< Deuteronomy 17 >

1 Thou shalt not sacrifice unto the Lord thy God any bullock, or lamb, whereon there is a blemish, any thing evil; for it is an abomination unto the Lord thy God.
Kada ku miƙa wa Ubangiji Allahnku, saniya ko tunkiyar da take da wani lahani, ko naƙasa a cikinta, gama wannan zai zama abar ƙyama gare shi.
2 If there be found in the midst of thee, within any one of thy gates, which the Lord thy God giveth thee. a man or a woman, that doth the wickedness in the eyes of the Lord thy God, to transgress his covenant,
In an sami wani namiji ko ta mace mai zama a cikinku, a ɗaya daga biranen da Ubangiji ya ba ku yana aikata abin da yake mugu a gaban Ubangiji Allahnku ta wurin karya alkawarinsa,
3 And he hath gone and served other gods, and worshipped them, either the sun, or the moon, or any of the host of heaven, which I have prohibited;
wanda ya saba wa umarnina, har ya yi sujada ga waɗansu alloli, yana rusuna musu, ko ga rana, ko ga wata, ko kuwa ga taurarin sama,
4 And it be told thee, and thou hearest of it: then shalt thou inquire diligently; and, behold, if it be true, the thing is certain, such abomination hath been wrought in Israel:
in kuwa aka faɗa muku wannan, to, dole a bincika sosai. In kuwa gaskiya ne, aka kuma tabbatar cewa wannan abin ƙyama ya faru a cikin Isra’ila,
5 Then shalt thou bring forth that man or that woman, who have committed this wicked thing, unto thy gates, the man or the woman, and thou shalt stone them with stones till they die.
sai a ɗauki namijin, ko ta mace wanda ya aikata wannan mugun abu zuwa ƙofar birni, a jajjefe wannan mutum sai ya mutu.
6 Upon the evidence of two witnesses, or of three witnesses, shall he that is worthy of death be put to death; he shall not be put to death upon the evidence of one witness.
Bisa ga shaidar mutum biyu ko uku, za a iya kashe mutum, amma ba za a iya kashe mutum bisa ga shaida mutum guda ba.
7 The hand of the witnesses shall be first upon him to put him to death, and the hand of all the people at the last; and thou shalt put the evil away from the midst of thee.
Hannuwan shaidun ne za su zama na farko a kisan wanda ake zargin, sa’an nan hannuwan dukan mutane. Dole ku fid da mugu daga cikinku.
8 If a matter be unknown to thee for decision, between blood and blood, between plea and plea, and between bodily injury and injury, [or] matters of controversy within thy gates: then shalt thou arise, and get thee up unto the place which the Lord thy God will choose;
In aka kawo ƙarar da yake da wuya sosai ga alƙali a kotunanku, ko wadda aka zub da jini ne, ko ta faɗa ce, ko kuwa ta wadda aka ci mutunci ce, ku kai su wurin da Ubangiji Allahnku zai zaɓa.
9 And thou shalt come unto the priests, the Levites, and unto the judge that may be in those days, and thou shalt inquire, and they shall inform thee of the sentence of the case;
Ku je wurin firistoci, waɗanda suke Lawiyawa, ga kuma alƙalin wanda yake mulki a lokacin. Ku bincika daga gare su, za su kuwa ba da hukunci.
10 And thou shalt do according to the sentence, which they may tell thee from that place which the Lord will choose, and thou shalt observe to do according to all that they may instruct thee;
Dole ku aikata hukuncin da suka yi a wurin da Ubangiji zai zaɓa. Ku lura fa, ku aikata kome da suka faɗa muku.
11 In accordance with the instruction which they may instruct thee, and according to the decision which they may say unto thee, shalt thou do: thou shalt not depart from the sentence which they may tell thee, to the right, or to the left.
Ku yi bisa ga dokar da suka koyar muku da kuma hukuncin da suka yi muku. Kada ku juya daga abin da suka faɗa muku, ko zuwa dama, ko zuwa hagu.
12 And the man that will act presumptuously, so as not to hearken unto the priest that standeth to minister there before the Lord thy God, or unto the judge, even that man shall die; and thou shalt put away the evil from Israel.
Duk mutumin da ya yi rashin hankali wa alƙali, ko ga firist wanda yake aiki a nan wa Ubangiji Allahnku, dole a kashe shi. Dole ku fid da mugu daga Isra’ila.
13 And all the people shall hear, and be afraid, and not act presumptuously any more.
Dukan mutane kuwa za su ji, su kuma ji tsoro, ba kuwa za su ƙara yin rashin hankali kuma ba.
14 When thou art come unto the land which the Lord thy God giveth thee, and thou hast taken possession of it, and dwellest therein, and thou sayest, I wish to set a king over me, like all the nations that are round about me:
Sa’ad da kuka shiga ƙasar da Ubangiji Allahnku yake ba ku, kuka mallake ta, kuka kuma zauna a cikinta, sai kuka ce, “Bari mu naɗa sarki a kanmu kamar sauran al’umman da suke kewaye da mu,”
15 Then mayest thou indeed set a king over thee, the one whom the Lord thy God will choose; [but] from the midst of thy brethren shalt thou set a king over thee; thou mayest not set over thee a stranger, who is not thy brother.
ku tabbata kun naɗa sarki a kanku wanda Ubangiji Allahnku ya zaɓa ne. Dole yă zama daga cikin’yan’uwanku. Kada ku sa baƙo a kanku, wanda ba mutumin Isra’ila ɗan’uwanku ba.
16 Only he shall not acquire for himself many horses; so that he may not cause the people to return to Egypt, in order to acquire many horses; whereas the Lord hath said unto you, Ye shall henceforth not return on that way any more.
Sarkin, ba zai nemi dawakai da yawa wa kansa ba, ko yă sa mutane su koma Masar don su sami ƙarin dawakai ba, gama Ubangiji ya faɗa muku, “Ba za ku ƙara koma wancan hanya kuma ba.”
17 Neither shall he take to himself many wives, that his heart may not turn away; nor shall he acquire for himself too much silver and gold.
Sarkin ba zai auri mata masu yawa ba, in ba haka ba zuciyarsa za tă karkata. Ba zai tara azurfa da zinariya da yawa ba.
18 And it shall be, when he sitteth upon the throne of his kingdom, that he shall write for himself a copy of this law in a book out of [that which is] before the priests, the Levites;
Sa’ad da ya hau kursiyin mulkinsa, sai yă rubuta wa kansa a littafin kofin wannan doka da aka ɗauka daga na firistoci, waɗanda suke Lawiyawa.
19 And it shall be with him, and he shall read therein all the days of his life: in order that he may learn to fear the Lord his God, to keep all the words of this law and these statutes, to do them.
Zai kasance tare da shi, zai kuma karanta shi dukan kwanakin ransa, saboda yă koyi girmama Ubangiji Allahnsa, yă kuma bi dukan kalmomin wannan doka da kuma waɗannan ƙa’idodi a hankali
20 So that his heart be not lifted up above his brethren, and so that he turn not aside from the commandment, to the right, or to the left: in order that he may live many days in his kingdom, he, and his children, in the midst of Israel.
don kada yă ɗauki kansa ya fi’yan’uwansa, yă kuma juya daga dokar zuwa dama, ko zuwa hagu. Sa’an nan shi da kuma zuriyarsa za su daɗe suna mulki a Isra’ila.

< Deuteronomy 17 >