< Exodus 40 >

1 And the Lord spoke unto Moses, saying,
Sa’an nan Ubangiji ya ce wa Musa,
2 On the first day of the first month shalt thou set up the tabernacle of the tent of the congregation.
“Ka kafa tabanakul, da Tentin Sujada, a kan rana ta fari ga watan fari.
3 And thou shalt put therein the ark of the testimony, and separate the ark with the vail.
Ka sa akwatin Alkawari a cikinsa, sa’an nan ka rufe shi da labule.
4 And thou shalt bring in the table, and arrange the order of the showbread upon it; and thou shalt bring in the candlestick, and light the lamps thereof.
Ka shigar da teburin ka shirya kayayyakin a kansa. Sa’an nan ka shigar da wurin ajiye fitilan ka kuma sa fitilunsa.
5 And thou shalt set the altar of gold for the incense before the ark of the testimony; and thou shalt put up the hanging at the door to the tabernacle.
Ka sa bagaden zinariya na ƙona turare a gaban akwatin Alkawari, ka kuma sa labule a ƙofar shiga tabanakul.
6 And thou shalt set the altar of burnt-offering before the door of the tabernacle of the tent of the congregation.
“Ka ajiye bagade na yin hadaya ta ƙonawa a gaban ƙofar tabanakul, da Tentin Sujada;
7 And thou shalt set the laver between the tabernacle of the congregation and the altar, and thou shalt put water therein.
ka ajiye daron tsakanin Tentin Sujada da bagaden, ka kuma zuba ruwa a cikinsa.
8 And thou shalt set up the court round about, and put up the hanging at the gate of the court.
Ka yi fili kewaye da shi, ka kuma sa labule a ƙofar shiga filin.
9 And thou shalt take the anointing oil, and anoint the tabernacle, and all that is therein; and thou shalt hallow it, with all its vessels, and it shall be holy.
“Ka ɗauki man shafewa ka shafe tabanakul da duka abin da yake cikinsa; ka keɓe shi da dukan kayayyakinsa, zai zama tsarkake.
10 And thou shalt anoint the altar of burnt-offering, and all its vessels; and thou shalt sanctify the altar, and the altar shall be most holy.
Sa’an nan ka shafe bagaden hadaya ta ƙonawa da kayansa; ka keɓe bagaden, zai zama mai tsarki.
11 And thou shalt anoint the laver with its foot, and sanctify it.
Ka shafe daron da wurin ajiyarsa, ka kuma keɓe su.
12 And thou shalt bring near Aaron and his sons unto the door of the tabernacle of the congregation, and wash them with water.
“Ka kawo Haruna da’ya’yansa a ƙofar Tentin Sujada ka wanke su da ruwa.
13 And thou shalt clothe Aaron with the holy garments; and thou shalt anoint him, and sanctify him, that he may be a priest unto me.
Sa’an nan ka sa wa Haruna tsarkakun riguna, ka shafe shi, ka kuma keɓe shi don yă yi mini hidima a matsayin firist.
14 And his sons shalt thou bring near, and clothe them with coats:
Ka kawo’ya’yansa maza ka sa musu taguwoyi.
15 And thou shalt anoint them, as thou hast anointed their father, that they may be priests unto me; and this shall be, that their anointing shall be unto them for an everlasting priesthood throughout their generations.
Ka shafe su yadda ka shafe mahaifinsu, don su yi mini hidima a matsayin firistoci. Shafe musu man, zai sa su zama firistoci na ɗinɗinɗin, dukan zamanansu.”
16 And Moses did so; all, just as the Lord had commanded him, so did he.
Musa ya aikata dukan kome yadda Ubangiji ya umarce shi.
17 And it came to pass in the first month in the second year, on the first of the month, that the tabernacle was reared up.
Da haka aka kafa tabanakul, a rana ta fari ga wata na fari a shekara ta biyu.
18 And Moses reared up the tabernacle, and placed its sockets, and set up its boards, and put in its bars, and reared up its pillars.
Sa’ad da Musa ya kafa tabanakul, ya sa rammuka a wurinsu, ya sa katakan, ya kuma sa sandunan, ya kakkafa dogayen sandunan.
19 And he spread the tent over the tabernacle, and put the covering of the tent over it above; as the Lord had commanded Moses.
Sa’an nan ya shimfiɗa tentin a bisa tabanakul, ya kuma sa murfi a bisa tentin, yadda Ubangiji ya umarce shi.
20 And he took and put the testimony into the ark, and placed the staves on the ark; and he put the mercy-seat upon the ark above.
Ya ɗauki dokokin Alkawari ya sa a cikin akwatin, ya kuma zura sandunan a zoban akwatin, sa’an nan ya sa murfin kafara a bisansa.
21 And he brought the ark into the tabernacle, and set up the vail of the separation, and made therewith a separation for the ark of the testimony; as the Lord had commanded Moses.
Sai ya kawo akwatin a cikin tabanakul, ya kuma rataye labulen rufewa ya tsare akwatin Alkawarin, yadda Ubangiji ya umarce shi.
22 And he put the table in the tabernacle of the congregation, upon the side of the tabernacle, northward, without the vail.
Musa ya sa teburin a Tentin Sujada, a gefen arewa na tabanakul waje da labulen.
23 And he arranged upon it the order of bread before the Lord; as the Lord had commanded Moses.
Ya shirya burodin a kai a gaban Ubangiji, yadda Ubangiji ya umarce shi.
24 And he placed the candlestick in the tabernacle of the congregation, opposite the table, on the side of the tabernacle, southward.
Ya sa wurin ajiye fitilan a Tentin Sujada ɗaura da teburin a gefen kudu na tabanakul
25 And he lighted the lamps before the Lord; as the Lord had commanded Moses.
ya kuma shirya fitilun a gaban Ubangiji, yadda Ubangiji ya umarce shi.
26 And he placed the golden altar in the tabernacle of the congregation before the vail.
Musa ya sa bagaden zinariya a cikin Tentin Sujada a gaban labulen
27 And he burnt thereon the incense of spices; as the Lord had commanded Moses.
ya ƙone turare mai ƙanshi a kai, yadda Ubangiji ya umarce shi.
28 And he put up the hanging at the door to the tabernacle.
Sa’an nan ya sa labule a ƙofar shiga na tabanakul.
29 And the altar of burnt-offering he placed by the door of the tabernacle of the tent of the congregation; and he offered upon it the burnt-offering and the meat-offering; as the Lord had commanded Moses.
Ya sa bagaden hadaya ta ƙonawa kusa da ƙofar tabanakul, Tentin Sujada, sa’an nan ya miƙa hadaya ta ƙonawa da hadaya ta gari a kansa, yadda Ubangiji ya umarce shi.
30 And he set the laver between the tabernacle of the congregation and the altar, and put water there, for washing.
Ya sa daro tsakanin Tentin Sujada da bagade, ya kuma zuba ruwa a cikinsa don wanki,
31 And Moses and Aaron and his sons washed therefrom their hands and their feet.
a cikin kuwa Musa da Haruna da’ya’yansa maza sukan wanke hannunsa da ƙafafunsu.
32 When they went in unto the tabernacle of the congregation, and when they came near unto the altar, they washed themselves; as the Lord had commanded Moses.
Sukan yi wanka a duk sa’ad da suka shiga Tentin Sujada, ko in suka kusaci bagade, yadda Ubangiji ya umarci Musa.
33 And he reared up the court round about the tabernacle and the altar, and put up the hanging of the gate of the court; and so did Moses finish the work.
Sa’an nan Musa ya yi fili kewaye da tabanakul da kuma bagaden, ya rataye labule a ƙofar shiga filin. Da haka Musa ya gama aikin.
34 And the cloud covered the tent of the congregation, and the glory of the Lord filled the tabernacle.
Sa’an nan girgije ya rufe Tentin Sujada sai ɗaukakar Ubangiji ta cika tabanakul.
35 And Moses was not able to enter into the tent of the congregation; because the cloud abode thereon, and the glory of the Lord filled the tabernacle.
Musa bai iya shiga Tentin Sujada ba domin girgije ya riga ya sauka a kansa, ɗaukakar Ubangiji kuwa ta cika tabanakul.
36 And when the cloud was taken up from over the tabernacle, the children of Israel were wont to go onward in all their journeyings.
Cikin tafiyar Isra’ilawa duka, sukan kama tafiyarsu ne a duk sa’ad da girgijen ya tashi daga kan tabanakul.
37 But if the cloud was not taken up, then they journeyed not till the day that is was taken up.
Idan girgijen bai tashi ba, ba za su tashi ba, sai a ranar da ya tashi.
38 For the cloud of the Lord was upon the tabernacle by day, and a fire was by night on it, before the eyes of all the house of Israel, throughout all their journeyings.
Gama a cikin tafiyarsu duka, girgijen Ubangiji yana kan tabanakul da rana, da dare kuwa wuta yake cikinsa domin dukan Isra’ilawa su gani.

< Exodus 40 >