< Exodus 19 >

1 In the third month, after the children of Israel were gone forth out of the land of Egypt, the same day they came into the wilderness of Sinai.
A rana ta farko a cikin watan uku bayan da Isra’ilawa suka bar Masar, a wannan rana, suka iso Hamadar Sinai.
2 For they had departed from Rephidim, and they came to the desert of Sinai, and encamped in the wilderness; and Israel encamped there opposite the mount.
Bayan da suka tashi daga Refidim, suka shiga Hamadar Sinai, sai Isra’ilawa suka yi sansani a gaban dutsen.
3 And Moses went up unto God, and the Lord called unto him from the mount, saying, Thus shalt thou say to the house of Jacob, and tell the children of Israel.
Sai Musa ya hau kan dutsen don yă sadu da Allah, Ubangiji kuwa ya kira shi daga dutsen ya ce, “Wannan shi ne abin da za ka faɗa wa gidan Yaƙub, da kuma abin da za ka faɗa wa mutanen Isra’ila.
4 Ye have yourselves seen what I have done unto the Egyptians, and how I bore you on eagles' wings, and brought you unto myself.
‘Ku da kanku kun ga abin da na yi wa Masar, da yadda na ɗauko ku a kan fikafikan gaggafa na kawo ku wurina.
5 Now therefore, if you will truly obey my voice, and keep my covenant, then shall ye be unto me a peculiar treasure above all nations; for all the earth is mine:
Yanzu, in kuka yi mini cikakken biyayya, kuka kuma kiyaye yarjejjeniyata, to, za ku zama keɓeɓɓiyar taska a gare ni a cikin dukan al’ummai. Ko da yake duk duniya tawa ce,
6 And ye shall be unto me a kingdom of priests, and a holy nation; these are the words which thou shalt speak unto the children of Israel.
za ku zama firistoci masu tsarki da kuma al’umma keɓaɓɓiya a gare ni.’ Waɗannan su ne kalmomin da za ka faɗa wa Isra’ilawa.”
7 And Moses came and called for the elders of the people, and laid before them all these words which the Lord had commanded him.
Sai Musa ya koma ya aika a kira dukan dattawan mutane, ya bayyana dukan kalmomin da Ubangiji ya umarta, ya faɗa.
8 And all the people answered unanimously, and said, all that the Lord hath spoken will we do; and Moses returned the words of the people unto the Lord.
Dukan mutane suka amsa gaba ɗaya suka ce, “Za mu yi duk abin da Ubangiji ya faɗa.” Sai Musa ya mayar wa Ubangiji amsar da mutane suka bayar.
9 And the Lord said unto Moses, Behold, I will come unto thee in a thick cloud, for the sake that the people may hear when I speak with thee, and that also in thee they shall believe for ever; and Moses told the words of the people unto the Lord.
Ubangiji kuwa ya ce wa Musa, “Ina zuwa wurinka a cikin baƙin hadari, domin mutane su ji ni ina maganar da kai, domin su amince da kai koyaushe.” Sa’an nan Musa ya faɗa wa Ubangiji abin da mutane suka ce.
10 And the Lord said unto Moses, Go unto the people, and sanctify them today and tomorrow, and let them wash their clothes.
Sai Ubangiji ya ce wa Musa, “Tafi wurin mutanen, ka tsarkake su yau da gobe, ka sa su wanke tufafinsu.
11 And they shall be ready against the third day; for on the third day will the Lord come down, before the eyes of all the people, upon mount Sinai.
Su zama da shiri a rana ta uku, gama a ranar ce Ubangiji zai sauko a kan Dutsen Sinai a idon dukan mutane.
12 And thou shalt set bounds unto the people, round about, saying, Take heed to yourselves, that ye go not up into the mount, nor touch the border of it; whosoever toucheth the mount shall surely be put to death.
Sai ka yi wa jama’a iyaka kewaye da dutsen, ka kuma faɗa musu cewa, ‘Ku mai da hankali, kada ku hau dutsen ko ku taɓa gefensa. Duk wanda ya taɓa dutsen, lalle za a kashe shi.
13 Yet not a hand shall touch him, but he shall surely be stoned, or shot through; whether it be beast or man, it shall not live; when the trumpet soundeth long, they may come up to the mount.
Za a jajjefe shi da duwatsu, ko a harbe shi da kibiyoyi, ba hannun da zai taɓa shi. Mutum ko dabbar da ya taɓa, ba za a bar shi da rai ba.’ Lokacin da aka ji muryar ƙaho ne kawai za su iya taru a gindin dutsen.”
14 And Moses went down from the mount unto the people, and sanctified the people: and they washed their clothes.
Bayan da Musa ya gangara wurin mutane, ya tsarkake su, sai suka wanke tufafinsu.
15 And he said unto the people, Be ready against the third day; approach not unto a woman.
Sa’an nan ya ce wa mutane, “Ku shirya kanku domin rana ta uku. Ku ƙame kanku daga yin jima’i.”
16 And it came to pass on the third day when it was morning, that there were thunders and lightnings, and a heavy cloud was upon the mount, and the voice of the cornet was exceedingly loud; so that all the people that were in the camp trembled.
A safiyar rana ta uku, aka yi tsawa, da walƙiyoyi, sai ga girgije mai duhu a bisa dutsen, aka tsananta busar ƙaho, sai dukan jama’ar da suke cikin sansani suka yi rawar jiki.
17 And Moses brought forth the people out of the camp to meet with God; and they placed themselves at the foot of the mount.
Sa’an nan Musa ya jagoranci mutane daga sansani domin su sadu da Allah, sai suka tsaya a gefen dutsen.
18 And mount Sinai smoked in every part, because the Lord had descended upon it in fire; and the smoke thereof ascended as the smoke of a furnace, and the whole mount quaked greatly.
Dutsen Sinai kuwa ya tunnuƙe duka da hayaƙi, gama Ubangiji ya sauko a bisan dutsen cikin wuta. Hayaƙin ya hau kamar hayaƙin da yake fitowa daga matoya, duk dutsen ya yi rawa da ƙarfi,
19 And the voice of the cornet went on, and waxed louder and louder; Moses spoke, and God answered him with a loud voice.
sai karar ƙaho ya yi ta ƙaruwa. Sa’an nan Musa ya yi magana, murya Allah kuwa ta amsa masa.
20 And the Lord came down upon mount Sinai, on the top of the mount; and the Lord called Moses up to the top of the mount, and Moses went up.
Ubangiji ya sauko a kan ƙwanƙolin Dutsen Sinai, ya kira Musa zuwa ƙwanƙolin dutsen. Musa kuwa ya haura
21 And the Lord said unto Moses, Go down, charge the people, lest they break through unto the Lord to gaze, and many of them might perish.
sai Ubangiji ya ce masa, “Ka sauka ka faɗa wa jama’a, kada su kuskura su ƙetare layin iyakan nan, garin son zuwa don ganin Ubangiji, gama duk waɗanda suka yi haka za su mutu.
22 And the priests also, who come near to the Lord, shall sanctify themselves; lest the Lord break forth among them.
Ko firistocin da za su kusato Ubangiji sai su tsarkake kansu, don kada in hallaka su.”
23 And Moses said unto the Lord, The people cannot come up to mount Sinai; for thou hast charged us, saying, Set bounds about the mount and sanctify it.
Musa ya ce wa Ubangiji, “Mutanen ba za su hau Dutsen Sinai ba, gama kai da kanka ka gargaɗe mu, ‘Ku sa iyaka kewaye da dutsen ku kuma tsarkake shi.’”
24 And the Lord said unto him, Go, get thee down, and then shalt thou come up, thou, and Aaron with thee; but the priests and the people shall not break through to come up unto the Lord, lest he break forth among them.
Ubangiji ya amsa, “Sauka ka kawo Haruna tare da kai. Amma kada firistoci da mutane su zarce iyakan nan, a kan za su zo wurin Ubangiji, don kada in hallaka su.”
25 So Moses went down unto the people, and spoke unto them.
Saboda haka Musa ya sauka wurin mutane ya kuma faɗa musu.

< Exodus 19 >