< Daniel 2 >

1 And in the second year of the reign of Nebuchadnezzar, Nebuchadnezzar dreamed dreams, whereat his spirit was troubled, and his sleep that was upon him was gone.
A shekara ta biyu ta mulkinsa, Nebukadnezzar ya yi mafarkai; hankalinsa ya tashi har ya kāsa barci.
2 Then said the king to call the magicians, and the astrologers and the sorcerers, and the Chaldeans, to solve for the king his dreams: and they came and placed themselves before the king.
Sai sarki ya sa aka tattara masa masu sihiri da masu dabo da bokaye da masanan taurari domin su faɗi abin da ya yi mafarki a kai. Da suka shigo suka tsaya a gaban sarki,
3 And the king said unto them, I have dreamed a dream, and my spirit is troubled to know the dream.
sai ya ce musu, “Na yi mafarkin da ya dame ni kuma ina so in san me yake nufi.”
4 Then spoke the Chaldeans to the king in Aramic, O king, live for ever: recite the dream to thy servants, and we will tell the interpretation.
Sai masanan taurarin suka amsa wa sarki da Arameyanci “Ran sarki yă daɗe! Ka faɗa wa bayinka mafarkin, mu kuma sai mu fassara.”
5 The king answered and said to the Chaldeans, The decree is firmly resolved on by me: If ye do not make known unto me the dream with its interpretation, ye shall be cut in pieces, and your houses shall be changed into a dunghill.
Sai sarki ya amsa wa masanan taurarin ya ce, “Na mance da abin, idan ba ku tuno mini mafarkin, duk da fassararsa ba, to, za a daddatse ku gunduwa-gunduwa, a mai da gidajenku juji.
6 But if ye tell the dream and its interpretation, then shall ye receive gifts and rewards and great honor from me. Therefore tell me the dream and its interpretation.
Amma in har kuka faɗa mini mafarkina kuka kuma bayyana fassararsa, za ku sami lada mai girma. Saboda haka ku faɗa mini mafarkin da kuma fassararsa.”
7 They answered the second time and said, Let the king recite the dream to his servants, and we will tell its interpretation.
Sai suka sāke amsa masa suka ce, “Ran sarki yă daɗe, faɗa wa bayinka mafarkin, mu kuma za mu fassara shi.”
8 The king answered and said, I know of a certainty that ye wish to gain time, because ye see the decree is firmly resolved on by me:
Sai sarki ya amsa ya ce, “Na gane cewa kuna ƙoƙari ku ɓata lokaci ne kawai domin ku ga na manta da abin.
9 That if ye do not make known unto me the dream, there is but one sentence for you; for ye have prepared lying and deceptive words to speak before me, till the time be changed. Therefore relate to me the dream, and I shall know that ye can tell me its interpretation.
In ba ku faɗa mini mafarkin ba, akwai hukunci guda ɗaya kurum dominku. Kun haɗa baki domin ku faɗa mini munanan al’amura domin ku ruɗe ni har lokaci yă wuce. Sai ku faɗa mini mafarkin, ta haka kuwa zan sani za ku iya yi mini fassararsa.”
10 The Chaldeans answered before the king, and said, There is not a man upon the habitable earth that can tell the king's matter: wherefore no mighty and powerful king ever hath asked such a thing of any magician, or astrologer, or Chaldean.
Sai masanan taurarin suka amsa wa sarki suka ce, “Babu wani mutum a duniyan nan da zai iya yin abin da sarki yake nema! Babu wani sarki mai daraja da girma wanda ya taɓa yin irin wannan tambaya ga masu sihiri ko masu dabo ko masanan taurari.
11 And the matter which the king requireth is difficult, and there is no other that can tell it before the king, except the gods, whose dwelling is not with flesh.
Abin da sarki yake nema yana da wuya matuƙa. Babu wani da zai iya bayyana wannan ga sarki sai dai alloli; kuma ba su zama tare da’yan adam.”
12 For all this cause the king became angry, and very furious; and he commanded to destroy all the wise men of Babylon.
Wannan ya sa sarki ya fusata ƙwarai, ya ba da umarni a tafi da dukan masu hikima na Babilon a kashe su.
13 And the law went forth and [some of] the wise men were slain: and they sought Daniel and his companions to slay them.
Sai aka ba da dokar da za a kashe masu hikima, sa’an nan aka aika mutane su je su nemo Daniyel da abokansa domin a kashe su.
14 Then made Daniel representations with intelligence and prudence to Aryoch the captain of the king's guard, who was gone forth to slay the wise men of Babylon.
Sa’ad da Ariyok, shugaban ƙungiyar matsaran sarki, ya fita domin yă kashe masu hikima na Babilon, sai Daniyel ya yi masa magana cikin hikima da dabara.
15 He commenced and said to Aryoch the king's commander, Wherefore is the law so hasty from the king? Then made Aryoch the matter known to Daniel.
Ya tambayi mai tsaro na sarki, “Me ya sa sarki ya fitar da wannan doka haka da fushi?” Sai Ariyok ya yi wa Daniyel bayanin batun.
16 But Daniel went in, and requested of the king that he would give him time, that he might tell the interpretation to the king.
Da jin haka sai Daniyel ya tafi wurin sarki ya nemi ƙarin lokaci, domin yă bayyana wa sarki mafarkin da kuma fassararsa.
17 Then went Daniel to his house, and made the matter known to Chananyah, Mishael, and 'Azaryah, his companions.
Sa’an nan Daniyel ya komo gida ya kuma sanar wa abokansa Hananiya, Mishayel da Azariya, batun nan duka.
18 In order that they might pray for mercy of the God of heaven concerning this secret: so that Daniel and his companions might not be destroyed with the rest of the wise men of Babylon.
Ya roƙe su su roƙi jinƙan Allah na sama domin wannan mafarki, saboda kada a kashe shi da abokansa tare da sauran masu hikima na Babilon.
19 Thereupon was the secret revealed unto Daniel in a vision of the night. Then did Daniel bless the God of heaven.
A wannan dare sai aka bayyana wa Daniyel mafarkin cikin wahayi. Daniyel kuwa ya ɗaukaka Allah na sama.
20 Daniel commenced and said, May the name of God be blessed from eternity and to all eternity; for wisdom and might are his;
Ya ce, “Yabo ya tabbata ga sunan Allah har abada abadin; hikima da iko nasa ne.
21 And he changeth times and seasons; he removeth kings, and raiseth up kings: he giveth wisdom unto the wise, and knowledge to those that possess understanding.
Yana sāke lokuta, yana tuɓe sarakuna yana kuma naɗa waɗansu. Yana ba da hikima ga masu hikima kuma ilimi ga masu basira.
22 He it is that revealeth what is deep and secret; he knoweth what is in the darkness, and the light dwelleth with him.
Yakan bayyana zurfafa da ɓoyayyun abubuwa; ya san abin da yake cikin dare, haske kuwa yana zaune tare da shi.
23 To thee, O God of my father, do I give thanks, and I praise thee, who hast given me wisdom and might, and because thou hast made known unto me what we prayed for of thee; for thou hast made known unto us the king's matter.
Na gode maka ina yabonka, Allah na kakannina. Kai ka san hikima da iko, ka sanar da ni abin da muka tambaye ka, ka kuma sanar da mu mafarkin sarki.”
24 Therefore did Daniel go in unto Aryoch, whom the king had ordered to destroy the wise men of Babylon, He went and said thus unto him, the wise men of Babylon must thou not destroy: bring me before the king, and I will tell unto the king the interpretation.
Sai Daniyel ya tafi wurin Ariyok, wanda sarki ya sa yă kashe masu hikiman Babilon, ya kuma ce masa, “Kada ka kashe masu hikiman Babilon ka kai ni wurin sarki, ni kuma zan fassara masa mafarkinsa.”
25 Then did Aryoch bring Daniel before the king in haste, and thus he said unto him, Here have I found a man out of the children of the exiles of Judah, who will make known unto the king the interpretation.
Sai Ariyok ya kai Daniyel wurin sarki nan take ya ce masa, “Na gano wani mutum daga cikin kamammun kabilar Yahuda wanda zai faɗa wa sarki abin da mafarkin yake nufi.”
26 The king answered and said to Daniel, whose name was Belteshazzar, Art thou able to make known unto me the dream which I have seen, and its interpretation?
Sarki ya tambayi Daniyel (wanda ake kira Belteshazar), za ka iya faɗa mini mafarkin da na yi ka kuma fassara shi?
27 Daniel answered in the presence of the king, and said, The secret which the king hath demanded no wise men, astrologers, magicians, or soothsayers, can tell unto the king;
Daniyel ya amsa, “Babu wani mai hikima, ko mai sihiri, ko mai dabo ko mai duban da zai iya warware wa sarki wannan matsala da ta dame shi,
28 But there is a God in heaven that revealeth secrets, and he hath made known to king Nebuchadnezzar what is to be in the latter days. Thy dream, and the visions of thy head upon thy couch, were these.
amma akwai Allahn da yake a sama wanda yake bayyana asirai, ya nuna wa sarki Nebukadnezzar abin da zai faru a kwanaki masu zuwa. Mafarkinka da wahayin da ya wuce cikin tunaninka a sa’ad da kake kwance a gadonka su ne,
29 As for thee, O king, thy thoughts, when thou wast on thy couch, rose [within thee] concerning what is to come to pass hereafter; and the Revealer of secrets hath made known to thee what is to come to pass.
“A sa’ad da kake kwance, ya sarki, tunaninka ya ga al’amuran da suke zuwa, kuma shi mai bayyana al’amuran ya bayyana maka asiran abubuwan da za su faru.
30 But as for me, this secret hath not been revealed to me because of any wisdom that is in me more than in all other living; but for the sake that men might make known the interpretation to the king, and that thou mightest understand the thoughts of thy heart.
Amma ba a bayyana mini wannan asiri saboda ina da wata hikima fiye da sauran mutane ba, sai dai domin a sanar wa sarki da fassarar, ka kuma san tunanin da ya shiga zuciyarka.
31 Thou, O king, sawest, and behold there was a large image; this image was mighty, and its brightness was excellent; it stood opposite to thee; and its form was fear-inspiring.
“Ya sarki, ka ga wata babbar siffa, mai girma, siffa ce mai haske, abar bantsoro tana tsaye a gabanka.
32 As regardeth this image, its head was of fine gold, its breast and its arms were of silver, its belly and its thighs of copper,
An yi kan wannan siffa da zinariya zalla, ƙirjinta da kuma hannuwanta an yi su da azurfa, cikinta da kuma cinyarta da tagulla ne.
33 Its legs of iron, its feet part of them of iron and part of them of clay.
An yi ƙafafun da ƙarfe, tafin ƙafafunta kuma an yi rabi da ƙarfe rabi kuma da yumɓu.
34 Thou didst look on till the moment that a stone tore itself loose, not through [human] hands, and it struck the image upon its feet that were of iron and clay, and ground them to pieces.
A lokacin da kake dubawa, sai aka yanko wani dutse, amma ba da hannun mutum ba. Ya fāɗa a kan ƙafafun siffar na ƙarfen da aka haɗa da yumɓu aka kuma ragargaje su.
35 Then were the iron, the clay, the copper, the silver, and the gold ground up together, and became like the chaff of the summer threshing-floors; and the wind carried them away, that no trace was found of them; and the stone that had stricken the image became a mighty mountain, and filled the whole earth.
Sai ƙarfen da yambun da tagulla da azurfan da kuma zinariyan suka ragargaje a lokaci ɗaya ya zama kamar ƙaiƙayi a masussuka a lokacin kaka. Sai iska ta kwashe su ta tafi, har ba a iya ganin ko alamarsu. Amma dutsen da ya fāɗo a siffar ya girke ya zama tsauni ya kuma cika dukan duniya.
36 This is the dream; and its interpretation will we relate before the king.
“Wannan shi ne mafarkin, yanzu kuma za mu fassara ta wa sarki.
37 Thou, O king, art a king of kings, to whom the God of heaven hath given kingdom, power, and strength, and honor:
Ya, sarki, kai ne sarkin sarakuna. Allah na sama ya ba ka iko da girma da suna;
38 And wheresoever the children of men dwell, hath he given the beasts of the field and the fowls of the heaven into thy hand, and hath made thee ruler over them all. Thou art the head of gold.
a cikin hannunka ya sanya ɗan adam, da namun jeji da tsuntsayen sama. A duk inda suke zaune, ya maishe ka ka yi mulki a bisansu kai ne kan zinariyan nan na siffar.
39 And after thee there will arise another kingdom inferior to thee; and another third kingdom of copper, which will bear rule over all the earth.
“A bayanka, za a yi wani mulki, wanda bai kai naka ba. A gaba kuma, za a yi mulki na uku wanda yake na tagulla, zai yi mulkin dukan duniya.
40 And the fourth kingdom will be as strong as iron; forasmuch as iron grindeth up and beateth down all things, and as iron that breaketh [every thing], will it grind up and break all these.
A ƙarshe, za a yi mulki na huɗu, mai ƙarfi kamar ƙarfe, Da yake baƙin ƙarfe yakan kakkarya, ya ragargaje abubuwa, haka nan wannan mulki zai ragargaje sauran mulkoki
41 And that thou sawest the feet and toes, and part of them of potter's clay, and part of them of iron, [signifieth] that it will be a divided kingdom, although there will be in it of the strength of the iron; forasmuch as thou sawest the iron mingled with miry clay.
Ka kuma ga an yi ƙafafun da yatsotsin da baƙin ƙarfe gauraye da yumɓu, wato, mulkin zai rabu, amma zai kasance da ƙarfi kamar na baƙin ƙarfe da yake gauraye da yumɓu.
42 And as the toes of the feet were part of them of iron, and part of them of clay: so will the kingdom be partly strong and partly brittle.
Kamar yadda yatsotsin rabi na ƙarfe rabi kuma na yumɓu ne, haka wannan mulki zai zama rabi mai ƙarfi rabi kuma marar ƙarfi.
43 And whereas thou sawest iron mingled with miry clay: so will they mingle themselves among the seed of men; but they will not cleave firmly one to another, even as iron cannot be mingled with clay.
Kamar dai yadda ka ga ƙarfen ya gauraye da yumɓu, haka mutanen za su zama a gauraye amma ba za su haɗu da juna ba, kamar yadda baƙin ƙarfe da yumɓu ba su haɗuwa.
44 But in the days of these kings will the God of heaven set up a kingdom: which shall to eternity not be destroyed, and its rule shall not be transferred to any other people; [but] it will grind up and make an end of all these kingdoms, while it will itself endure for ever.
“A lokacin mulkin waɗannan sarakunan, Allah na sama zai kafa mulki da ba zai taɓa rushewa ba, ba kuma za a ba ma waɗansu mutane ba. Zai ragargaje waɗannan mulkokin da kuma kawo su ga ƙarshe, amma shi wannan mulki zai dawwama har abada.
45 Whereas thou sawest that out of the mountain a stone tore itself loose, not through [human] hands, and that it ground up the iron, the copper, the clay, the silver, and the gold: the great God hath made known to the king what is to come to pass after this. And the dream is reliable, and its interpretation certain.
Wannan shi ne ma’anar wannan wahayin da ka gani na dutsen da aka yanko daga jikin tsaunin, amma ba da hannun ɗan adam ba, dutsen da ya ragargaza ƙarfen, da tagullar, da yumɓun da azurfar da kuma zinariyar. “Allah mai girma ya nuna wa sarki abin da zai faru nan gaba. Mafarkin gaskiya ne, fassararsa kuma abin dogara ne.”
46 Then did king Nebuchadnezzar fall upon his face, and he bowed down to Daniel, and ordered that they should offer an oblation and sweet odors unto him.
Sai sarki Nebukadnezzar ya fāɗi da fuskarsa har ƙasa a gaban Daniyel domin ya girmama shi ya kuma umarta a miƙa hadaya da kuma hadayar ƙonawa ta turare ga Daniyel.
47 The king answered unto Daniel, and said, Of a truth it is, that your God is the God of gods, and the Lord of kings, and the revealer of secrets; because thou hast been able to reveal this secret.
Sarki ya kuma ce wa Daniyel, “Tabbatacce Allahnka shi ne Allahn alloli da kuma Sarkin sarakuna da mai bayyana asirai, gama ka iya bayyana wannan asiri.”
48 Then did the king elevate Daniel, and gave him many great presents, and made him ruler over the whole province of Babylon, and chief of the superintendents over all the wise men of Babylon.
Sai sarki ya ɗora Daniyel a babban matsayi ya kuma sanya shi mai mulki a kan dukan yankin ƙasar Babilon; ya kuma ɗora shi yă zama mai kula da duk masu hikima.
49 Then requested Daniel of the king, that he might appoint Shadrach, Meshach, and 'Abed-nego, over the public service of the province of Babylon; but Daniel remained in the gate of the king.
Bugu da ƙari, bisa ga bukatar Daniyel sai sarki yă naɗa Shadrak da Meshak da Abednego su zama masu kula da harkokin lardin Babilon, amma Daniyel kuma ya tsaya a fadar sarki.

< Daniel 2 >