< Deuteronomy 25 >
1 If there be a controversy between men, and they come nigh unto a court of justice, and they judge them; and they justify the righteous, and condemn the wicked:
Idan mūsu ya tashi tsakanin mutum biyu har abin ya kai su kotu, alƙalai kuwa suka yanke hukunci a kan batun, suka kuɓutar da marar laifi sa’an nan suka hukunta mai laifi,
2 Then shall it be, if the guilty man deserve to be beaten, that the judge shall cause him to lie down, and to be beaten before his face, according to the degree of his fault, by a [certain] number.
in mai laifin ya cancanci bulala, alƙali zai sa yă kwanta a yi masa bulala a gabansa da yawan bulalan da ya dace da laifin,
3 Forty stripes may he give him, not more; so that he shall not exceed to have him beaten above these with too many stripes, and thy brother be thus rendered vile before thy eyes.
amma kada yă yi masa bulala fiye da arba’in. In ya yi masa fiye da haka, za a ƙasƙantar da ɗan’uwanku, zai kuma zama rainanne a idonku.
4 Thou shalt not muzzle the ox when he thresheth out the corn.
Kada ku yi wa saniya takunkumi sa’ad da take tattaka hatsi.
5 If brothers dwell together, and one of them die, and have no child: then shall the wife of the dead not be married abroad, unto a stranger; her husband's brother shall go in unto her, and take her to himself for wife, and perform the duty of a husband's brother unto her.
In’yan’uwa suna zama tare, in ɗayansu ya mutu babu ɗa, kada gwauruwar tă yi aure waje da iyalin. Ɗan’uwan mijinta zai ɗauke ta, yă aure ta, yă kuma cika abin da yă kamaci ɗan’uwan miji yă yi.
6 And it shall be, that the first-born whom she may bear shall succeed in the name of his brother who is dead; so that his name be not blotted out of Israel.
Ɗan farin da ta haifa zai ɗauki sunan ɗan’uwan da ya rasu saboda kada sunansa yă ɓace daga Isra’ila.
7 And if the man have no desire to take his sister-in-law: then shall his sister-in-law go up to the gate unto the elders, and say, My husband's brother refuseth to raise up unto his brother a name in Israel, he will not perform on me the duty of a husband's brother.
Amma fa, in mutum ba ya so yă auri matar ɗan’uwansa, sai tă tafi wurin dattawa a ƙofar gari tă ce, “Ɗan’uwan mijina ya ƙi yă wanzar da sunan ɗan’uwansa a Isra’ila. Ya ƙi yă cika abin da ya kamaci ɗan’uwan miji yă yi gare ni.”
8 Then shall the elders of his city call him, and speak unto him; and if he persist, and say, I have no desire to take her:
Sai dattawan garinsa su kira shi, su kuma yi masa magana. In ya nace yana cewa, “Ba na so in aure ta,”
9 Then shall his sister-in-law come nigh unto him in the presence of the elders, and pull his shoe from off his foot, and spit out before him, and shall commence and say, Thus shall be done unto that man that will not build up his brother's house.
sai gwauruwan nan, matar ɗan’uwansa tă haura wurinsa a gaban dattawa, tă tuɓe takalminsa guda, ta tofa masa miyau a fuska, tă ce, “Haka za a yi ga mutumin da zai ƙi kafa gidan ɗan’uwansa.”
10 And his name shall be called in Israel, The house of the barefooted.
Za a kira zuriyarsa a Isra’ila Iyalin da aka tuɓe masa takalmi.
11 When men strive together one with the other, and the wife of the one draweth near to deliver her husband out of the hand of him that smiteth him, and putteth forth her hand, and taketh him by the secrets:
In mutane biyu suna faɗa, sai matar mutum ɗaya daga cikinsu ta zo don tă kuɓutar da mijinta daga abokin faɗarsa, ta kuma miƙa hannu ta kama marainan wancan,
12 Then shalt thou cut off her hand, thy eye shall not have pity.
sai ku yanke hannunta. Kada ku ji tausayinta.
13 Thou shalt not have in thy bag divers weights, a great and a small.
Kada ku kasance da ma’auni iri biyu a jakarku, ɗaya babba, ɗaya ƙarami.
14 Thou shalt not have in thy house divers measures, a great and a small.
Kada ku kasance da mudu iri biyu a jakarku, ɗaya babba, ɗaya ƙarami.
15 A perfect and just weight shalt thou have, a perfect and just measure shalt thou have; in order that thy days may be prolonged in the land which the Lord thy God giveth thee;
Dole ku kasance da ma’aunin da kuma mudun da yake daidai, kuma na gaskiya, saboda ku yi tsawon rai a ƙasar da Ubangiji Allahnku yake ba ku.
16 For an abomination of the Lord thy God is every one that doth such things, every one that acteth unrighteously.
Gama Ubangiji Allahnku yana ƙyamar duk mai yi waɗannan abubuwa, da kuma mai rashin gaskiya.
17 Remember what 'Amalek did unto thee, by the way, at your coming forth out of Egypt;
Ku tuna da abin da Amalekawa suka yi muku a hanya, sa’ad da kuka fito Masar.
18 How he met thee by the way, and smote the hindmost of thee, all that were feeble behind thee, when thou was faint and weary; and he feared not God.
Yadda suka yi muku kwanto a hanya, suka fāɗa muku ta baya, suka karkashe waɗanda suka gaji tiɓis. Ba su ko ji tsoron Allah ba.
19 And it shall come to pass, when the Lord thy God giveth thee rest from all thy enemies round about, in the land which the Lord thy God giveth thee for an inheritance to possess it, that thou shalt blot out the remembrance of 'Amalek from under the heavens: thou shalt not forget.
Sa’ad da Ubangiji Allahnku ya ba ku hutu daga dukan abokan gābanku kewaye da ku, a ƙasar da yake ba ku ku mallaka a matsayin gādo, sai ku shafe Amalekawa daga duniya, don kada a ƙara tunawa da su. Kada fa ku manta!