< Daniel 1 >
1 In the third year of the reign of Jehoyakim the king of Judah came Nebuchadnezzar the king of Babylon unto Jerusalem, and besieged it.
A Shekara ta uku ta mulki Yehohiyakim sarkin Yahuda, Nebukadnezzar sarkin Babilon ya zo Urushalima ya kuma yi mata ƙawanya.
2 And the Lord gave up into his hand Yehoyakim the king of Judah, with part of the vessels of the house of God: and he brought them into the land of Shin'ar into the house of his god, namely, he brought the vessels into the treasure-house of his god.
Sai Ubangiji ya bashe Yehohiyakim sarkin Yahuda a hannunsa, tare da waɗansu kayayyakin haikalin Allah. Ya ɗauki waɗannan kayan zuwa cikin haikalin allahnsa a Babilon cikin ma’ajin gidan allahnsa.
3 And the king said unto Ashpenas, the chief of his eunuchs, that he should bring out of the children of Israel, and of the royal seed, and of the nobles,
Sa’an nan sarkin ya umarci Ashfenaz, shugaban fadarsa yă kawo waɗansu daga cikin Isra’ilawan da suka fito daga gidan sarauta da kuma na fitattun mutane.
4 [Certain] lads in whom there should be no kind of blemish, but who should be handsome in appearance, and intelligent in all wisdom, and acquainted with knowledge, and understanding science, and such as should have the ability to serve in the king's palace, and that these should be taught the learning and the language of the Chaldeans.
Matasa maza waɗanda ba su da wata naƙasa kuma kyawawa, hazikai ta kowace hanyar koyo, sanannu, masu saurin fahimtar abu, da kuma waɗanda suka cancanci su yi aiki a fadar sarki. Zai koya musu harshen Babiloniyawa da kuma littattafansu.
5 And the king ordered for them a daily provision for its day of the king's food, and of the wine which he drank, and to educate them three years, so that at the end thereof they should serve before the king.
Sarki kuma ya sa a ba su abinci da ruwan inabi kowace rana daga cikin abincin sarki. Za a koyar da su har shekaru uku, bayan haka kuma su shiga yin wa sarki hidima.
6 Now there were among these of the children of Judah, Daniel, Chananyah, Mishael, and 'Azaryah.
Daga cikin waɗannan da aka zaɓa akwai waɗansu daga Yahuda, Daniyel, Hananiya, Mishayel da kuma Azariya.
7 And the chief of the eunuchs assigned them names; and he assigned to Daniel the name of Belteshazzar; and to Chananyah, of Shadrach; and to Mishael, of Meshach; and to 'Azaryah, of 'Abed-nego.
Sai sarkin fada ya raɗa musu sababbin sunaye, ga Daniyel ya raɗa masa Belteshazar; ga Hananiya ya raɗa masa Shadrak; ga Mishayel ya raɗa masa Meshak; ga Azariya kuma ya raɗa masa Abednego.
8 But Daniel resolved in his heart that he would not defile himself with the food of the king, nor with the wine which he drank: and therefore he requested of the chief of the eunuchs that he might not need to defile himself.
Amma Daniyel ya ƙudura a zuciyarsa ba zai ƙazantar da kansa da abinci da ruwan inabin sarki ba, sai ya tambayi sarkin fada don a ba shi izinin kada yă ƙazantar da kansa ta wannan hanya.
9 And God gave Daniel kindness and mercy before the chief of the eunuchs.
Sai Allah ya sa sarkin fada ya nuna masa tagomashi ya kuma ƙaunaci Daniyel,
10 And the chief of the eunuchs said unto Daniel, I fear my lord the king, who hath ordered your food and your drink; for why should he see your face sadder looking than that of the lads who are of your age? and ye would thus endanger my head with the king.
amma sai sarkin fada ya ce wa Daniyel, “Ina jin tsoron ranka yă daɗe, sarkina wanda ya sa a ba ku abinci da ruwan inabi. Me zai sa yă ga kuna ramewa fiye da sauran samari, tsaranku? Sarki zai sa a fille mini kai saboda ku.”
11 Then said Daniel to the steward whom the chief of the eunuchs had given charge over Daniel, Chananyah, Mishael, and 'Azaryah,
Sai Daniyel ya ce wa mai gadi wanda sarkin fada ya sa yă kula da Daniyel, Hananiya, Mishayel da Azariya,
12 Prove, I beseech thee, thy servants, ten days; and let them give us vegetables to eat, and water to drink;
“Ina roƙonka ka gwada bayinka kwana goma. Kada ka ba mu kome sai kayan lambu mu ci da kuma baƙin ruwa mu sha.
13 And then let our countenances be looked at before thee, and the countenance of the lads that eat the food of the king: and as thou mayest see [fitting], so deal with thy servants.
Sa’an nan sai ka dubi fuskokinmu da na sauran samarin da suke ci daga abincin sarki; sa’an nan ka yi da bayinka bisa ga abin da ka gani.”
14 And he hearkened unto them in this matter, and proved them ten days.
Sai ya amince da haka ya kuma gwada su har kwana goma.
15 And at the end of ten days their countenances appeared better and fuller in flesh than [that of] all the lads who ate the food of the king.
A ƙarshen kwana goma sai aka ga fuskokinsu suna sheƙi, sun kuma yi ƙiba fiye da samarin da suke cin abinci irin na sarki.
16 And the steward took away their [apportioned] food, and the wine that they were to drink, and gave them vegetables.
Sai mai gadinsu ya janye abinci da ruwan inabi irin na sarki, ya ci gaba da ba su kayan lambu.
17 But as regardeth all these four lads, God gave them knowledge and intelligence in all learning and wisdom; and Daniel had understanding in all visions and dreams.
Ga samarin nan guda huɗu Allah ya ba su sani da ganewar dukan irin littattafai da kuma koyarwa. Daniyel kuma ya iya gane wahayi da kowane irin mafarki.
18 And at the end of the days [after] which the king had said that they should be presented, the chief of the eunuchs presented them before Nebuchadnezzar.
A ƙarshen lokacin da sarki ya sa da za a kawo su ciki, sai sarkin fada ya gabatar da su ga Nebukadnezzar.
19 And the king spoke with them; and there was not found among them all any one like Daniel, Chananyah, Mishael, and 'Azaryah: and so they served before the king.
Sarki kuwa ya yi magana da su, sai ya gano cewa babu wani kamar Daniyel, Hananiya, Mishayel da kuma Azariya; don haka sai suka shiga yi wa sarki hidima.
20 And in every matter of wise understanding, which the king required of them, he found them ten times superior above all the magicians and astrologers that were in all his kingdom.
A dukan al’amuran hikima da na fahimta wanda sarki ya tambaye su, ya tarar sun fi dukan masu sihiri da bokaye waɗanda suke cikin mulkinsa sau goma.
21 And Daniel continued even unto the first year of king Cyrus.
Daniyel kuwa ya kasance a nan har shekara ta farko ta mulkin sarki Sairus.