< Amos 6 >

1 Woe to those that are free from care in Zion, and that are in safety on the mount of Samaria, who are named the chief of the nations, to whom the house of Israel come!
Taku ta ƙare, ku da kuke zaman sakewa a Sihiyona, da ku waɗanda kuke ji zama a Dutsen Samariya lafiya ne, ku manyan mutanen ƙasar da take sananniya, waɗanda mutanen Isra’ila suke zuwa!
2 Pass ye over unto Calneh, and see; and go from there to Chamath-rabbah; then go down to Gath of the Philistines: whether they be better than these kingdoms? or whether their territory be greater than your territory?
Ku je Kalne ku dube ta; ku wuce daga can zuwa Hamat-rabba, sa’an nan ku gangara zuwa Gat a Filistiya. Sun fi masarautunku biyu ne? Ƙasarsu ta fi taku girma?
3 [Ye] that deem far away the evil day, and cause the seat of violence to come near;
Kuna ƙoƙari ku kauce wa wannan muguwar rana kuna kuma jawo mulkin tashin hankali kusa.
4 That lie upon beds of ivory, and are stretched out upon their couches, and eat lambs out of the flock, and calves out of the midst of the stall;
Kuna kwanciya a kan gadajen da aka yi musu shimfiɗar hauren giwa kuna mimmiƙe a kan kujerunku. Kuna cin naman ƙibabbun raguna da na ƙosassun’yan maruƙa.
5 That chant to the sound of the psaltery, and like David's do they imagine their instrument of music to be;
Kuna kaɗa molayenku yadda Dawuda ya yi kuna ƙirƙiro waƙoƙi a kan kayan kaɗe-kaɗe.
6 That drink out of wine-bowls, and anoint themselves with the costliest of ointments; but who feel no pain for the wound of Joseph.
Da manyan kwanoni kuke shan ruwan inabi kuna kuma shafa mai mafi kyau, amma ba kwa baƙin ciki game da kangon da Yusuf ya zama.
7 Therefore now shall they go into exile at the head of exiles, and the noisy banquet of those that were stretched out shall pass away.
Saboda haka za ku zama na farkon da za su tafi zaman bauta; bukukkuwanku da shagulgulanku za su ƙare.
8 The Lord Eternal hath sworn by his own existence, saith the Lord the God of hosts, I abhor the pride of Jacob, and his palaces do I hate: therefore will I surrender up [to the enemy] the city with all that filleth it.
Ubangiji Mai Iko Duka da kansa ya rantse, Ubangiji Allah Maɗaukaki ya furta, “Ina ƙyamar girman kan Yaƙub, ba na kuma son kagarunsa; zan ba da birnin da duk abin da yake cikinta.”
9 And it shall come to pass, that if there remain ten men in one house, they shall die.
Ko da mutum goma ne suka ragu a gida guda, su ma za su mutu.
10 And should a man's uncle or relative carry him forth, to bring out the bones out of the house, and say unto him that is in the recesses of the house, Is there yet any one with thee? he will say, There is no one left. Then will he say, Be silent; for we may not make mention of the name of the Lord.
In kuma wani dangi ya shiga don yă fitar da gawawwakin yă ƙone ya kuwa tambayi wani wanda yake ɓoye a can, yana cewa, “Akwai wani tare da kai?” Ya kuwa ce, “Babu,” sai yă ce, “Kul! Kada mu ambaci sunan Ubangiji.”
11 For, behold, the Lord commandeth, and he will smite the great house with breaches, and the little house with clefts.
Gama Ubangiji ya ba da umarni, zai kuma ragargaza babban gidan nan kucu-kucu ƙaramin gidan kuwa zai yi rugu-rugu da shi.
12 Do horses ever run upon the rock? or will one plough there with oxen? that ye have turned justice into poison, and the fruit of righteousness into wormwood;
Dawakai sukan yi gudu a kan duwatsu? Wani yana iya yin noma a teku da shanun noma? Amma ga shi kun mai da gaskiya ta zama dafi amfanin adalci kuma ya zama ɗaci,
13 Ye who rejoice for a thing of naught, who say, Have we not through our own strength procured ourselves horns?
ku da kuke murna saboda an ci Lo Debar da yaƙi kuka kuma ce, “Ba da ƙarfinmu ne muka ƙwace Karnayim ba?”
14 For, behold, I will raise up against you a nation, O house of Israel, saith the Lord the God of hosts, and they shall oppress you from the entrance of Chamath unto the brook of the wilderness.
Gama Ubangiji Allah Maɗaukaki ya ce, “Zan sa wata ƙasa ta tayar muku, ya ku gidan Isra’ila, wadda za tă matsa muku tun daga Lebo Hamat zuwa kwarin Araba.”

< Amos 6 >