< Deuteronomy 5 >

1 And Moses called all Israel, and said unto them, Hear, O Israel, the statutes and the ordinances which I speak in your ears this day, that ye may learn them, and that ye may observe to do them.
Musa ya tattara dukan Isra’ila ya ce, Ku ji, ya Isra’ila, ƙa’idodi da dokokin da na furta a kunnuwanku a yau. Ku koye su, ku kuma tabbata kun bi su.
2 The Lord our God made a covenant with us in Horeb.
Ubangiji Allahnmu ya yi alkawari da mu a Horeb.
3 Not with our fathers did the Lord make this covenant, but with us, we who are here all of us alive this day.
Ba da kakanninmu ba ne Ubangiji ya yi wannan alkawari, amma da mu ne, da dukanmu waɗanda muke da rai a yau.
4 Face to face did the Lord speak with you on the mount, out of the midst of the fire,
Ubangiji ya yi magana fuska da fuska da ku daga wuta a kan dutse.
5 (I was standing between the Lord and between you at that time, to announce to you the word of the Lord; for ye were afraid by reason of the fire, and ye went not up into the mount; ) saying,
(A wannan lokaci na tsaya tsakanin Ubangiji da ku, don in furta muku maganar Ubangiji, domin kun ji tsoron wutar, ba ku kuwa hau dutsen ba.) Ya ce,
6 I am the Lord thy God, who have brought thee out of the land of Egypt, from the house of slavery.
“Ni ne Ubangiji Allahnka, wanda ya fitar da ku daga Masar, daga ƙasar bauta.
7 Thou shalt have no other gods before me.
“Ba za ka kasance da waɗansu alloli a gabana ba.
8 Thou shalt not make unto thyself any graven image, any likeness of any thing that is in the heavens above, or that is on the earth beneath, or that is in the water under the earth:
Ba za ka yi wa kanka gunki, ko wata siffar abin da take a sama a bisa, ko siffar abin da yake a duniya a ƙasa, ko siffar abin da yake a cikin ruwa a ƙarƙashin ƙasa ba.
9 Thou shalt not bow thyself down unto them, nor serve them; for I the Lord thy God am a jealous God, visiting the iniquity of the fathers upon the children, and upon the third and upon the fourth generation of them that hate me,
Ba za ka rusuna musu, ko ka yi musu sujada ba. Gama Ni, Ubangiji Allahnka, Allah ne mai kishi, nakan hukunta’ya’ya saboda zunuban iyaye har tsara ta uku da ta huɗu na waɗanda suka ƙi ni.
10 And showing kindness unto the thousandth generation of them that love me, and keep my commandments.
Amma nakan nuna ƙauna ga dubban tsararraki na waɗanda suke ƙaunata, suke kuma kiyaye dokokina.
11 Thou shalt not take the name of the Lord thy God in vain; for the Lord will not hold him guiltless that taketh his name in vain.
Ba za ka yi amfani da sunan Ubangiji Allahnka a banza ba, gama Ubangiji zai ba wa duk mai yin amfani da sunansa a banza laifi.
12 Keep the sabbath-day to sanctify it, as the Lord thy God hath commanded thee.
Ka kiyaye ranar Asabbaci ta wurin kiyaye ta da tsarki, yadda Ubangiji Allahnka ya umarce ka.
13 Six days shalt thou labor, and do all thy work;
Kwanaki shida za ka yi aiki, ka kuma yi dukan aikinka,
14 But the seventh day is the sabbath in honor of the Lord thy God; on it thou shalt not do any work, neither thou, nor thy son, nor thy daughter, nor thy man-servant, nor thy maid-servant, nor thy ox, nor thy ass, nor any of thy cattle, nor thy stranger that is within thy gates: in order that thy man-servant and thy maid-servant may rest as well as thou.
amma rana ta bakwai, Asabbaci ne ga Ubangiji Allahnka. A kanta ba za ka yi wani aiki ba, ko kai, ko ɗanka, ko’yarka, ko bawanka, ko baiwarka, ko saniyarka, ko jakinka, ko wani daga dabbobinka, ko baƙo a ƙofofinka, don bayinka maza da mata su ma su huta, kamar ka.
15 And thou shalt remember that thou hast been a servant in the land of Egypt, and that the Lord thy God brought thee out from there by a mighty hand and by an outstretched arm; therefore hath the Lord thy God commanded thee to observe the sabbath-day.
Ka tuna fa, dā kai bawa ne a ƙasar Masar amma Ubangiji Allahnka ya fitar da kai daga can da iko da kuma ƙarfi. Saboda haka Ubangiji Allahnka ya umarce ka ka kiyaye ranar Asabbaci.
16 Honor thy father and thy mother, as the Lord thy God hath commanded thee: in order that thy days may be prolonged, and in order that it may go well with thee, in the land which the Lord thy God giveth thee.
Ka ba da girma ga mahaifinka da mahaifiyarka, yadda Ubangiji Allahnka ya umarce ka, don ka yi tsawon rai, ka kuma sami zaman lafiya a ƙasar da Ubangiji Allahnka yake ba ka.
17 Thou shalt not kill.
Kada ka yi kisankai.
18 Neither shalt thou commit adultery.
Kada ka yi zina.
19 Neither shalt thou steal.
Kada ka yi sata.
20 Neither shalt thou bear false witness against thy neighbor.
Kada ka ba da shaidar ƙarya a kan maƙwabcinka.
21 Neither shalt thou covet thy neighbor's wife. Neither shalt thou desire thy neighbor's house, nor his field, nor his man-servant, nor his maid-servant, nor his ox, nor his ass, nor anything that is thy neighbor's.
Kada ka yi ƙyashin matar maƙwabcinka. Kada kuma ka yi sha’awar gidan maƙwabcinka, ko gonarsa, ko bayinsa maza da mata, ko saniyarka, ko jakinsa, ko dai wani abin da yake na maƙwabtanka.”
22 These words did the Lord speak unto all your assembly on the mount out of the midst of the fire, of the cloud, and of the thick darkness, with a great voice, but he did so no more; and he wrote them on two tables of stone, and he gave them unto me.
Waɗannan su ne dokokin da Ubangiji ya furta da babbar murya ga taronku gaba ɗaya, a can dutse ta tsakiyar wuta, girgije da kuma baƙin duhu; bai kuma ƙara kome ba. Sa’an nan ya rubuta su a kan alluna biyu na dutse, ya kuma ba ni su.
23 And it came to pass, when ye heard the voice out of the midst of the darkness, while the mount was burning with fire, that ye came near unto me, even all the heads of your tribes, and your elders;
Sa’ad da kuka ji muryar daga duhu, yayinda dutsen yana cin wuta, dukan manyan kabilanku da dattawanku suka zo wurina.
24 And ye said, Behold, the Lord our God hath caused us to see his glory and his greatness, and his voice have we heard out of the midst of the fire: this day have we seen that God can speak with man, who nevertheless may live.
Kuka kuma ce, “Ubangiji Allahnmu ya nuna mana ɗaukakarsa da zatinsa, mun kuma ji muryarsa a tsakiyar wutar. A yau mun ga cewa mutum zai iya rayu idan ma Allah ya yi magana da shi.
25 But now why should we die? for this great fire may consume us; if we continue to hear the voice of the Lord our God any more, then shall we die.
Amma yanzu, don me za mu mutu? Wannan wuta mai girma za tă cinye mu, za mu kuwa mutu in muka ci gaba da jin muryar Ubangiji Allahnmu.
26 For where is there any flesh, that hath heard the voice of the living God speaking out of the midst of the fire, like us, and hath remained alive?
Gama wanda ɗan adam ne ya taɓa jin muryar Allah mai rai yana magana daga wuta, kamar yadda muka ji, ya kuma tsira?
27 Do thou approach, and hear all that the Lord our God may say; and thou shalt speak unto us all that the Lord our God may speak unto thee; and we will hear and do it.
Kai, ka matsa kusa, ka saurara ga dukan abin da Ubangiji Allahnmu ya faɗa. Sa’an nan ka faɗa mana dukan abin da Ubangiji Allahnmu ya faɗa maka. Za mu saurara, mu kuma yi biyayya.”
28 And the Lord heard the voice of your words, while ye were speaking unto me; and the Lord said unto me, I have heard the voice of the words of this people, which they have spoken unto thee: they have done well in all that they have spoken.
Ubangiji ya ji ku, sa’ad da kuka yi magana da ni, sai Ubangiji ya ce mini, “Na ji abin da wannan mutane suka faɗa maka. Abin da suka faɗa daidai ne.
29 Who would grant that this their heart might remain in them, to fear me, and to keep all my commandments at all times; in order that it might be well with them, and with their children for ever!
Kash, da a ce zukatansu za su zama masu tsorona, su kuma kiyaye dukan dokokina kullum mana, saboda kome yă zama da lafiya gare su, da kuma’ya’yansu har abada!
30 Go, say to them, Return you unto your tents.
“Je, ka faɗa musu su koma tentunansu.
31 But as for thee, remain thou here by me, and I will speak unto thee all the commandments, and the statutes, and the ordinances, which thou shalt teach them, that they may do them in the land which I give them to possess it.
Kai kuwa ka tsaya a nan tare da ni saboda in ba ka umarnai, ƙa’idodi da kuma dokoki duka, da za ka koya musu don su bi a ƙasar da nake ba su, su mallaka.”
32 Observe ye then to do as the Lord your God hath commanded you: ye shall not turn aside to the right or to the left.
Sai ku yi hankali don ku yi abin da Ubangiji Allahnku ya umarce ku; kada ku juya dama ko hagu.
33 altogether in the way, which the Lord your God hath commanded you, shall ye walk; in order that ye may live, and that it may be well with you, and that ye may remain many days in the land which ye will possess.
Ku yi tafiya cikin dukan hanyar da Ubangiji Allahnku ya umarce ku, saboda ku zauna, ku yi nasara, ku kuma yi tsawon rai a ƙasar da za ku mallaka.

< Deuteronomy 5 >