabbobi.
11 And the magicians could not stand before Moses because of the inflammation; for the inflammation was upon the magicians, and upon all the Egyptians.
Bokaye suka kāsa tsayawa a gaban Musa saboda maruran da suke bisansu da a kan dukan Masarawa.
12 And the Lord hardened the heart of Pharaoh, and he hearkened not unto them; as the Lord had spoken unto Moses.
Amma Ubangiji ya taurare zuciyar Fir’auna, bai kuwa saurare Musa da Haruna ba kamar yadda Ubangiji ya riga ya ce wa Musa.
13 And the Lord said unto Moses, Rise up early in the morning, and place thyself before Pharaoh, and say unto him, Thus hath said the Eternal, the God of the Hebrews, Let my people go, that they may serve me.
Sa’an nan Ubangiji ya ce wa Musa, “Tashi da sassafe, ka sadu da Fir’auna, ka ce masa, ‘Ga abin da Ubangiji, Allah na Ibraniyawa ya ce, Ka bar mutanena su tafi don su yi mini sujada,
14 For at this time I send all my plagues against thy heart, and against thy servants, and against thy people; in order that thou mayest know that there is none like me on all the earth.
ko kuwa a wannan lokaci zan aika da cikakkiyar annoba mai ƙarfi a kanka da a kan fadawanka da mutanenka, domin ka san cewa ba kama da ni a dukan duniya.
15 For even now I might have stretched out my hand, and I might have smitten thee and thy people with the pestilence; and thou wouldst have been cut off from the earth;
Gama da ni kaina na miƙa hannuna na buge ka da jama’arka da annoba, ai, da an hallaka ku a duniya ƙaƙaf.
16 But for this cause have I allowed thee to remain, in order to show thee my power; and in order that they may proclaim my name throughout all the earth.
Amma na bar ka ka rayu domin in nuna maka ikona, domin kuma sunana yă zama abin darajantawa a dukan duniya.
17 If thou dost yet wantonly oppress my people, so as not to let them go:
Har yanzu kana gāba da mutanena, ba ka kuma bar su su tafi ba.
18 Behold, then will I let rain, about this time tomorrow, a very grievous hail, the like of which hath not been in Egypt since the day of its foundation even until now.
Saboda haka, gobe war haka, zan sa a yi ƙanƙara mai tsananin gaske, irin wadda Masar ba tă taɓa gani ba tun kahuwarta, har yă zuwa yanzu.
19 And now send, and bring under shelter thy cattle, and all that thou hast in the field; [for] every man and beast that shall be found in the field, and shall not be brought into the house, upon them shall the hail come down, and they shall die.
Yanzu, ka ba da umarni a dawo da shanunku da kuma kome da kuke da shi wanda yake a gona zuwa gida, gama ƙanƙarar za tă kashe kowane mutum ko dabba wadda take a gona wadda ba a kawo cikin gida ba, sa’ad da ta fāɗo.’”
20 He that feared the word of the Lord among the servants of Pharaoh made his servants and his cattle flee into the houses;
Waɗansu daga cikin dattawan Fir’auna suka cika da tsoro saboda abin da Ubangiji ya faɗa, nan da nan suka shigo da dabbobinsu da bayinsu da sauri daga gona zuwa cikin gida.
21 And he that regarded not the word of the Lord left his servants and his cattle in the field.
Amma waɗanda ba su kula da maganar Ubangiji ba, suka bar bayinsu da dabbobi a gona.
22 And the Lord said unto Moses, Stretch forth thy hand toward heaven, and there shall be hail in all the land of Egypt, upon man, and upon beast, and upon every herb of the field, in the land of Egypt.
Sa’an nan Ubangiji ya ce wa Musa, “Miƙa hannunka sama don a yi ƙanƙara a bisa dukan Masar, a bisa mutane da dabbobi, da bisa dukan abubuwan da suke girma a gonakin Masar.”
23 And Moses stretched forth his staff toward heaven; and the Lord sent thunder and hail, and the fire ran down to the ground; and the Lord rained hail upon the land of Egypt.
Da Musa ya miƙa sandansa sama, sai Ubangiji ya aiko da tsawa da ƙanƙara, da walƙiya har ƙasa. Ta haka Ubangiji ya yi ruwan ƙanƙara a bisa ƙasar Masar;
24 And there was hail, and fire was flaming up amidst the hail, very grievous, the like of which had not been in all the land of Egypt, since it had become a nation.
ƙanƙara ta fāɗo, walƙiya kuma tana ta wulƙawa. Wannan ce ƙanƙara mafi munin da aka taɓa yi, a dukan ƙasar Masar, tun tarihin kahuwarta na zaman al’umma.
25 And the hail smote throughout all the land of Egypt all that was in the field, both man and beast; and every herb of the field did the hail smite, and every tree of the field did it break.
Ko’ina a Masar ƙanƙara ta bugi duk abin da yake a gonaki, mutane da dabbobi, ta bugi duk ganyaye da suke a gonaki, ta kuma ragargaza kowane itace.
26 Only in the land of Goshen, where the children of Israel were, there was no hail.
Wuri guda kaɗai da ba a yi ruwan ƙanƙara ba, shi ne yankin Goshen, inda Isra’ilawa suke.
27 And Pharaoh sent, and called for Moses and Aaron, and he said unto them, I have sinned this time; the Eternal is the righteous, and I and my people are the wicked.
Sai Fir’auna ya aika a kira Musa da Haruna. Ya ce musu, “A wannan karo na yi zunubi. Ubangiji, shi ne da gaskiya, ni da mutane mu ke da kuskure.
28 Entreat the Lord that there may be no more of the thunders of God, and hail; and I will let you go, and ye shall no longer stay here.
Ku roƙi Ubangiji, yă tsai da tsawar da ƙanƙarar. Ni kuwa na yi alkawari zan bar ku ku tafi, ba za ku ƙara tsayawa a nan ba.”
29 And Moses said unto him, As soon as I am gone out of the city, I will spread out my hands unto the Lord: the thunders shall cease, and the hail shall not be any more; in order that thou mayest know how that to the Lord belongeth the earth.
Musa ya amsa, “To, da kyau, da zarar na fita daga birnin, zan yi addu’a ga Ubangiji, tsawar za tă tsaya, ƙanƙarar kuma za tă daina, don ku sani cewa duniya ta Ubangiji ce.
30 But as for thee and thy servants, I know that ye are not yet afraid before the Lord God.
Amma na san cewa kai da fadawanka, har wa yau ba ku ji tsoron Ubangiji Allah ba tukuna.”
31 And the flax and the barley were smitten; for the barley was in the ear, and the flax was bolled.
(Rama da sha’ir suka lalace, gama sha’ir ya riga ya nuna, rama kuwa tana fid da kai.
32 But the wheat and the millet were not smitten; for they are late-ripening.
Alkama da gero kam, ba a hallaka su ba, gama lokacin nunansu bai yi ba tukuna.)
33 And Moses went away from Pharaoh out of the city, and spread out his hands unto the Lord: and the thunders and hail ceased, and the rain was not poured out upon the earth.
Sai Musa ya tashi daga gaban Fir’auna, ya fita daga birni. Da ya miƙa hannuwansa ta wajen Ubangiji, sai tsawa da ƙanƙara suka tsaya, kwararowar ruwa kuma ta ɗauke.
34 And when Pharaoh saw that the rain, and the hail, and the thunders had ceased, he sinned yet farther, and hardened his heart, he and his servants.
Da Fir’auna ya ga cewa ruwa da ƙanƙara da tsawa sun daina, sai ya sāke yin zunubi. Shi da fadawansa, suka taurare zukatansu.
35 And the heart of Pharaoh remained hardened, and he did not let the children of Israel go; as the Lord had spoken by the hand of Moses.
Ta haka zuciyar Fir’auna ta taurare, bai kuwa bar Isra’ilawa suka tafi ba, kamar yadda Ubangiji ya riga ya faɗa ta wurin Musa.

< Exodus 9 >