< Ecclesiastes 12 >
1 But remember also thy Creator in the days of thy youthful vigor, while the evil days are not yet come, nor those years draw nigh of which thou wilt say, I have no pleasure in them;
Ka tuna da Mahaliccinka a kwanakin ƙuruciyarka, kafin lokacin wahala ta zo shekaru kuma su ƙarato sa’ad da za ka ce, “Ba na jin daɗinsu,”
2 While the sun, and the light, and the moon, and the stars, are not yet darkened, and the clouds return not again after the rain;
kafin rana da haske wata da taurari su daina haske, gizagizai kuma su tattaru bayan da suka sheƙa ruwa;
3 On the day when the watchmen of the house will tremble and the men of might will bend themselves, and the grinders stand idle, because they are become few, and those be darkened that look through the windows;
sa’ad da masu tsaron gida suke rawar jiki, majiya ƙarfi kuma suka rasa ƙarfi, sa’ad da masu niƙa suka daina don ba su da yawa, idanun da suke duba ta taga suka duhunta;
4 And when the two doors on the streets will be locked, while the sound of the mill becometh dull, and man riseth up at the voice of the bird, and all the daughters of song are brought low;
sa’ad da aka rufe ƙofofin shiga tituna ƙarar niƙa kuma ya tsagaita; sa’ad da kukan tsuntsaye ta farkar da mutane, ba a kuwa jin waƙoƙinsu,
5 Also when men will be afraid of every elevation, and are terrified on every way, and the almond-tree will refuse [its blossom], and the locust will drag itself slowly along, and the desire will gainsay compliance; because man goeth to his eternal home, and the mourners go about the streets;
sa’ad da mutane suke jin tsoron tudu da kuma hatsarori a tituna; sa’ad da itacen almon ya toho, fāra kuma ya yi ta jan jikinsa da ƙyar, sha’awace-sha’awace sun kafe. Daga nan mutum ya tafi madawwamiyar gidansa ya bar masu makoki suna ta yi.
6 While the silver cord is not yet torn loose, and the golden bowl is not crushed, and the pitcher is not broken at the fountain, and the wheel is not crushed at the cistern;
Ka tuna da shi, kafin igiyar azurfa ta katse, ko tasar zinariya ta fashe; kafin tulu yă ragargaje a maɓulɓula, ko guga ta tsinke a rijiya,
7 When the dust will return to the earth as it was, and the spirit will return unto God who gave it.—
turɓaya ta koma ƙasar da ta fito, rai kuma yă koma ga Allah wanda ya ba da shi.
8 Vanity of vanities, saith Koheleth: all is vanity.—
“Ba amfani! Ba amfani!” In ji Malami, “Gaba ɗaya ba amfani!”
9 And in addition to this that Koheleth was wise, he continually also taught the people knowledge, and he probed, and searched out, and composed many proverbs.
Ba kawai Malami ya kasance mai hikima ba, amma kuma ya koyar da mutane. Ya yi tunani ya kuma yi binciken da ya tsara karin magana masu yawa.
10 Koheleth sought to find out acceptable words, and that which would be written down uprightly, even words of truth.
Malami ya yi bincike don yă sami kalmomin da suka dace, kuma abin da ya rubuta daidai ne da kuma gaskiya.
11 The words of the wise are like goads, and like nails fastened [are the words of] the men of the assemblies, which are given by one shepherd.
Kalmomin masu hikima kamar tsinken tsokanar dabba ne, tarin maganganunsu kuma kamar ƙusoshi ne da aka kafa daram, da aka ba wa Makiyayi guda.
12 But more than all these, my son, take warning for thyself: the making of many books would have no end; and much preaching is a weariness of the flesh.
Ka yi hankali ɗana, game da duk wani ƙari a kan waɗannan. Wallafa littattafai ba shi da iyaka, kuma yawan karatu yakan gajiyar da jiki.
13 The end of the matter is, let us hear the whole: Fear God, and keep his commandments; for this is the whole [duty of] man.
Yanzu an ji kome; ga ƙarshen magana. Ka ji tsoron Allah ka kuma kiyaye umarnansa, gama wannan shi ne dukan hakkin mutum.
14 For every deed will God bring into the judgment concerning every thing that hath been hidden, whether it be good, or whether it be bad.
Gama Allah zai shari’anta kowane irin aiki, har da waɗanda aka yi a ɓoye, ko nagari ne, ko mugu.