< 2 Samuel 4 >

1 And when Saul's son heard that Abner had died in Hebron, his hands became enfeebled, and all the Israelites were troubled.
Sa’ad da Ish-Boshet ya ji labari cewa Abner ya mutu a Hebron, sai ya karaya, sai dukan hankalin Isra’ila ya tashi.
2 And Saul's son had two men who were captains of bands; the name of the one was Ba'anah, and the name of the other Rechab, the sons of Rimmon the Beerothite, of the children of Benjamin: (for Beeroth also was reckoned to Benjamin:
To, ɗan Shawulu yana da’ya’ya maza biyu da suke shugabannin’yan hari. Ana kiran ɗaya Ba’ana, ɗayan kuma Rekab. Su’ya’yan Rimmon mutumin Benyamin ne daga Beyerot, an lissafta Beyerot a ɓangaren Benyamin,
3 And the Beerothites had fled to Gittayim, and remained sojourners there until this day.)
domin mutanen Beyerot sun gudu zuwa Gittayim inda suke zaman baƙunci har wa yau.
4 And Jonathan, Saul's son, had a son that was lame on both feet. He was five years old when the tidings came of Saul and Jonathan from Yizre'el, and his nurse took him up and fled: and it came to pass, in her haste to flee, that he fell, and was rendered lame. And his name was Mephibosheth.
(Yonatan ɗan Shawulu yana da ɗa mai suna Mefiboshet wanda yake gurgu a duka ƙafafu. Yana da shekara biyar ne sa’ad da labarin mutuwar Shawulu da Yonatan ya zo daga Yezireyel. Sai mai renonsa ta ɗauke shi ta gudu, amma yayinda take hanzari tă gudu, sai ya fāɗo, ya gurgunce.)
5 And the sons of Rimmon the Beerothite, Rechab and Ba'anah, went, and came at the heat of the day to the house of Ish-bosheth, who was just lying in bed as usual at noon.
To, Rekab da Ba’ana,’ya’yan Rimmon mutumin Beyerot, suka tafi gidan Ish-Boshet, suka isa can da tsakar rana yayinda yake hutun tsakar rana.
6 And they came thither into the interior of the house, as buyers of wheat; and they smote him under the fifth rib: and Rechab and Ba'anah his brother escaped.
Suka shiga sashe na cikin gida sai ka ce suna so su ɗibo alkama ne, suka soke shi a ciki. Sa’an nan Rekab da Ba’ana ɗan’uwansa suka zame suka ɓace.
7 Namely, they came into the house, while he was lying on his bed in his sleeping-chamber, and they smote him, and slew him, and cut off his head, and took his head, and went by the way of the plain all the night.
Sun shiga gidan yayinda yake kwance a gado a ɗakin barcinsa. Bayan sun soke shi sai suka kashe shi, suka kuma datse kansa. Suka ɗauke shi, suka yi tafiya dukan dare suka bi ta Araba.
8 And they brought the head of Ish-bosheth unto David to Hebron, and they said to the king, Behold, here is the head of Ish-bosheth the son of Saul thy enemy, who sought thy life: and the Lord hath granted to my lord the king vengeance this day on Saul, and on his seed.
Suka kawo kan Ish-Boshet wa Dawuda a Hebron, suka ce wa sarki, “Ga kan Ish-Boshet ɗan Shawulu, maƙiyinka, wanda ya nemi yă kashe ka. A yau Ubangiji ya rama wa ranka yă daɗe sarki, a kan Shawulu da zuriyarsa.”
9 But David answered Rechab and Ba'anah his brother, the sons of Rimmon the Beerothite, and said unto them, As the Lord liveth, who hath redeemed my soul out of all adversity,
Dawuda ya ce wa Rekab da ɗan’uwansa Ba’ana,’ya’yan Rimmon mutumin Beyerot, “Muddin Ubangiji yana a raye, wanda ya kuɓutar da ni daga wahala,
10 When one told me, saying, Behold, Saul is dead, and he was in his own eyes as though he brought good tidings, I took hold of him, and slew him in Ziklag, who [thought] that I should give him a reward for his tidings:
sa’ad da wani mutum ya ce mini, ‘Shawulu ya mutu,’ yana tsammani ya kawo labari mai daɗi ne, na kama shi na kashe a Ziklag. Ladar da na ba shi ke nan saboda labarinsa!
11 How much more, when wicked men have slain a righteous man in his own house upon his bed? and now, behold, I will require his blood of your hand, and I will remove you away from the earth.
Balle fa, sa’ad da mugayen mutane suka kashe marar laifi a gidansa, a bisa gadonsa, ashe, ba zan nemi jininsa daga hannunku in kawar da ku a duniya ba!”
12 And David gave the command to the young men, and they slew them, and cut off their hands and their feet, and hanged them up by the pool in Hebron. But the head of Ish-bosheth they took, and buried it in the sepulchre of Abner in Hebron.
Saboda haka Dawuda ya umarci mutanensa, suka kuwa kashe su. Suka yayyanka hannuwansu da ƙafafunsu, suka kuma rataye jikunansu kusa da tafki a Hebron. Amma suka ɗauki kan Ish-Boshet suka binne a kabarin Abner a Hebron.

< 2 Samuel 4 >