< Deuteronomy 27 >
1 And Moses with the elders of Israel commanded the people, saying, Keep the whole commandment which I command you this day.
Musa tare da dattawan Isra’ila suka umarci mutane suka ce, “Ku kiyaye dukan umarnai da na ba ku a yau.
2 And it shall be on the day when ye pass over the Jordan unto the land which the Lord thy God giveth thee, that thou shalt set up for thyself great stones, and cover them with plaster;
Sa’ad da kuka haye Urdun zuwa cikin ƙasar da Ubangiji Allahnku yake ba ku, ku kakkafa waɗansu manyan duwatsu, ku yi musu shafe da farar ƙasa.
3 And thou shalt write upon them all the words of this law, so soon as thou art passed over; in order that thou mayest go in unto the land which the Lord thy God giveth thee, a land flowing with milk and honey; as the Lord, the God of thy fathers, hath spoken unto thee.
Ku rubuta dukan waɗannan kalmomin doka a kansu, sa’ad da kuka haye kuka shiga ƙasar da Ubangiji Allahnku yake ba ku, ƙasa mai zub da madara da zuma, kamar dai yadda Ubangiji Allah na kakanninku, ya yi muku alkawari.
4 And it shall be so soon as ye are gone over the Jordan, that ye shall set up these stones, which I command you this day, on mount 'Ebal; and thou shalt cover them with plaster.
Sa’ad da kuma kuka haye Urdun, ku kakkafa waɗannan duwatsu a bisa Dutsen Ebal, kamar yadda na umarce a yau, ku yi musu shafe da farar ƙasa.
5 And thou shalt build there an altar unto the Lord thy God, an altar of stones: thou shalt not lift up any iron tool upon them.
Ku gina bagade wa Ubangiji Allahnku, bagaden dutse. Kada ku yi amfani da wani kayan aiki na ƙarfe a kansu.
6 Of whole stones shalt thou build the altar of the Lord thy God; and thou shalt offer thereupon burnt-offerings unto the Lord thy God;
Ku gina bagaden Ubangiji Allahnku da duwatsun fili, ku kuma miƙa hadaya ta ƙonawa a kansa ga Ubangiji Allahnku.
7 And thou shalt slay peace-offerings, and eat [them] there; and thou shalt rejoice before the Lord thy God.
Ku miƙa hadayun salama a can, kuna ci, kuna farin ciki a gaban Ubangiji Allahnku.
8 And thou shalt write upon the statues all the words of this law, very plainly.
Za ku kuma rubuta a fayyace dukan kalmomin wannan doka a kan waɗannan duwatsun da kuka kakkafa.”
9 And Moses with the priests, the Levites, spoke unto all Israel, saying, Be attentive, and hearken, O Israel! this day art thou become a people unto the Lord thy God.
Sai Musa da firistoci waɗanda suke Lawiyawa suka ce wa dukan Isra’ila, “Ku yi shiru, ya Isra’ila, ku saurara! Yanzu kun zama mutanen Ubangiji Allahnku.
10 Thou shalt therefore hearken to the voice of the Lord thy God, and do his commandments and his statutes, which I command thee this day.
Ku yi biyayya ga Ubangiji Allahnku, ku bi umarnansa da ƙa’idodin da nake ba ku a yau.”
11 And Moses commanded the people on the same day, saying,
A wannan rana Musa ya umarce mutane,
12 These shall stand upon mount Gerizzim to bless the people, when ye are come over the Jordan: Simeon, and Levi, and Judah, and Issachar, and Joseph, and Benjamin.
Sa’ad da kuka haye Urdun, sai waɗannan kabilai su tsaya a bisa Dutsen Gerizim su sa wa jama’a albarka, wato, kabilar Simeyon, Lawi, Yahuda, Issakar, Yusuf da Benyamin.
13 And these shall stand for the sake of the curse upon mount 'Ebal: Reuben, Gad, and Asher, and Zebulun, Dan, and Naphtali.
Waɗannan kabilai kuma za su tsaya a bisa Dutsen Ebal su furta la’ana, wato, kabilar Ruben, Gad, Asher, Zebulun, Dan da Naftali.
14 And the Levites shall commence, and say unto all the men of Israel with a loud voice,
Lawiyawa za su karanta wa dukan mutanen Isra’ila da babbar murya su ce,
15 Cursed be the man who maketh a graven or molten image, the abomination of the Lord, the work of the hands of the craftsman, and putteth it in a secret place; and all the people shall answer, and say, Amen.
“La’ananne ne mutumin da ya sassaƙa siffa, ko ya yi zubin gunki, abar ƙyama ce ga Ubangiji, aikin hannu mai sana’a da aka kafa a ɓoye.” Sai dukan mutane su ce, “Amin!”
16 Cursed be he that holdeth in light esteem his father or his mother; and all the people shall say, Amen.
“La’ananne ne mutumin da ya ƙasƙantar da mahaifinsa ko mahaifiyarsa.” Sai dukan mutane su ce, “Amin!”
17 Cursed be he that removeth the landmark of his neighbor; and all the people shall say, Amen.
“La’ananne ne mutumin da ya gusar da dutsen da aka kafa don nuna shaidar iyaka.” Sai dukan mutane su ce, “Amin!”
18 Cursed be he that causeth the blind to wander out of the way; and all the people shall say, Amen.
“La’ananne ne mutumin da ya karkatar da makaho daga hanya.” Sai dukan mutane su ce, “Amin!”
19 Cursed be he that perverteth the cause of the stranger, of the fatherless, and of the widow; and all the people shall say, Amen.
“La’ananne ne mutumin da ya yi rashin adalci ga baƙo, maraya ko gwauruwa.” Sai dukan mutane su ce, “Amin!”
20 Cursed be he that lieth with his father's wife; because he uncovereth his father's skirt; and all the people shall say, Amen.
“La’ananne ne mutumin da ya kwana da matar mahaifinsa, gama ya ƙasƙantar da gadon mahaifinsa ke nan.” Sai dukan mutane su ce, “Amin!”
21 Cursed be he that lieth with any manner of beast; and all the people shall say, Amen.
“La’ananne ne mutumin da ya yi jima’i da dabba.” Sai dukan mutane su ce, “Amin!”
22 Cursed be he that lieth with his sister, the daughter of his father, or the daughter of his mother; and all the people shall say, Amen.
“La’ananne ne mutumin da ya kwana da’yar’uwarsa,’yar mahaifinsa ko’yar mahaifiyarsa.” Sai dukan mutane su ce, “Amin!”
23 Cursed be he that lieth with his mother-in-law; and all the people shall say, Amen.
“La’ananne ne mutumin da ya kwana da mahaifiyar matarsa.” Sai dukan mutane su ce, “Amin!”
24 Cursed be he that smiteth his neighbor secretly; and all the people shall say, Amen.
“La’ananne ne mutumin da ya kashe maƙwabcinsa a ɓoye.” Sai dukan mutane su ce, “Amin!”
25 Cursed be he that taketh a bribe to slay a person, an innocent blood; and all the people shall say, Amen.
“La’ananne ne mutumin da ya karɓi cin hanci don yă kashe marar laifi.” Sai dukan mutane su ce, “Amin!”
26 Cursed be he that executeth not the words of this law to do them; and all the people shall say, Amen.
“La’ananne ne mutumin da bai yi na’am da kalmomin wannan doka ta wurin aikata su ba.” Sai dukan mutane su ce, “Amin!”