< Amos 1 >

1 The words of 'Amos, who was among the herdmen of Tekoa, which he foresaw concerning Israel in the days of 'Uzziyah the king of Judah, and in the days of Jerobo'am the son of Joash the king of Israel, two years before the earthquake.
Kalmomin Amos, ɗaya daga cikin makiyayan Tekowa, abubuwan da ya gani game da Isra’ila shekaru biyu kafin a yi girgizar ƙasa, a lokacin da Uzziya yake sarkin Yahuda, Yerobowam ɗan Yowash kuma yake sarkin Isra’ila.
2 And he said, The Lord will cry aloud out of Zion, and from Jerusalem will he send forth his voice; and then shall mourn the pastures of the shepherds, and then shall dry up the top of Carmel.
Ya ce, “Ubangiji ya yi ruri daga Sihiyona ya kuma yi tsawa daga Urushalima; wuraren kiwo duk sun bushe, dutsen Karmel kuma ya yi yaushi.”
3 Thus hath said the Lord, For three transgressions of Damascus, and for four, will I not turn away their punishment; because they have threshed [the inhabitants of] Gil'ad with threshing instruments of iron;
Ga abin da Ubangiji ya ce, “Saboda zunubai uku na Damaskus, har guda huɗu ma, ba zan fasa hukunta su ba. Domin sun ci zalunci Gileyad zalunci mai tsanani,
4 And I will send a fire into the house of Chazael, which shall devour the palaces of Ben-hadad.
zan sa wuta a gidan Hazayel, da za tă ƙona kagarun Ben-Hadad.
5 And I will break the bars of Damascus, and cut off the inhabitants from the valley of Aven, and him that holdeth the sceptre from the house of 'Eden: and the people of Syria shall be exiled unto Kir, saith the Lord.
Zan kakkarye ƙofofin Bet-Damaskus; zan hallaka sarkin da yake cikin Kwarin Awen da kuma mai riƙe da sandar mulkin Bet-Eden. Mutanen Aram za su je bauta a ƙasar Kir,” in ji Ubangiji.
6 Thus hath said the Lord, For three transgressions of Gazzah, and for four, will I not turn away their punishment; because they carried away exiles in full numbers, to deliver them up to Edom;
Ga abin da Ubangiji ya ce, “Saboda zunubai uku na Gaza, har guda huɗu ma, ba zan fasa hukunta su ba. Don sun kwashe al’umma gaba ɗaya sun sayar wa Edom,
7 And I will send a fire against the wall of Gazzah, which shall devour her palaces;
Zan aika da wuta a katangar Gaza ta ƙone duk kagarunta.
8 And I will cut off the inhabitants from Ashdod, and him that holdeth the sceptre from Ashkelon, and I will turn my hand against 'Ekron: and the remnant of the Philistines shall perish, saith the Lord Eternal.
Zan hallaka sarkin Ashdod da kuma mai riƙe da sandar mulki na Ashkelon. Zan hukunta Ekron, har sai dukan Filistiyawa sun mutu,” in ji Ubangiji Mai Iko Duka.
9 Thus hath said the Lord, For three transgressions of Tyre, and for four, will I not turn away their punishment; because they delivered up the exiles in full numbers to Edom, and remembered not the brotherly covenant;
Ga abin da Ubangiji ya ce, “Saboda zunubai uku na Taya, har guda huɗu ma, ba zan fasa hukunta su ba. Don sun kwashe al’umma gaba ɗaya sun kai su bauta a Edom, ba su kula da yarjejjeniyar da aka yi ta zama kamar’yan’uwa ba,
10 And I will send a fire against the walls of Tyre, which shall devour her palaces.
zan aika da wuta a Taya, da za tă ƙone kagarunta.”
11 Thus hath said the Lord, For three transgressions of Edom, and for four, will I not turn away their punishment; because he pursued with the sword his brother, and disregarded his mercy, and his anger tore in pieces continually, and he kept his wrath for ever:
Ga abin da Ubangiji ya ce, “Saboda zunubai uku na Edom, har guda huɗu ma, ba zan fasa hukunta shi ba. Don ya fafari ɗan’uwansa da takobi, babu tausayi, domin ya ci gaba da fusata bai yarda yă huce daga fushinsa ba.
12 And I will send out a fire against Theman, which shall devour the palaces of Bozrah.
Zan aika wuta a Teman da za tă ƙone kagarun Bozra.”
13 Thus hath said the Lord, For three transgressions of the children of 'Ammon, and for four, will I not turn away their punishment; because they have ripped up the pregnant women of Gil'ad, in order to enlarge their own territory;
Ga abin da Ubangiji ya ce, “Saboda zunubai uku na Ammon, har guda huɗu ma, ba zan fasa hukunta shi ba. Don ya tsaga cikin matan Gileyad masu juna biyu don kawai yă ƙwace ƙasar.
14 And I will kindle a fire within the walls of Rabbah, which shall devour her palaces, with shouting on the day of battle, with a storm on the day of the tempest;
Zan sa wuta a katangar Rabba da za tă ƙone kagarunta za a yi kururuwa a ranar yaƙi, faɗan kuwa zai yi rugugi kamar hadiri.
15 And their king shall go into exile, he and his princes together, saith the Lord.
Sarkinta zai je bauta, shi da ma’aikatansa,” in ji Ubangiji.

< Amos 1 >