< Amos 5 >

1 Hear ye this word which I take up against you, as a lamentation, O house of Israel.
Ku ji wannan magana, ya gidan Isra’ila, ina makokin nan dominku.
2 She is fallen, she will not rise again—the virgin of Israel: she is thrown down upon her land; there is none to raise her up.
“Budurwa Isra’ila ta fāɗi, ba za tă ƙara tashi ba, an yashe ta a ƙasarta, ba wanda zai ɗaga ta.”
3 For thus hath said the Lord Eternal, The city that goeth forth with a thousand shall retain but a hundred, and she that goeth forth with a hundred shall retain but ten, [left] to the house of Israel.
Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka ya ce, “Birnin da ta fitar da masu ƙarfi dubbai don Isra’ila guda ɗari kaɗai za su dawo; garin da ya fitar da masu ƙarfi ɗari kuwa goma kaɗai za su dawo.”
4 For thus hath said the Lord unto the house of Israel, Seek ye for me, and ye shall live;
Ga abin da Ubangiji ya ce wa gidan Isra’ila. “Ku neme ni ku rayu;
5 But seek not for Beth-el, and into Gilgal enter not, and to Beer-sheba' do not pass over; for Gilgal shall surely go into exile, and Beth-el shall become naught.
kada ku nemi Betel, kada ku je Gilgal, kada ku yi tafiya zuwa Beyersheba. Gama ba shakka Gilgal za tă tafi bauta, za a kuwa mai da Betel ba kome ba.”
6 Seek for the Lord, and ye shall live: so that he come not suddenly like fire over the house of Joseph, and it devour, and there be none to quench it in Beth-el;
Ku nemi Ubangiji ku kuma rayu, ko kuwa zai ratsa yă share gidan Yusuf kamar wuta; zai cinye Betel kuwa ba zai sami wanda zai kashe ta ba.
7 Ye who change justice into wormwood, and cast down righteousness to the earth!
Ku ne masu mai da gaskiya ta koma ɗaci ku kuma zubar da adalci.
8 [But] he maketh the seven stars and Orion, and changeth into morning the shadow of death, and maketh the day dark into night; he it is that calleth for the waters of the sea, and poureth them out over the face of the earth: The Lord is his name;
(Shi wanda ya yi Taurarin nan da ake ce Kaza da’Ya’yanta da kuma Mai Farauta da Kare, wanda ya mai da duhu ya zama haske ya kuma baƙanta rana ta zama dare, yakan kwashe ruwan teku ya zubar a ƙasa, Ubangiji ne sunansa,
9 That causeth wasting to prevail against the strong, so that wasting shall come against the fortress.
yakan kawo hallaka a mafaka mai ƙarfi yakan kuma mai da birnin mai katanga ya zama kufai).
10 They hate him that rebuketh in the gate, and him that speaketh uprightly they abhor.
Ba ku son mai yin gaskiya a ɗakin shari’a kuna ƙin mai faɗar gaskiya.
11 Therefore forasmuch as you tread down upon the poor, and ye take from him onerous contributions of corn: if ye have built houses of hewn stone, ye shall not dwell in them; if ye have planted pleasant vineyards, ye shall not drink their wine.
Kuna matsa wa matalauta kuna sa su dole su ba ku hatsi. Saboda haka, ko da yake kun gina gidajen duwatsu, ba za ku zauna a cikinsu ba; ko da yake kun nome gonaki masu kyau, ba za ku sha ruwan inabinsu ba.
12 For I know your manifold transgressions and your numerous sins: ye are those that are the adversaries of the just, that take a ransom, and that wrest [the cause of] the needy in the gate.
Gama na san yawan laifofinku da kuma girman zunubanku. Kuna danne masu adalci kuna kuma cin hanci kuna kuma hana a yi wa matalauta shari’ar adalci a majalisa.
13 Therefore will the intelligent keep silence in that time; for it is an evil time.
Saboda haka mai hankali yakan yi shiru a lokuta kamar haka, gama lokutan mugaye ne.
14 Seek for the good, and not the evil, in order that ye may live: and so will the Lord, the God of hosts, be with you, as ye have said.
Ku yi nagarta, ba mugunta ba; don ku rayu sa’an nan Ubangiji Allah Maɗaukaki zai kasance da ku, kamar yadda kuka ce zai yi.
15 Hate the evil, and love the good, and establish justice firmly in the gate: perhaps the Lord the God of hosts will be gracious unto the remnant of Joseph.
Ku ƙi mugunta, ku ƙaunaci nagarta; ku dinga yin shari’ar gaskiya a ɗakunan shari’a. Mai yiwuwa Ubangiji Allah Maɗaukaki zai ji tausayin raguwar Yusuf.
16 Therefore thus hath said the Eternal, the God of hosts, the Lord, On all public places there is lamentation, and in all the streets they cry, Woe! woe! and they call the husbandman to mourning, and to lamentation those skilled in wailing.
Saboda haka ga abin da Ubangiji, Ubangiji Allah Maɗaukaki yana cewa, “Za a yi kururuwa a dukan tituna a kuma yi kuka don azaba a dukan wuraren da jama’a sukan taru. Za a yi kira ga manoma su yi kuka masu makoki kuma su yi kuka.
17 And in all vineyards there is lamentation; for I will pass through thy midst, saith the Lord.
Za a yi kuka a dukan gonakin inabi, gama zan ratsa a cikinku,” in ji Ubangiji.
18 Woe unto you that long for the day of the Lord! for what do you wish the day of the Lord? it is [one of] darkness, and not of light.
Kaitonku masu son ganin ranar Ubangiji! Don me kuke son ganin ranar Ubangiji? Za a duhunta ranan nan, ba haske ba.
19 As if a man were to flee from a lion, and a bear should meet him; and he enter into the house, and lean his hand against the wall, and a serpent should bite him.
Za ku zama kamar mutanen da suka guje wa zaki sai suka fāɗa a hannun beyar, ko kuma kamar wanda ya shiga gida ya dāfa hannu a bango sai maciji ya sare shi.
20 Behold the day of the Lord is [one of] darkness, and not of light; yea, it is obscure, and hath no brightness.
Ashe, ranar Ubangiji ba duhu ba ce, a maimakon haske, duhu wuluk, ba tare da ko ɗan haske ba.
21 I hate, I despise your feast-days, and I will not smell [the sacrifices] on your festive assemblies.
“Na ƙi, ina kuma ƙyamar bukukkuwanku na addini; ba na son ganin tarurrukanku.
22 For though ye should offer me burnt-offerings and your meat-offerings, I will not accept them in favor: and the peace-offerings of your fatted cattle will I not look at.
Ko da kun kawo mini hadayu na ƙonawa da kuma hadayu na hatsi, ba zan karɓa ba. Ko da kun kawo zaɓaɓɓun hadayu na zumunta, ba zan ɗauke su a bakin kome ba.
23 Remove thou from around me the noise of thy songs: and the playing of thy psalteries I will not hear.
Ku tashi daga nan da surutan waƙoƙinku! Ba zan saurari kaɗe-kaɗe da bushe bushenku ba.
24 But let justice roll along like water, and righteousness like a mighty stream.
Amma bari gaskiya ta kwararo kamar kogi, adalci kuma kamar rafin da ba ya taɓa bushewa!
25 Have ye offered unto me sacrifices and meat-offerings in the wilderness [during] forty years, O house of Israel?
“Kun kawo mini hadayu da sadakoki shekaru arba’in a cikin jeji, ya ku gidan Isra’ila?
26 Bear then the canopy of your chief idol, and the figure of your images, the star of your god, which ye have made for yourselves.
Kun ɗaga masujadar sarkinku, siffofin gumakanku, tauraron allahnku, wanda kuka yi wa kanku.
27 And I will cause you to go into exile far beyond Damascus, saith the Lord, The God of hosts is his name.
Saboda haka zan tura ku zaman bauta gaba da Damaskus,” in ji Ubangiji, wanda sunansa ne Allah Mai Iko.

< Amos 5 >