< Exodus 7 >

1 And the Lord said unto Moses, See, I have made thee a god to Pharaoh; and Aaron thy brother shall be thy prophet.
Sai Ubangiji ya ce wa Musa, “Duba, na maishe ka kamar Allah ga Fir’auna, ɗan’uwanka Haruna kuma zai zama annabinka.
2 Thou shalt speak all that I shall command thee; and Aaron thy brother shall speak unto Pharaoh, that he send away the children of Israel out of his land.
Za ka faɗi kome da na umarce ka, ɗan’uwanka Haruna kuwa zai faɗa wa Fir’auna, yă bar Isra’ilawa su fita daga ƙasarsa.
3 And I will harden the heart of Pharaoh, and I will multiply my signs and my wonders in the land of Egypt.
Amma zan taurare zuciyar Fir’auna, kuma ko da na ninka mu’ujizai da kuma alamu a Masar,
4 And Pharaoh will not hearken unto you, and I will lay my hand upon Egypt, and bring forth my armies, my people, the children of Israel, out of the land of Egypt by means of great judgments.
ba zai saurare ku ba. Don haka zan miƙa hannuna a kan Masar, in murƙushe ta da bala’i iri-iri, bayan haka zan fitar da taron mutanen Isra’ila daga ƙasar Masar ta wurin hukuntaina masu girma.
5 And the Egyptians shall know that I am the Lord, when I stretch forth my hand over Egypt, and bring out the children of Israel from the midst of them.
Masarawa kuwa za su san cewa ni ne Ubangiji sa’ad da na miƙa hannuna a kan Masar, na kuma fitar da Isra’ilawa daga gare ta.”
6 And Moses and Aaron did so; as the Lord commanded them, so did they.
Musa da Haruna suka aikata yadda Ubangiji ya umarce su.
7 And Moses was eighty years old, and Aaron eighty and three years old, when they spoke unto Pharaoh.
Musa yana da shekara tamanin da haihuwa, Haruna kuma yana da shekara tamanin da uku, sa’ad da suka yi magana da Fir’auna.
8 And the Lord said unto Moses and unto Aaron, saying,
Ubangiji ya ce wa Musa da Haruna,
9 If Pharaoh shall speak unto you, saying, Show a miracle for yourselves: then shalt thou say unto Aaron, Take thy staff and cast it down before Pharaoh; it shall become a serpent.
“Sa’ad da Fir’auna ya ce muku, ‘Aikata wani al’ajabi,’ sai ka ce wa Haruna, ‘Ɗauki sandanka ka jefa shi a ƙasa, a gaban Fir’auna,’ zai kuwa zama maciji.”
10 And Moses and Aaron went in unto Pharaoh, and they did so, as the Lord had commanded; and Aaron cast down his staff before Pharaoh, and before his servants, and it became a serpent.
Sai Musa da Haruna suka tafi wurin Fir’auna, suka yi yadda Ubangiji ya umarce su. Haruna ya jefa sandansa ƙasa, a gaban Fir’auna da bayinsa, sai sandan ya zama maciji.
11 Then Pharaoh also called for the wise men and the sorcerers; and they also, the magicians of Egypt, did with their secret arts in like manner.
Fir’auna kuwa ya kira masu hikima da masu sihiri, sai bokayen Masarawa ma suka yi irin abubuwan nan da bokancinsu.
12 And they cast down every man his staff, and they became serpents; but Aaron's staff swallowed up their staves.
Kowannensu ya jefa sandansa ƙasa, ya kuwa zama maciji. Amma sandan Haruna ya haɗiye sandunansu.
13 But the heart of Pharaoh was hard, and he hearkened not unto them; as the Lord had spoken.
Duk da haka zuciyar Fir’auna ta taurare, bai kuwa saurare su ba, kamar dai yadda Ubangiji ya riga ya faɗa.
14 And the Lord said unto Moses, The heart of Pharaoh is obdurate, he refuseth to let the people go.
Sa’an nan Ubangiji ya ce wa Musa, “Zuciyar Fir’auna taurariya ce, ya ƙi yă bar mutanen su tafi.
15 Get thee unto Pharaoh in the morning; lo, he goeth out unto the water; and thou shalt place thyself opposite to him by the brink of the river; and the staff which was turned to a serpent shalt thou take in thy hand.
Ka je wurin Fir’auna da safe, yayinda za shi kogi. Ka jira a bakin Nilu don ka sadu da shi, ka ɗauki sandan nan da ya canja zuwa maciji a hannunka.
16 And thou shalt say unto him, The Eternal, the God of the Hebrews, hath sent me unto thee, saying, Let my people go, that they may serve me in the wilderness: and, behold, thou wouldst not hear, up to this time.
Sa’an nan ka ce masa, ‘Ubangiji, Allah na Ibraniyawa, ya aiko ni in faɗa maka, Ka bar mutanena su tafi domin su yi mini sujada a hamada. Amma har yanzu ba ka yi biyayya ba.
17 Thus hath said the Lord, By this thou shalt know that I am the Lord: behold, I will smite with the staff that is in my hand upon the waters which are in the river, and they shall be turned to blood.
Ga abin da Ubangiji ya ce, da wannan za ka san cewa ni ne Ubangiji. Da sandan da yake hannuna zan bugi ruwan Nilu, zai kuma zama jini.
18 And the fish that is in the river shall die, and the river shall stink; and the Egyptians shall loath to drink water from the river.
Kifi a ciki Nilu za su mutu, ruwan kuma zai yi ɗoyi; Masarawa ba za su iya shan ruwansa ba.’”
19 And the Lord said unto Moses, Say unto Aaron, Take thy staff, and stretch out thy hand over the waters of Egypt, over their streams, over their rivers, and over their ponds, and over all their pools of water, that they become blood; and there shall be blood throughout all the land of Egypt, also in vessels of wood, and in vessels of stone.
Ubangiji ya ce wa Musa, “Ka ce wa Haruna, ‘Ka ɗauki sandanka, ka miƙa hannunka kan ruwan Masar, kan kogunansu da rafuffukansu da kududdufansu da kuma dukan tafkunansu, za su zama jini.’ Jini zai kasance ko’ina a Masar, har ma a cikin abubuwan ajiyar ruwansu da aka yi da itace da kuma dutse.”
20 And Moses and Aaron did so, as the Lord had commanded; and he lifted up [his hand] with the staff, and smote the waters that were in the river, before the eyes of Pharaoh, and before the eyes of his servants; and all the waters that were in the river were turned to blood.
Musa da Haruna suka yi yadda Ubangiji ya umarta. Ya ɗaga sandansa a gaban Fir’auna da bayinsa, ya bugi ruwan Nilu, dukan ruwan kuwa ya zama jini.
21 And the fish that was in the river died; and the river stank, and the Egyptians could not drink water from the river; and the blood was throughout all the land of Egypt.
Kifin da suke cikin Nilu suka mutu, kogin kuwa ya yi wari sosai yadda Masarawa ba su iya shan ruwan ba. Jini ya bazu ko’ina a Masar.
22 And the magicians of Egypt did so with their secret arts: and the heart of Pharaoh remained hardened, and he did not hearken unto them; as the Lord had spoken.
Amma bokayen Masar ma suka yi abubuwan nan da sihirinsu, sai zuciyar Fir’auna ta taurare; bai saurari Musa da Haruna ba, kamar dai yadda Ubangiji ya riga ya faɗa.
23 And Pharaoh turned away and went into his house, and he did not set his heart to this thing also.
A maimakon yă saurara, sai ya juya ya koma fadarsa, bai ma damu da abin da aka yi ba.
24 And all the Egyptians dug in the neighborhood of the river for water to drink; for they could not drink of the water of the river.
Sai dukan Masarawa suka yi ta tonon gefen Nilu don su sami ruwan sha, domin ba su iya shan ruwan kogin ba.
25 And full seven days elapsed, after that the Lord had smitten the river.
Kwana bakwai suka wuce bayan da Ubangiji ya bugi kogin.

< Exodus 7 >