< 2 Samuel 1 >

1 Now it came to pass after the death of Saul, when David was returned from smiting the 'Amalekites, that David abode in Ziklag two days.
Bayan mutuwar Shawulu, Dawuda ya dawo daga karkashe Amalekawa. Sai ya zauna a Ziklag kwana biyu.
2 And it came to pass on the third day, that, behold, a man came out of the camp from Saul with his clothes rent, and earth upon his head: and it happened, when he came to David, that he fell to the earth, and prostrated himself.
A rana ta uku sai ga wani mutum ya zo daga sansanin Shawulu da yagaggen riga da ƙura a kansa. Da ya zo wurin Dawuda sai ya fāɗi a ƙasa don yă nuna bangirma.
3 And David said unto him, From where comest thou? And he said unto him, Out of the camp of Israel am I escaped.
Dawuda ya tambaye shi ya ce, “Daga ina ka fito?” Ya amsa ya ce, “Na tsere ne daga sansanin Isra’ila.”
4 And David said unto him, What took place there? I pray thee, tell me. And he said, That the people are fled from the battle, and that also many of the people are fallen and have died; and that also Saul and Jonathan his son are dead.
Dawuda ya ce, “Gaya mini, me ya faru?” Sai ya ce, “Mutane sun gudu daga yaƙi, aka kuma karkashe yawancin mutane. Shawulu da ɗansa Yonatan ma sun mutu.”
5 And David said unto the young man that told him, How knowest thou that Saul is dead as also Jonathan his son?
Sai Dawuda ya ce wa saurayin da ya kawo labarin, “Yaya ka san cewa Shawulu da ɗansa Yonatan sun mutu?”
6 And the young man that told him said, I happened entirely by chance to be upon mount Gilboa', when, behold, there was Saul leaning upon his spear; and, lo, the chariots and horsemen had overtaken him.
Saurayin ya ce, “Ina kan dutsen Gilbowa a lokacin sai na ga Shawulu jingine a māshinsa. Kekunan yaƙi da mahayansu suna matsowa kusa da shi.
7 And he turned round, and he saw me, and called unto me, And I said, Here am I.
Da ya juya ya gan ni sai ya kira ni, na kuwa ce masa, ‘Ga ni?’
8 And he said unto me, Who art thou! And I answered him, An 'Amalekite am I.
“Ya tambaye ni ya ce, ‘Wane ne kai?’ “Na ce, ‘Ni mutumin Amalek ne.’
9 And he said unto me, Place thyself, I pray thee, by me, and slay me; for a mortal tremor hath seized on me, although my life is yet whole in me.
“Sai ya ce mini, ‘Matso kusa ka kashe ni! Ina cikin azabar mutuwa, sai dai har yanzu ina da rai.’
10 So I placed myself by him, and slew him, because I was sure that he could not live after his fall; and I took the crown that was upon his head, and the bracelet that was on his arm, and I have brought them unto my lord hither.
“Saboda haka na matso kusa da shi na kashe shi, domin na san cewa ba zai yi rai ba, da yake ya riga ya fāɗi. Sai na cire rawanin da yake kansa, na kuma cire warwaron hannunsa, na kuwa kawo maka su duka, ranka yă daɗe!”
11 David thereupon took hold of his clothes, and rent them; and [so did] likewise all the men that were with him:
Sai Dawuda da dukan mutanen da suke tare da shi suka yayyage rigunarsu.
12 And they lamented, and wept, and fasted until the evening, for Saul, and for Jonathan his son, and for the people of the Lord, and for the house of Israel; because they were fallen by the sword.
Suka yi makoki, da kuka, da azumi har yamma saboda Shawulu da ɗansa Yonatan, da saboda sojojin Ubangiji, da kuma gidan Isra’ila, gama an karkashe su a yaƙi.
13 And David said unto the young man that told him, Whence art thou? And he said, The son of a stranger, an 'Amalekite, am I.
Dawuda ya ce wa saurayin da ya kawo labarin, “Daga ina ka fito?” Ya ce, “Ni ɗan wani baƙo ne, mutumin Amalek.”
14 And David said unto him, How wast thou not afraid to stretch forth thy hand to destroy the Lord's anointed?
Dawuda ya ce masa, “Yaya ba ka ji tsoro ɗaga hannu ka hallaka shafaffe na Ubangiji ba?”
15 And David called one of the young men, and said, Come near, and fall upon him. And he smote him that he died.
Sai Dawuda ya kira ɗaya daga cikin mutanensa ya ce, “Je ka kashe shi!” Haka kuwa ya buge shi, ya kuwa mutu.
16 And David said unto him, Thy blood is upon thy own head; for thy mouth hath testified against thee, saying, I myself have slain the Lord's anointed.
Gama Dawuda ya riga ya ce masa, “Alhakin jininka yana bisa kanka tun da yake da bakinka ka ce, ‘Ni ne na kashe shafaffe na Ubangiji.’”
17 And David lamented with this lamentation over Saul and over Jonathan his son:
Dawuda ya rera wannan makoki saboda Shawulu da ɗansa Yonatan.
18 And he said, That the children of Judah should be taught the bow; behold it is written in the book of Yashar.
Ya umarta a koya wa mutanen Yahuda wannan waƙa mai suna Makokin Baka (tana a rubuce a Littafin Yashar),
19 O beauty of Israel! upon the high places slain: how are the mighty fallen!
“Ya Isra’ila, an kashe darajarki a kan tuddanki. Ga shi, jarumawa sun fāɗi!
20 Tell it not in Gath, publish it not in the streets of Ashkelon; that the daughters of the Philistines may not be glad, that the daughters of the uncircumcised may not rejoice.
“Kada a faɗe shi a Gat, kada a yi shelarsa a titunan Ashkelon, don kada’yan matan Filistiyawa su yi murna don kada’yan matan marasa kaciya su yi farin ciki.
21 O mountains of Gilboa', no dew, nor rain be upon you, nor fields of offerings; for there the shield of the mighty was stained, the shield of Saul, as though it had not been anointed with oil.
“Ya duwatsun Gilbowa, kada a sāke yin ruwa ko raɓa a kanku, balle gonakin da suke ba da hatsin hadaya su ƙara bayarwa. Gama a can ne garkuwoyin manyan sojoji suka kwanta, suka kwanta a wulaƙance. Garkuwar Shawulu kuwa, ba za a ƙara shafa mata mai ba.
22 From the blood of the slain, from the fat of the mighty, the bow of Jonathan turned never back, and the sword of Saul never returned empty.
“Daga jinin waɗanda aka kashe, daga tsokar naman jarumi, bakan Yonatan bai juye baya ba, takobin Shawulu bai komo ba tare da gamsuwa ba.
23 Saul and Jonathan, the beloved and the dear in their lives, were even in their death not divided: more than eagles were they swift, more than lions were they strong.
Shawulu da Yonatan, a raye ƙaunatattu ne da kuma bansha’awa, a mace kuma ba su rabu ba. Sun fi gaggafa sauri, sun fi zaki ƙarfi.
24 O daughters of Israel, weep for Saul, who clothed you in scarlet, with beautiful dresses, who put on ornaments of gold upon your apparel.
“Ya ku’yan matan Isra’ila, ku yi kuka saboda Shawulu, wanda ya suturta ku da jajjayen kayan ado, wanda ya yi wa rigunarku ado da zinariya.
25 How are the mighty fallen in the midst of the battle! O Jonathan, on thy high places slain.
“Jarumawa sun fāɗi a yaƙi! Ga Yonatan matacce a tuddanku.
26 I am distressed for thee, my brother Jonathan; very dear hast thou been unto me: wonderful was thy love for me, passing the love of women.
Na yi baƙin ciki saboda kai, Yonatan ɗan’uwana; ƙaunatacce kake a gare ni. Ƙaunarka a gare ni abar al’ajabi ce, abar al’ajabi fiye da ta mace.
27 How are the mighty fallen, and lost the instruments of war!
“Jarumawa sun fāɗi! Makaman yaƙi sun hallaka!”

< 2 Samuel 1 >