< Deuteronomy 30 >

1 And it shall come to pass, when all these things are come upon thee, the blessing and the curse, which I have set before thee, and thou reflectest on them in thy heart among all the nations, whither the Lord thy God hath driven thee,
Sa’ad da dukan albarku da la’anonin nan da na sa a gabanku suka zo muku, kuka kuma sa su a zuciya, a duk inda Ubangiji Allahnku ya watsar da ku a cikin al’ummai,
2 So that thou returnest unto the Lord thy God, and hearkenest unto his voice according to all that I command this day, thou and thy children, with all thy heart, and with all thy soul:
sa’ad da kuma ku da’ya’yanku kuka komo ga Ubangiji Allahnku, kuka kuma yi biyayya da dukan zuciyarku da kuma dukan ranku, bisa ga kome da na umarce ku a yau,
3 That then the Lord thy God will restore thy captivity, and have mercy upon thee; and he will again gather thee from all the nations, whither the Lord thy God hath scattered thee.
a sa’an nan ne Ubangiji Allahnku zai yi muku jinƙai, yă ji tausayinku, yă kuma sāke tattara ku daga dukan al’ummai inda ya warwatsa ku.
4 If thy outcasts be at the outmost parts of heaven, from there will the Lord thy God gather thee, and from there will he fetch thee:
Ko da ma an kore ku zuwa ƙasa mafi nisa a ƙarƙashin sammai, daga can Ubangiji Allahnku zai tattara ku, yă dawo da ku.
5 And the Lord thy God will bring thee into the land which thy fathers possessed, and thou shalt possess it; and he will do thee good, and multiply thee above thy fathers.
Zai dawo da ku zuwa ƙasar da take ta kakanninku, za ku kuwa mallake ta. Zai sa ku yi arziki, ku kuma yi yawa fiye da kakanninku.
6 And the Lord thy God will circumcise thy heart, and the heart of thy seed, to love the Lord thy God with all thy heart, and with all thy soul, in order that thou mayest live.
Ubangiji Allahnku zai yi wa zukatanku kaciya da kuma zukatan zuriyarku, saboda ku ƙaunace shi da dukan zuciyarku da kuma dukan ranku, ku kuma rayu.
7 And the Lord thy God will put all these denunciations upon thy enemies, and on those that hate thee, who have persecuted thee.
Ubangiji Allahnku zai sa dukan waɗannan la’anoni a kan abokan gābanku waɗanda suke ƙinku, suke kuma tsananta muku.
8 And thou wilt return and hearken unto the voice of the Lord, and thou wilt do all his commandments which I command thee this day.
Za ku sāke yi wa Ubangiji biyayya, ku kuma bi dukan umarnan da nake ba ku a yau.
9 And the Lord thy God will make thee pre-eminent in every work of thy hand, in the fruit of thy body, and in the fruit of thy cattle, and in the fruit of thy land, for good; for the Lord will again rejoice over thee for good, as he rejoiced over thy fathers;
Sa’an nan Ubangiji Allahnku zai mayar da ku masu arziki ƙwarai a cikin dukan aiki hannuwanku, da kuma cikin’ya’yanku, da’ya’yan shanunku, da kuma hatsin gonarku. Ubangiji zai sāke jin daɗinku yă sa ku yi arziki, kamar dai yadda ya ji daɗin kakanninku.
10 If thou wilt hearken unto the voice of the Lord thy God, to keep his commandments and his statutes which are written in this book of the law; if thou wilt return unto the Lord thy God with all thy heart, and with all thy soul.
In dai kuka yi biyayya ga Ubangiji Allahnku, kuka kuma kiyaye umarnansa da ƙa’idodin da aka rubuta a wannan Littafin Doka, kuka juyo ga Ubangiji Allahnku da dukan zuciyarku da kuma dukan ranku.
11 For this commandment which I command thee this day, is not hidden from thee, nor is it far off.
To, abin da nake umartanku a yau, ba mai wuya ba ne gare ku, ba kuma abin da ya fi ƙarfinku ba ne.
12 It is not in heaven; that thou shouldst say, Who will go up for us to heaven, and fetch it down unto us, and cause us to hear it, that we may do it?
Ba ya can sama, balle ku ce, “Wa zai hau sama yă kawo mana, yă kuma furta mana, don mu yi biyayya?”
13 Neither is it beyond the sea; that thou shouldst say, Who will go over the sea for us, and fetch it unto us, and cause us to hear it, that we may do it!
Ba kuwa yana gaba da teku ba, da za ku ce, “Wa zai haye tekun don yă kawo mana, yă kuma furta mana, don mu yi biyayya?”
14 But the word is very nigh unto thee, in thy mouth, and in thy heart, that thou mayest do it.
A’a, kalmar tana nan dab da ku, tana cikin bakinku da cikin zuciyarku, don ku yi biyayya.
15 See, I have set before thee this day life and the good, death and the evil;
Ku duba, na sa a gabanku a yau, rai da wadata, mutuwa da kuma hallaka.
16 In that I command thee this day to love the Lord thy God, to walk in his ways, and to keep his commandments and his statutes and his ordinances; that thou mayest live and multiply; and that the Lord thy God may bless thee in the land whither thou goest to possess it.
Gama na umarce ku a yau, ku ƙaunaci Ubangiji Allahnku, don ku yi tafiya a hanyoyinsa, ku kuma kiyaye umarnansa, ƙa’idodinsa da kuma dokokinsa, sa’an nan za ku rayu, ku kuma ƙaru, Ubangiji Allahnku kuwa zai albarkace ku a ƙasar da kuke shiga don ci gādonta.
17 But if thy heart turn away, so that thou wilt not hearken, and thou sufferest thyself to be drawn away, and thou bowest down to other gods, and servest them:
Amma in zukatanku suka kangare, ba su kuwa yi biyayya ba, in kuma aka rinjaye ku don ku rusuna ga waɗansu alloli ku yi musu bauta,
18 I announce unto you this day, that ye shall surely perish; ye shall not remain many days upon the land, whither thou passest over the Jordan to go thither to possess it.
na furta muku yau cewa tabbatacce za a hallaka ku. Ba za ku zauna a ƙasar da kuke hayewa Urdun don ku shiga ku ci gādonta ba.
19 I call heaven and earth as witnesses against you this day, that I have set before you life and death, the blessing and the curse; therefore choose thou life, in order that thou mayest live, both thou and thy seed;
A wannan rana na kira bisa sama da ƙasa a matsayin shaidu a kanku, cewa na sa a gabanku rai da mutuwa, albarku da la’anoni. Yanzu sai ku zaɓi rai, saboda ku da’ya’yanku ku rayu
20 To love the Lord thy God, to hearken to his voice, and to cleave unto him; for he is thy life, and the length of thy days; that thou mayest dwell in the land which the Lord swore unto thy fathers, to Abraham, to Isaac, and to Jacob, to give unto them.
don kuma ku ƙaunaci Ubangiji Allahnku, ku saurari muryarsa, ku kuma manne masa. Gama Ubangiji shi ranku, zai kuwa ba ku shekaru masu yawa a ƙasar da ya rantse zai ba wa kakanninku, Ibrahim, Ishaku da Yaƙub.

< Deuteronomy 30 >