< Exodus 4 >

1 And Moses answered and said, But, behold, they will not believe me, nor hearken unto my voice; for they will say, The Lord hath not appeared unto thee.
Musa ya amsa ya ce, “In ba su gaskata ni ba, suka kuma ce, ‘Ubangiji bai bayyana gare ka ba fa’?”
2 And the Lord said unto him, What is that in thy hand? and he said, A staff.
Sai Ubangiji ya ce, “Mene ne wannan a hannunka?” Musa ya amsa ya ce, “Sanda.”
3 And he said, Cast it on the ground; and he cast it on the ground, and it became a serpent; and Moses fled from before it.
Sai Ubangiji ya ce, “Jefa shi ƙasa.” Musa ya jefa shi ƙasa, sai sandan ya zama maciji, Musa kuwa ya gudu daga gare shi.
4 And the Lord said unto Moses, Put forth thy hand, and grasp it by the tail; and he put forth his hand, and laid hold of it, and it became a staff in his hand.
Sai Ubangiji ya ce masa, “Sa hannunka ka ɗauke shi ta wutsiya.” Sai Musa ya miƙa hannu, ya kama macijin, macijin kuwa ya dawo sanda a hannunsa.
5 In order that they may believe that there hath appeared unto thee the Everlasting One, the God of their fathers, the God of Abraham, the God of Isaac, and the God of Jacob.
Ubangiji ya ce, “Wannan zai sa su ba da gaskiya cewa Ubangiji, Allah na kakanninsu, Allah na Ibrahim, Allah na Ishaku, da kuma Allah da Yaƙub, ya bayyana gare ka.”
6 And the Lord said farthermore unto him, Do put thy hand into thy bosom: and he put his hand into his bosom; and when he took it out, behold, his hand was leprous, white as snow.
Sa’an nan Ubangiji ya ce, “Sa hannunka cikin rigarka.” Sai Musa ya sa hannunsa cikin rigarsa, sa’ad da ya fitar da shi, sai hannun ya a kuturce fari fat, kamar ƙanƙara.
7 And he said, Put thy hand again into thy bosom: and he put his hand again into his bosom; and when he pulled it out of his bosom, behold, it was turned again as his other flesh.
Sai Ubangiji ya ce, “Yanzu, mayar da hannunka a rigarka.” Sai Musa ya sa hannunsa cikin rigarsa, da ya fitar da shi, sai hannun ya koma kamar sauran jikinsa.
8 And it shall come to pass, if they will not believe thee, neither hearken to the voice of the first sign, that they will believe the voice of the latter sign.
Sa’an nan Ubangiji ya ce, “In ba su gaskata ba, ko kuma ba su kula da mu’ujiza ta fari ba, wataƙila su gaskata da ta biyun.
9 And it shall come to pass, if they will not believe also these two signs, and will not hearken unto thy voice, that thou shalt take of the water of the river, and pour it upon the dry land: and the water which thou shalt take out of the river shall become blood upon the dry land.
Amma in ba su gaskata mu’ujizan nan biyu ba, ko kuwa ba su saurare ka ba, sai ka ɗibo ruwa daga Nilu, ka zuba a busasshiyar ƙasa. Ruwan da ka ɗebo daga kogin zai zama jini a ƙasar.”
10 And Moses said unto the Lord, Pardon, O Lord, I am not a man of words, neither yesterday, nor the day before, nor since thou hast spoken unto thy servant; for I am heavy of speech, and heavy of tongue.
Musa ya ce wa Ubangiji, “Ya Ubangiji, ni ban mai iya magana ba ne, ban taɓa iya ba, ko a yanzu ma, bayan ka yi magana da ni, gama ni mai nauyin baki ne, mai nauyin harshe kuma.”
11 And the Lord said unto him, Who hath given a mouth to man? or who maketh him dumb, or deaf, or seeing, or blind? is it not I the Lord?
Ubangiji ya ce masa, “Wa ya ba mutum bakinsa? Wa yake maishe shi kurma ko bebe? Wa yake ba shi gani ko yă makanta shi? Ashe ba Ni Ubangiji ba ne?
12 Now therefore go, and I will be with thy mouth, and I will teach thee what thou shalt speak.
Yanzu tafi, zan taimake ka ka yi magana, zan kuma koya maka abin da za ka faɗa.”
13 And he said, Pardon, O Lord, send, I pray thee, by the hand of him whom thou wouldst send.
Amma Musa ya ce, “Ya Ubangiji, ina roƙonka, ka nemi wani ka aika.”
14 And the anger of the Lord was kindled against Moses, and he said, Is there not Aaron, thy brother, the Levite? I know that he can speak well; and also, behold, he cometh forth to meet thee; and when he seeth thee, he will be glad in his heart.
Sai Ubangiji ya yi fushi da Musa ya ce, “Ɗan’uwanka Haruna Balawe, ba ya nan ne? Na san ya iya magana. Ya riga ya kama hanya don yă sadu da kai, zai kuma yi farin ciki sa’ad da ya gan ka.
15 And thou shalt speak unto him, and put the words in his mouth: and I will be with thy mouth, and with his mouth, and I will teach you what ye shall do.
Za ka yi masa magana. Ka kuma sa masa maganata a baki; zan kuma taimake ku magana, in koya muku abin da za ku yi.
16 And he shall speak for thee unto the people; and he shall be, yea he shall be to thee as a mouth, and thou shalt be to him as a God.
Zai yi magana da mutane a madadinka, zai zama kamar bakinka, kai kuwa kamar Allah a gare shi.
17 And this staff shalt thou take in thy hand, wherewith thou shalt do the signs.
Amma ka ɗauki wannan sanda a hannunka domin yă aikata mu’ujizan.”
18 And Moses went and returned to Jether his father-in-law, and said unto him, Let me go, I pray thee, and return unto my brethren that are in Egypt, and see whether they be yet alive; and Jithro said to Moses, Go in peace.
Sai Musa ya koma wurin Yetro surukinsa, ya ce masa, “Bari in koma wurin mutanena a Masar, in ga ko da mai rai a cikinsu.” Yetro ya ce, “Tafi, ka kuma sauka lafiya.”
19 And the Lord said unto Moses in Midian, Go, return into Egypt; for all the men are dead who sought thy life.
Ubangiji ya riga ya gaya wa Musa a Midiyan, “Koma Masar, domin dukan mutanen da suke neman su kashe ka sun mutu.”
20 And Moses took his wife and his sons, and set them upon an ass, and he returned to the land of Egypt; and Moses took the staff of God in his hand.
Sai Musa ya ɗauki matarsa da’ya’yansa maza, ya sa su a kan jaki, suka kama hanya zuwa Masar. Ya kuma ɗauki sandan Allah a hannunsa.
21 And the Lord said unto Moses, When thou goest to return into Egypt, regard well all the wonders which I have put in thy hand, and do them before Pharaoh; but I will harden his heart, and he will not let the people go.
Ubangiji ya ce wa Musa, “Bayan ka koma Masar, ka tabbata ka aikata dukan mu’ujizan da na sa cikin ikonka a gaban Fir’auna. Amma zan taurare zuciyarsa domin kada yă bar mutanen su tafi.
22 And thou shalt say unto Pharaoh, Thus hath said the Lord, My son, my first-born, is Israel.
Sa’an nan ka gaya wa Fir’auna, ‘Ga abin da Ubangiji ya ce; Isra’ila shi ne ɗan farina,
23 And I said unto thee, Let my son go, that he may serve me; and thou refusest to let him go; so, behold, I will slay thy son, thy first-born.
na gaya maka, “Ka bar ɗana yă tafi domin yă yi mini sujada.” Amma ka ƙi ka bari yă tafi, saboda haka zan kashe ɗan farinka.’”
24 And as he was on the journey in the inn, the Lord met him, and sought to kill him.
Ya zama kuwa sa’ad da Musa yake masauki a kan hanya sai Ubangiji ya gamu da shi, ya nema ya kashe shi.
25 Then took Zipporah a sharp instrument, and cut off the foreskin of her son, and cast it at his feet, and said, Surely a bloody relative art thou to me.
Amma Ziffora ta ɗauki dutsen ƙanƙara mai ci, ta yanke loɓar ɗanta ta taɓa ƙafafun Musa da shi. Ta ce, “Tabbatacce kai angon jini ne a gare ni.”
26 And then he withdrew from him; when she said, A bloody relative, but only in respect of the circumcision.
Sai Ubangiji ya ƙyale shi. (A lokacin ta ce “angon jini,” tana nufin kaciya.)
27 And the Lord said to Aaron, Go to meet Moses, into the wilderness; and he went and met him by the mount of God, and kissed him.
Ubangiji ya ce wa Haruna, “Tafi cikin hamada ka sadu da Musa.” Sai ya sadu da Musa a dutsen Allah, ya sumbace shi.
28 And Moses told Aaron all the words of the Lord wherewith he had sent him, and all the signs which he had commanded him.
Sai Musa ya gaya wa Haruna dukan abin da Ubangiji ya aike yă faɗa, da kuma dukan mu’ujizan da ya umarce shi yă aikata.
29 And Moses and Aaron went and assembled all the elders of the children of Israel:
Musa da Haruna suka tattara dukan dattawan Isra’ilawa,
30 And Aaron spoke all the words which the Lord had spoken unto Moses; and he did the signs before the eyes of the people.
sai Haruna ya gaya musu dukan abin da Ubangiji ya ce wa Musa. Ya kuma aikata mu’ujizan a gaban mutanen,
31 And the people believed: and when they heard that the Lord had visited the children of Israel, and that he had looked upon their affliction, then they bowed their heads and worshipped.
sai suka gaskata. Sa’ad da suka ji cewa Ubangiji ya damu da su, ya kuma ga azabarsu, sai suka durƙusa suka yi sujada.

< Exodus 4 >