< Exodus 16 >

1 And they took their journey from Elim, and all the congregation of the children of Israel came unto the wilderness of Sin, which is between Elim and Sinai, on the fifteenth day of the second month after their departing out of the land of Egypt.
Dukan taron Isra’ila suka tashi daga Elim suka zo hamadar Sin, wadda take tsakanin Elim da Sinai, a rana ta goma sha biyar ga wata biyu, bayan sun fito daga Masar.
2 And the whole congregation of the children of Israel murmured against Moses and Aaron in the wilderness:
A hamadan, dukan taro suka yi gunaguni a kan Musa da Haruna.
3 And the children of Israel said unto them, Would to God that we had died by the hand of the Lord in the land of Egypt, when we sat by the flesh-pot, when we ate bread to the full; for ye have brought us forth into this wilderness, to kill this whole assembly with hunger.
Isra’ilawa suka ce musu, “Da ma a hannun Ubangiji ne muka mutu a Masar, inda muka zauna kewaye da tukwanen nama, muna cin duk abincin da muke so, amma kun kawo mu cikin wannan hamada don ku kashe dukan wannan taro da yunwa.”
4 Then said the Lord unto Moses, Behold, I will let rain for you bread from heaven; and the people shall go out and gather a certain portion every day, in order that I may prove it, whether it will walk in my law, or not.
Sai Ubangiji ya ce wa Musa, “Zan zubo muku burodi kamar ruwa daga sama. Mutanen za su fita kowace rana su tattara abin da zai ishe su na ranan. Ta haka zan gwada su in ga ko za su bi umarnaina.
5 And it shall come to pass, on the sixth day, when they prepare what they shall have brought in, that it shall be twice as much as they shall gather daily.
A rana ta shida za su shirya abin da suka kwaso, wannan kuwa zai zama ninki biyu na abin da sukan tattara na sauran ranaku.”
6 And Moses and Aaron said unto all the children of Israel, At evening, then shall ye know that it is the Lord who hath brought you out from the land of Egypt:
Saboda haka Musa da Haruna suka ce wa dukan Isra’ila, “Da yamma za ku sani Ubangiji ne ya fitar da ku daga Masar.
7 And in the morning, then shall ye see the glory of the Lord; since he heareth your murmurings against the Lord; and what are we, that ye should murmur against us?
Da safe za ku ga ɗaukakar Ubangiji, saboda ya ji gunaguninku a kansa. Wane mu, da za ku yi gunaguni a kanmu?”
8 And Moses said, When the Lord giveth you in the evening flesh to eat, and bread in the morning to the full; since the Lord heareth your murmurings which ye murmur against him: —what are we then? not against us are your murmurings, but against the Lord.
Musa ya kuma ce, “Za ku san cewa shi ne Ubangiji, sa’ad da ya ba ku nama ku ci da yamma, da kuma duk burodin da kuke so da safe, saboda ya ji gunagunin da kuka yi a kansa. Namu a wane? Ai, gunaguninku ba a kanmu ba, amma a kan Ubangiji ne.”
9 And Moses said unto Aaron, Say unto all the congregation of the children of Israel, Come near before the Lord; for he hath heard your murmurings.
Sai Musa ya ce wa Haruna, “Ka faɗa wa dukan taron Isra’ila, ‘Ku zo gaban Ubangiji, gama ya ji gunaguninku.’”
10 And it came to pass, as Aaron was speaking unto the whole congregation of the children of Israel, that they turned round toward the wilderness, and, behold, the glory of the Lord appeared in the cloud.
Yayinda Haruna yake magana da dukan taron Isra’ila, sai suka duba wajen hamada, sai ga ɗaukakar Ubangiji tana bayyana a girgije.
11 And the Lord spoke unto Moses, saying,
Ubangiji ya ce wa Musa,
12 I have heard the murmurings of the children of Israel: speak unto them, saying, Toward evening ye shall eat flesh, and in the morning ye shall be filled with bread; and ye shall know that I am the Eternal your God.
“Na ji gunagunin Isra’ilawa. Ka faɗa musu, ‘A tsakanin fāɗuwar rana da almuru, za ku ci nama, da safe kuma za ku ƙoshi da burodi. Sa’an nan za ku sani ni ne Ubangiji Allahnku.’”
13 And it came to pass, that at evening the quails came up, and covered the camp; and in the morning there was a layer of dew round about the camp.
Da yamman wannan rana, sai makware suka rufe dukan sansani, da safe kuma sai ga raɓa ta kewaye sansani.
14 And when the layer of dew was gone up, behold, there was upon the face of the wilderness something fine in grains, small as the hoar-frost, on the ground.
Lokacin da raɓar ta watse, sai ga wani abu kamar tsaki, falle-falle kuma da laushi, fari, kamar hazo, a ƙasa.
15 And when the children of Israel saw it, they said one to another, It is manna, for they knew not what it was; and Moses said unto them, This is the bread which the Lord hath given you to eat.
Sa’ad da Isra’ilawa suka ga wannan, sai suka ce wa junansu, “Mene ne wannan?” Gama ba su san ko mene ne ba. Musa ya ce musu, “Wannan shi ne burodin da Ubangiji ya ba ku ku ci.
16 This is the thing which the Lord hath commanded, Gather of it every man according to his eating: an omer for every head, according to the number of your persons that every man hath in his tent, shall ye take.
Wannan shi ne abin da Ubangiji ya umarta, ‘Kowane mutum zai tattara bisa ga bukatarsa. Ku tara rabin gallon don mutum guda da yake cikin tentinku.’”
17 And the children of Israel did so; and they gathered, some much, some little.
Isra’ilawa suka yi kamar yadda aka faɗa musu, waɗansu suka tattara da yawa, waɗansu kuma kaɗan.
18 And when they measured it with an omer, he that had gathered much had nothing over, and he that had gathered little had no lack: every man according to his eating, had they gathered.
Da suka gwada a mudu, wanda ya tattara da yawa bai sami mafi yawa ba, wanda kuma ya tattara kaɗan bai sami ƙanƙani ba. Kowane mutum ya tattara daidai bukatarsa.
19 And Moses said, Let no man leave of it till the morning.
Sa’an nan Musa ya ce musu, “Kada wani yă bar saura har safe.”
20 But they hearkened not unto Moses; but some men left of it until morning, and it bred worms, and stank; and Moses was wroth with them.
Duk da haka waɗansu ba su kula da umarnin Musa ba, suka bar saura har safe, kashegari kuwa ta yi tsutsotsi, ta ruɓe, sai Musa ya yi fushi da su.
21 And so they gathered it every morning, every man according to his eating; and when the sun waxed hot, it melted.
Kowace safiya, kowanne mutum yakan tattara daidai bukatarsa, lokacin da rana ta yi zafi, sai ta narke.
22 And it came to pass on the sixth day, that they gathered twofold bread, two omers for every one; all the rulers of the congregation came and told it to Moses.
A rana ta shida, suka tattara ninki biyu, mudu biyu ga mutum guda, sai shugabannin taron suka zo suka kawo ƙara wurin Musa.
23 And he said unto them. This is what the Lord hath spoken, A rest, a holy rest is unto the Lord tomorrow: that which ye will bake bake today, and what ye will seethe seethe today; and all the remaining lay up for you to be kept until the morning.
Shi kuma ya ce musu, “Wannan shi ne umarnin Ubangiji, ‘Gobe za tă zama ranar hutu, Asabbaci mai tsarki ga Ubangiji. Domin haka sai ku toya abin da kuke so ku toya, ku kuma dafa abin da kuke so ku dafa. Abin da ya rage ku ajiye har safe.’”
24 And they laid it up till the morning, as Moses had bidden; and it did not stink, nor was there any worm therein.
Sai suka bar saura har safe, kamar yadda Musa ya umarta, bai kuwa yi wari ko yă yi tsutsa ba.
25 And Moses said, Eat it today; for a sabbath is this day unto the Lord: today ye will not find it in the field.
Musa ya ce, “Ku ci shi yau, saboda yau Asabbaci ne na Ubangiji. Ba za ku same shi a ƙasa a yau ba.
26 Six days shall ye gather it; but on the seventh day, the sabbath, on it there shall be none.
Kwana shida za ku tattara shi, amma a rana ta bakwai, Asabbaci, ba za a same shi ba.”
27 And it came to pass on the seventh day, that there went out some of the people to gather; but they found nothing.
Duk da haka waɗansu mutane suka fita a ranar Asabbaci don su tattara, amma ba su sami kome ba.
28 And the Lord said unto Moses, How long refuse ye to keep my commandments and my laws?
Sai Ubangiji ya ce wa Musa, “Har yaushe za ku ƙi bin dokokina da umarnaina?
29 See, that the Lord hath given you the sabbath, therefore he giveth you on the sixth day bread for two days; remain ye, every man in his place, let no man go out of his place on the seventh day.
Ku lura fa, ai, Ubangiji ne ya ba ku Asabbaci; shi ya sa a kan ba ku burodi na kwana biyu, a rana ta shida. Kowa ya kamata yă kasance inda yake a rana ta bakwai; kada kowa yă fita.”
30 So the people rested on the seventh day.
Sai mutanen suka huta a rana ta bakwai.
31 And the house of Israel called the name thereof Manna, [[Man]]; and it was like coriander-seed, white, and its taste was like wafers made with honey.
Mutanen Isra’ila suka kira burodin Manna. Manna yana nan fari kamar farin riɗi, ɗanɗanonsa kuma yana kama da masa da aka yi da zuma.
32 And Moses said, This is the thing which the Lord hath commanded, One omer-full of it is to be kept for your generations; in order that they may see the bread which I gave you to eat in the wilderness, when I brought you forth out of the land of Egypt.
Musa ya ce, “Wannan shi ne abin da Ubangiji ya umarta, ‘Ku auna mudu guda na Manna, a adana ta dukan zamananku, domin kowane zamani yă ga irin abincin da na ba ku ku ci a hamada, yayinda na fitar da ku daga Masar.’”
33 And Moses said unto Aaron, Take a flask, and put therein an omer-full of manna, and lay it up before the Lord, to be kept for your generations.
Saboda haka Musa ya ce wa Haruna, “Ka ɗauki tulu, ka sa mudu guda na Manna a ciki. Sa’an nan ka sa shi a gaban Ubangiji, don a adana don tsararraki masu zuwa.”
34 As the Lord had commanded Moses, so did Aaron lay it up before the Testimony, to be kept.
Sai Haruna ya ajiye Mannar a gaban Akwatin Alkawari, don a adana ta kamar yadda Ubangiji ya umarci Musa.
35 And the children of Israel ate the manna forty years, until they came to an inhabited land; the manna they did eat, until they came unto the borders of the land of Canaan.
Isra’ilawa suka yi shekaru arba’in suna cin Manna, har sai da suka shiga cikin ƙasar da take da mutane, suka ci Manna har zuwa kan iyakar ƙasar Kan’ana.
36 But the omer is a tenth part of an ephah.
(Omer guda, daidai ne da kashi ɗaya bisa goma na Efa.)

< Exodus 16 >