< Amos 8 >

1 Thus did the Lord Eternal show unto me: and, behold, there was a basket of summer fruit.
Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka ya nuna mini. Ubangiji ya nuna mini kwandon nunannun’ya’yan itace.
2 And he said, What dost thou see, 'Amos? And I said, A basket of summer fruit. Then said the Lord unto me, The end is come for my people Israel: I will not farther indulge them any more.
Ya yi tambaya ya ce, “Me ka gani Amos?” Sai na amsa na ce, “Kwandon nunannun’ya’yan itace.” Sai Ubangiji ya ce mini, “Lokaci ya yi wa mutanena Isra’ila da ba zan ƙara barinsu ba.
3 And the songs of the temple shall become a wailing on that day, saith the Lord Eternal: many shall be the dead bodies; in every place shall men throw them down, [saying, ] Be silent.
“A ranan nan,” in ji Ubangiji Mai Iko Duka, “Waƙoƙin a haikali za su koma makoki. Za a ga gawawwaki a ko’ina! Shiru!”
4 Hear this, O ye that are greedy to swallow the needy, and to ruin the poor of the land,
Ku ji wannan, ku da kuke tattake masu bukata kuka kori matalautan ƙasar.
5 Saying, When will the new moon be gone, that we may sell provision? and the sabbath, that we may open the corn-warehouses, making the ephah small, and increasing the shekel, and cheating with deceitful balances?
Kuna cewa, “Yaushe Sabon Wata zai wuce don mu sayar da hatsi, Asabbaci ta wuce, don mu sayar da alkama?” Mu yi awo da ma’aunin zalunci mu ƙara kuɗin kaya mu kuma cutar da mai saya,
6 That we may buy the poor for silver, and the needy for a pair of shoes; and even sell the refuse of the corn?
mu sayi matalauta da azurfa masu bukata kuma da takalmi, mu sayar da alkamar haɗe da yayi.
7 Sworn hath the Lord by the excellency of Jacob, Surely I will not forget to eternity all their works.
Ubangiji ya rantse da Girman Yaƙub, “Ba zan taɓa mantawa da duk wani abin da suka yi ba.
8 Shall because of this the land not tremble, and mourn every one that dwelleth therein? and shall it not rise up like a stream wholly, and roll onward and sink again like the stream of Egypt?
“Shin, ƙasar ba za tă yi rawan jiki saboda wannan ba, kuma duk masu zama a cikinta ba za su yi makoki ba? Ƙasar duka za tă hau ta sauka kamar Nilu; za a dama ta sa’an nan ta nutse kamar kogin Masar.
9 And it shall come to pass on that day, saith the Lord Eternal, that I will cause the sun to set at noon, and I will bring darkness over the earth on a bright day;
“A wannan rana,” in ji Ubangiji Mai Iko Duka, “Zan sa rana ta fāɗi da tsakar rana in kuma duhunta duniya da rana tsaka.
10 And I will change your feasts into mourning, and all your songs into lamentations; and I will bring upon all loins sackcloth, and upon every head baldness; and I will cause [the land] to mourn as one doth for an only son, and its end to be as a day of bitter [complaint].
Zan mai da bukukkuwanku na addini su zama makoki kuma dukan waƙoƙinku su zama kuka. Zan sa dukanku ku sa rigunan makoki za ku kuma aske kawunanku. Zan sa wannan lokaci yă zama kamar lokacin da ake makokin ɗan tilon da ake da shi kuma ƙarshenta kamar rana mai ɗaci.
11 Behold, days are coming, saith the Lord Eternal, when I will send a famine in the land, not a famine for bread, nor a thirst for water, but to hear the words of the Lord:
“Ranakun suna zuwa,” in ji Ubangiji Mai Iko Duka, “sa’ad da zan aika da yunwa cikin ƙasar, ba yunwar abinci ko ta ƙishirwa ba, sai dai yunwa ta jin maganar Ubangiji.
12 And they will wander about from sea to sea, and from the north even to the east, they will roam about to seek the word of the Lord; but they shall not find it.
Mutane za su yi ta tangaɗi daga teku zuwa teku suna yawo daga arewa zuwa kudu, suna neman maganar Ubangiji, amma ba za su samu ba.
13 On that day shall the fair virgins and the young men faint for thirst;
“A wannan rana “kyawawan’yan mata da kuma samari masu ji da ƙarfi za su suma don ƙishirwa.
14 Those that swear by the guilt of Samaria, and say, As thy god liveth, O Dan; and, As liveth the worshipped idol of Beer-sheba', —yea, they shall fall, and never rise up again.
Waɗanda suka yi rantsuwa da abin kunya na Samariya, ko kuma su ce, ‘Muddin allahnku yana a raye, ya Dan,’ ko kuwa, ‘Muddin allahn Beyersheba yana a raye,’ za su fāɗi, ba kuwa za su ƙara tashi ba.”

< Amos 8 >