< 2 Samuel 22 >
1 And David spoke unto the Lord the words of this song, and on the day that the Lord had delivered him out of the hand of all his enemies, and out of the hand of Saul.
Dawuda ya rera wannan waƙa ga Ubangiji, sa’ad da Ubangiji ya cece shi daga hannun dukan abokan gābansa, da kuma daga hannun Shawulu.
2 And he said, Lord, my rock, my fortress, and my deliverer;
Ya ce, “Ubangiji shi ne dutsena, kagarata da kuma mai cetona;
3 God, my rock, in whom I trust; my shield, and the horn of my salvation, my high tower, and my refuge, my saviour! from violence dost thou save me!
Allahna shi ne dutsena. A gare shi nake samun kāriya shi ne garkuwata da kuma ƙahon cetona. Shi ne mafakata, maɓuyata, da mai cetona. Daga mutane masu fitina, ka cece ni.
4 Praised, I cried, be the Lord, and from my enemies was I saved.
“Na kira ga Ubangiji, wanda ya cancanci yabo, na kuwa tsira daga abokan gābana.
5 For the waves of death encompassed me, the floods of destruction made me afraid;
Raƙumar ruwan mutuwa sun kewaye ni; raƙumar ruwan hallaka suna cin ƙarfina.
6 The bonds of hell encircled me, the snares of death seized on me: (Sheol )
Igiyoyin mutuwa sun nannaɗe ni; tarkuna kuma suka auka mini. (Sheol )
7 [When] in my distress I called upon the Lord, and to my God I cried; and he heard from his temple my voice, and my complaint [entered] into his ears.
“A cikin wahalata na yi kira ga Ubangiji; na yi kira ga Allahna. Daga cikin haikalinsa ya saurare muryata; kukata ta zo kunnensa.
8 Then shook and trembled the earth; the foundations of the heavens were moved; and they shook, because he was wroth.
Ƙasa ta yi rawa ta kuma girgiza, harsashan sararin sama sun jijjigu; suka yi makyarkyata saboda yana fushi.
9 Smoke went up in his anger, and consuming fire out of his mouth, coals flamed forth from him.
Hayaƙi ya taso daga kafaffen hancinsa; harshen wuta mai cinyewa daga bakinsa, garwashi mai ƙuna daga bakinsa.
10 And he bent the heavens, and came down, and thick darkness was under his feet.
Ya buɗe sararin sama, ya sauko ƙasa, girgije mai duhu suna ƙarƙashin ƙafafunsa.
11 And he rode upon a cherub, and flew along, and he was seen upon the wings of the wind.
Ya hau kerubobi, ya tashi sama; ya yi firiya a fikafikan iska.
12 And he made darkness round about him into pavilions, heavy masses of waters, thick clouds of the skies.
Ya mai da duhu abin rufuwarsa gizagizai masu kauri cike da ruwa suka kewaye shi.
13 From the brightness before him flamed forth coals of fire.
Daga cikin hasken gabansa garwashi wuta mai ci ya yi walƙiya.
14 The Lord thundered from heaven, and the Most High uttered forth his voice.
Ubangiji ya yi tsawa daga sararin sama; aka ji muryar Mafi Ɗaukaka.
15 And he sent out arrows, and scattered them; lightning, and discomfited them.
Ya harbe kibiyoyi, ya wartsar da abokan gāba, da walƙiya kuma ya sa suka gudu.
16 And then were seen the channels of the sea, there were laid open the foundations of the world; at the rebuke of the Lord, through the blast of the breath of his nostrils.
Aka bayyana kwarin teku, tushen duniya suka tonu. A tsawatawar Ubangiji, da numfashinsa mai ƙarfi daga hancinsa.
17 He stretched out from above [his hand], he took me; he drew me out from the mighty waters.
“Daga sama ya miƙo hannu ya ɗauke ni, ya tsamo ni daga zurfafa ruwaye.
18 He delivered me from my enemy, the strong, from those that hated me, when they were too mighty for me.
Ya kuɓutar da ni daga hannun abokin gāba mai iko, daga maƙiyina da suka fi ƙarfina.
19 They overcame me on the day of my calamity; but the Lord became my stay;
Suka auka mini cikin ranar masifata, amma Ubangiji ya kiyaye ni.
20 And he brought me forth into a large space: he delivered me, because he had delight in me.
Ya fito da ni, ya kai ni wuri mafi fāɗi; ya kuɓutar da ni gama yana jin daɗina.
21 The Lord rewarded me according to my righteousness: according to the purity of my hands did he recompense me.
“Ubangiji ya sāka mini bisa ga adalcina; bisa ga tsabtar hannuwana ya sāka mini.
22 For I had kept the ways of the Lord, and had not wickedly departed from my God.
Gama na kiyaye hanyoyin Ubangiji; ban yi wani mugun abu da zai juyar da ni daga Allahna ba.
23 For all his ordinances were before me, and from none of his statutes did I depart.
Dukan dokokinsa suna a gabana; ban ƙi ko ɗaya daga umarnansa ba.
24 I was also upright toward him, and I guarded myself against my iniquity.
Ba ni da laifi a gabansa na kiyaye kaina daga yin zunubi.
25 Therefore did the Lord recompense me according to my righteousness, according to my purity before his eyes.
Ubangiji ya sāka mini bisa ga adalcina bisa ga tsarkina a gabansa.
26 With the kind thou wilt show thyself kind; with the upright mighty man thou wilt show thyself upright.
“Ga masu aminci, kakan nuna kanka mai aminci, ga marasa laifi, kakan nuna kanka marar laifi,
27 With the pure thou wilt show thyself pure; and with the perverse thou wilt wage a contest.
ga masu tsarki, kakan nuna musu tsarki. Amma ga masu karkataccen hali, kakan nuna kanka mai wayo.
28 And the afflicted people thou wilt save; but thy eyes are upon the haughty, [that] thou mayest bring [them] down.
Kakan ceci mai tawali’u, amma idanunka suna a kan masu girman kai don ka ƙasƙantar da su.
29 For thou art my lamp, O Lord! and the Lord will enlighten my darkness.
Ya Ubangiji kai ne fitilata; Ubangiji ya mai da duhuna haske.
30 For [aided] by thee I run through a troop: [helped] by my God I leap over a wall.
Da taimakonka zan iya auka wa rundunar sojoji; tare da Allahna zan iya hawan katanga.
31 As for God—his way is perfect; the word of the Lord is tried; he is a shield to all that trust in him.
“Ga Allah dai, hanyarsa cikakkiya ce; maganar Ubangiji babu kuskure. Shi garkuwa ce ga waɗanda suka nemi mafaka a gare shi.
32 For who is God, save the Lord? and who is a rock, save our God?
Gama wane ne Allah, in ba Ubangiji ba? Wane ne dutse kuma in ba Allahnmu ba?
33 God is my strength and power; and he rendereth free from obstruction my way.
Allah ne ya ba ni ƙarfi, ya kuma mai da hanyata cikakkiya.
34 He maketh my feet like those of the hinds, and upon my high places he causeth me to stand.
Ya sa ƙafafuna kamar ƙafafun barewa; ya sa na iya tsayawa a kan duwatsu.
35 He teaches my hands for the war, so that a brazen bow is bent by my arms.
Ya hori hannuwana don yaƙi, hannuwana za su iya tanƙware bakan tagulla.
36 And thou gavest me the shield of thy salvation; and thy assistance hath made me great.
Ka ba ni garkuwar nasararka; ka sauko don ka sa in sami girma.
37 Thou enlargest my steps under me, so that my joints do not slip.
Ka fadada hanya a ƙarƙashina domin kada idon ƙafana yă juya.
38 I pursue my enemies and destroy them; and I return not again until I have made an end of them.
“Na fafari abokan gābana, na murƙushe su; ban kuwa juya ba sai da na hallaka su.
39 And I make an end of them, and I crush them, that they cannot rise; and they fall under my feet.
Na hallaka su ƙaƙaf, ba kuwa za su ƙara tashi ba, sun fāɗi a ƙarƙashin sawuna.
40 For thou hast girded me with strength for the war; thou subduest my opponents under me.
Ka ba ni ƙarfi don yaƙi; ka sa maƙiyina suka rusuna a ƙafafuna.
41 And my enemies thou causest to turn their back to me; those that hate me, —that I may destroy them.
Ka sa abokan gābana suka juya a guje, na kuwa hallaka maƙiyina.
42 They look about, but there is none to help; unto the Lord—but he answereth them not.
Suka nemi taimako, amma babu wanda zai cece su, suka yi kira ga Ubangiji, amma ba a amsa musu ba.
43 And I beat them small as the dust of the earth; as the mire of the street, I stamp them, I tread them down.
Na murƙushe su, suka yi laushi kamar ƙura; na daka na kuma tattake su kamar caɓi a kan tituna.
44 Thou hast also delivered me from the contests of my people: thou preservest me to be the head of nations, a people which I know not shall serve me.
“Ka kuɓutar da ni daga harin mutanena; ka kiyaye ni kamar shugaban al’ummai. Mutanen da ban sansu ba za su kasance a ƙarƙashina,
45 The children of the stranger shall utter flattery unto me; as soon as their ear heareth they shall be obedient unto me.
baƙi kuma su na zuwa don su yi mini fadanci; da zarar sun ji ni, sukan yi mini biyayya.
46 The children of the stranger shall fade away, and come forth tottering out of their close places.
Zukatansu ta karaya; suka fito da rawan jiki daga kagararsu.
47 The Lord liveth, and blessed be my Rock; and exalted be the God, the Rock of my salvation;
“Ubangiji yana a raye! Yabo ta tabbata ga Dutsena! Ɗaukaka ga Allah, Dutse, Mai Cetona!
48 The God, that granteth me vengeance, and bringeth down nations under me;
Shi ne Allahn da yake rama mini, wanda ya sa al’ummai a ƙarƙashina,
49 And that bringeth me forth from my enemies: also above my opponents thou liftest me up, from the man of violence thou deliverest me.
wanda ya kuɓutar da ni daga maƙiyina. Ka ɗaukaka ni bisa maƙiyina; ka kiyaye ni daga hannun mugayen mutane.
50 Therefore will I give thanks unto thee, O Lord, among the nations, and unto thy name will I sing praises;
Saboda haka, zan yabe ka, ya Ubangiji cikin dukan al’ummai; Zan rera waƙoƙin yabo ga sunanka.
51 [To] the tower of salvation of his king, and who showeth kindness to his anointed, to David and to his seed forever.
“Ya ba wa sarkinsa kyakkyawan nasara; ya nuna madawwamiyar ƙauna ga shafaffensa, ga Dawuda da zuriyarsa har abada.”